Saturday, December 13
Shadow
Sojoji Sun Kàshè Manyan masu ikirarin Jìhàdì A jihar Bòrnò

Sojoji Sun Kàshè Manyan masu ikirarin Jìhàdì A jihar Bòrnò

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} A ranar Litinin, 9 ga watan Yuni 2025, dakarun haɗin gwiwa na sojoji sun kai farmaki maɓoyar ƴan ta’adda na Boko Haram da ISWAP a Nzalgana da ke ƙaramar hukumar Gujba da kuma yankin Timbuktu Triangle. Sanarwar da rundunar ta fitar a shafinta na X ta ce an kashe ƴan ta’adda da dama ciki har da jagororinsu. Daga cikin waɗanda aka kashe akwai Ameer Malam Jidda, wani babban kwamanda da ke da tasiri a ƙauyukan Ngorgore da Malumti. Sojojin sun ƙara cewa sun kuma ƙwato makamai da was...
Ka shiga taitayinka, naga take-takenka baka a da’a>>Shugaba Tinubu ya gargadi Sanata Ali Ndume bayan da yace ‘yan Najeriya na cikin wahala

Ka shiga taitayinka, naga take-takenka baka a da’a>>Shugaba Tinubu ya gargadi Sanata Ali Ndume bayan da yace ‘yan Najeriya na cikin wahala

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Fadar shugaban kasar Najeriya ta gargadi Sanata Ali Ndume kan kalaman da yake yi wanda ta kira na rashin da'a ga shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. Fadar shugaban kasar tace akwai rashin da'a a cikin kalaman na sanata Ali Ndume. Sanarwar ta fito ne daga bakin me magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga inda yace maganar da Sanata Ndume yayi cewa akwai masu satar kudin talakawa da wadanda basu cancanta ba a cikin gwamnatin Tinubu bai kawo wata hujja akan ta ba. Yace Ndume n...
Duk da ni dan APC ne, bana goyon bayan Tinubu ya zarce a 2027 saboda ‘yan Najeriya na cikin wahala>>Inji Sanata Ali Ndume

Duk da ni dan APC ne, bana goyon bayan Tinubu ya zarce a 2027 saboda ‘yan Najeriya na cikin wahala>>Inji Sanata Ali Ndume

Duk Labarai
Sanata Ali Ndume wanda ya fito daga jihar Borno ya bayyana cewa baya cikin 'yan jam'iyyar APC da suke neman shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya zarce. Ya bayyana hakanne a hirar da aka yi dashi a gidan talabijin na Channels TV. Sanata Ali Ndume yace dalilinsa kuwa shine lamura sun kazance a kasarnan inda farashin kayan masarufi suka yi tashin gwauron zabo, ga matsalar tsaro kuma rayuwa ta wa talaka tsanani. Yace 'yan Najeriya basa hangen wani abin ci gaba a gwamnatin shugaban kasa Bola Tinubu. Yace kuma kada shugaba Tinubu ya rudu da maganar Gwamnonin APC da suka ce suna goyon bayansa, ya tuna cewa, Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan gwamnoni 22 suka goyi bayansa amma duk da haka ya fadi zabe.
Ba dan kin goyon bayan Atiku da muka yi ba da yanzu ya jefa kasar cikin wahala da rikici>>Inji Wike

Ba dan kin goyon bayan Atiku da muka yi ba da yanzu ya jefa kasar cikin wahala da rikici>>Inji Wike

Duk Labarai
Ministan babban Birnin tarayya, Abuja, Nyesom Wike ya bayyana cewa ba dan kin goyon bayan Atiku Abubakar da suka yi ba shi da gwamnoni da suka kira kansu da G5 ba da Tuni kasarnan na cikin rikici. Wike da sauran gwamnonin da suka hada dana Seyi Makinde na jihar Oyo da Samuel Ortom na jihar Benue, da Okezie Ikpeazu na jihar Abia da Ifeanyi Uguanyi na jihar Enugu ne suka hadewa Atiku kai. Sun ce ba zasu goyi bayan Atiku ba inda suka goyi bayan Tinubu wanda hakan na daga cikin dalilin da yasa Atiku Abubakar ya fadi zabe. Wike a wajan taron masu ruwa da tsaki na jam'iyyar PDP ya bayyana cewa, ba su yi nadamar abinda suka aikata ba. Yace duk da rikicin dake cikin PDP, jam'iyyar ba zata ruguje ba. Ya bayyana cewa a ko da yaushe bin dokar jam'iyya da na kundin tsarin mulkin Najeriy...
Da Duminsa: Bayan Buratai: ‘Yan Bìndìgà sun sake baiwa wani baban dan siyasa hari

Da Duminsa: Bayan Buratai: ‘Yan Bìndìgà sun sake baiwa wani baban dan siyasa hari

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Abia na cewa, 'yan Bindiga sun budewa motar kwamishinan gidaje na jihar, Mr. Chaka Chukwumerije wuta inda suka fasa gilasan motar. Lamarin ya farune da daren ranar Asabar akan titin Enugu-Umuahia dake jihar Imo. Rahotanni sun ce lamarin ya farune a yayin da dan siyasar ya baro mahaifarsa, Umunneochi yana kan hanyar zuwa Umuahia. Akwai mutane 3 da suka rakashi saidai babu wanda ya jikkata a harin amma motarsu ta lalace da harin harsashi. A jawabinsa bayan faruwar lamarin, Chukwumerije ya bayyana cewa, Allah ne ya tsaresu a harin daya faru inda yace lamarin ya matukar girgizashi.
Ji Dalilin da yasa shugaba ‘yan siyasa ke ta tururuwa zuwa gidan Tinubu dake Legas

Ji Dalilin da yasa shugaba ‘yan siyasa ke ta tururuwa zuwa gidan Tinubu dake Legas

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa gidan Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu dake Legas ya zama kamar wata makkar 'yan siyasa. Inda suke ta tururuwa dan zuwa ganinsa tun bayan da ya fara hutun Sallah a can. Tinubu ya je Legas ranar 27 ga watan Mayu inda ya halarci taron kungiyar ECOWAS sannan daga nan ya kaddamar da wasu ayyuka sannan ya fara hutun Sallah. Daga cikin manyan 'yan siyasar da suka kaiwa shugaba Tinubu ziyara akwai; Gwamