Monday, December 15
Shadow
Da Duminsa: “Akwai yiyuwar Kwankwaso ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC”

Da Duminsa: “Akwai yiyuwar Kwankwaso ya zama sabon shugaban jam’iyyar APC”

Duk Labarai
Wani jigo a jam'iyyar APC da bai so a bayyana sunansa ba ya bayyana cewa, akwai alamu masu karfi dake nuna cewa, tsohon gwamnan jihar Kano, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso zai koma jam'iyyar. A hirarsa da jaridar Guardian ya bayyana cewa, bayan komawar Kwankwaso APC akwai kuma yiyuwar zai zama shugaban jam'iyyar. Hakan na zuwane kwana daya bayan da Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya sauka daga mukamin shugaban jam'iyyar APC. Dan APC din ya bayyana cewa, matsawa Ganduje akayi ya sauka daga kan kujerar tasa ba dan yana so ba. Da aka tambayeshi ko saukar Ganduje daga shugabancin jam'iyyar APC zai iya sa Tinubu ya rasa kuri'ar Kano, sai yace hakan ba lallai ya faru ba domin duk da sauke Ganduje daga mukaminsa har yanzu yanawa uwar jam'iyyar APC biyayya.
Ina da Burin samun kudin shiga Naira Biliyan 30 kullun>>Dangote

Ina da Burin samun kudin shiga Naira Biliyan 30 kullun>>Dangote

Duk Labarai
Shugaban kamfanin Dangote, Alhaji Aliko Dangote ya bayyana xewa kamfaninsa na yin takin zamani suna tsammanin zai rika samar da kudin shiga da suka kai dala Miliyan $20 kullun. Yace kuma suna tsammanin kamfanin zai samar da kudaden shigar da suka kai dala Biliyan $70. Ya bayyana hakane yayin ziyarar da shuwagabannin hukumar hadahadar kasuwancin hannun jari suka kai masa matatar man sa dake Legas. Sun bashi tabbacin taimakawa dan saka kamfanin nasa na yin takin zamani a kasuwar saye da sayarwar hannun jari.
An nada magajin Ganduje

An nada magajin Ganduje

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa an nada mataimakin shugaban APC na yankin Arewa, Ali Bukar Dalori dan ya maye gurbin Dr. Abdullahi Umar Ganduje a matsayin shugaban jam'iyyar na riko. Hakan na zuwane yayin da aka kira taron kwamitin gudanarwa na jam'iyyar da zai tattauna dan nemo mafita bayan Saukar Ganduje. Ganduje ya mika takardar barin aiki inda yace yayi hakan ne saboda ya samu damar kula da lafiyarsa.
Bidiyo: Ku kwantar da hankalinku Amare kuma zan muku wakar da zata share muku hawaye>>Ali Jita

Bidiyo: Ku kwantar da hankalinku Amare kuma zan muku wakar da zata share muku hawaye>>Ali Jita

Duk Labarai
Tauraron mawakin Hausa, Ali Jita ya bayyana cewa ya samu sakonni bayan fitar da wakarsa ta yabon Uwar gida. Saidai yace an nemi ya yiwa Amarya itama waka. Yace wakar dan nishadi ne yayi ta kuma yana neman a zauna lafiya a gidaje. https://www.tiktok.com/@realalijita/video/7520613137016540421?_t=ZM-8xZ66BriPJg&_r=1 Yace nan gaba kadan Amare su saurareshi zai musu wakarsu suma.
Bani da lafiya a taimaka a barni in je neman magani kasar waje>>Yahya Bello ya roki kotu a yayin da ake shari’a kan zargin satar Naira Biliyan 80.2 da ake masa

Bani da lafiya a taimaka a barni in je neman magani kasar waje>>Yahya Bello ya roki kotu a yayin da ake shari’a kan zargin satar Naira Biliyan 80.2 da ake masa

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan jihar Kogi, Yahya Bello ya roki babbar kotun dake da zama a Abuja data taimaka ta barshi ya je kasar waje neman magani. Yahya Bello ya roki kotun data bashi fasfonsa wanda a baya ya bayar dan cika sharadin bayar da belinsa. Bello ya mika wannan korafinne ta hannun lauyansa, Joseph Daudu (SAN), Ana shari'a ne kan zargin da akewa Tsohon gwamnan na satar Naira Biliyan 80.2 wanda hukumar EFCC ta shigar da kararsa.
Tinubu zai je ziyara yankin Karebiyan da taron BRICS a Brazil

Tinubu zai je ziyara yankin Karebiyan da taron BRICS a Brazil

Duk Labarai
Shugaba Bola Tinubu zai bar Abuja a gobe Asabar domin ziyarar ƙasashe biyu Saint Lucia da Brazil, kamar yadda wata sanarwa da kakakinsa, Bayo Onanuga ta bayyana. Sanarwar ta ce da farko shugaban zai yada zango a Saint Lucia a ziyarar da zai yi domin kyautata dangantaka tsakanin Najeriya da ƙasashen yankin Karebiya. Daga nan kuma shugaban zai tashi ya nufi Brazil domin halartar taron ƙoli na 17 na ƙungiyar ƙasashe masu haɓakar tattalin arziƙi ta BRICS a birnin Rio de Janeiro, daga ranar 6 – 7, ga watan Yuli mai kamawa, 2025. Zai halarci taron ne a matsayin Najeriya na abokiyar tafiyar ƙungiyar. Afirka ta Kudu da Masar da Habasha su ne ƙasashen Afirka da ke zaman mambobin ƙungiyar a Afirka.
Yanzu-Yanzu: Ganduje ya bayyana ainahin dalilin da yasa ya sauka daga shugaban APC

Yanzu-Yanzu: Ganduje ya bayyana ainahin dalilin da yasa ya sauka daga shugaban APC

Duk Labarai
Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya sauka daga shugabancin jam'iyyar APC a yau, Juma'a. Ya bayyana hakane a wata wasika da ya aikewa jam'iyyar. A cikin wasikar, Ganduje ya bayyana dalilin rashin lafiya a matsayin abinda yasa ya sauka daga mukamin nasa. Tsohon Gwamnan jihar Kanon ya sha suka daga mutanen yankin Arewa maso gabas saboda zargin rashin goyon bayan Kashim Shettima a matsayin abokin takarar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a zaben shekarar 2027 me zuwa. An bayyana cewa wani daga cikin mataimakan Gandujenne zai zama shugaban riko na jam'iyyar kamin babban zabenta a watan Disamba me zuwa.
Da Duminsa: Tinubu na son ya dauki Kwankwaso a matsayin mataimaki a 2027 shiyasa ya ya sauke Ganduje daga shugaban APC, ji bayani dalla-dalla

Da Duminsa: Tinubu na son ya dauki Kwankwaso a matsayin mataimaki a 2027 shiyasa ya ya sauke Ganduje daga shugaban APC, ji bayani dalla-dalla

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu na shiri daukar Dr. Rabiu Musa Kwankwa a matsayin mataimakinsa. rahoton yace shiyasa ma Shugaban ya matsayawa Ganduje ya sauka daga shugabancin jam'iyyar APC. A yaune dai aka samu rahotannin dake cewa, Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya sauka daga mukamin shugaban jam'iyyar APC bayan da fadar shugaban kasa ta nemi yayi hakan. Idan hakan ta tabbata, rade-radin da ake yadawa cewa shugaba Tinubu ba zai tafi da Kashim Shettima ba a zaben shekarar 2027 ta tabbata kenan.
Ji irin Wulakancin da Akawa Ganduje kamin ya sauka daga shugaban APC

Ji irin Wulakancin da Akawa Ganduje kamin ya sauka daga shugaban APC

Duk Labarai
Rahotanni sun tabbata cewa Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya sauka daga shugaban APC. Wasu bayanai sun ce kamin saukarsa Ganduje, an cire duk wasu kayan aikinsa daga ofishinsa dake hedikwatar jam'iyyar APC dake Abuja. Rahoton yace kuma daga fadar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu aka umarci Ganduje ya sauka daga mukamin nasa. Wane ne Abdullahi Ganduje? An haifi Abdullahi Umar a ƙauyen Ganduje da ke cikin ƙaramar hukumar Dawakin Tofa ta jihar Kano a 1949. Ya fara karatun Ƙur'ani da Islamiyya a ƙauyensu, inda ya samu ilimin addini. Ya shiga firamare ta Dawakin Tofa daga 1956 zuwa 1963. Ganduje ya fara makarantar sakandiren Birnin Kudu a 1964 inda ya kammala a 1968. Ya shiga makarantar horar da malamai da ke Kano tsakanin 1969 zuwa 1972. Tsohon gwamnan jihar Kanon ya samu d...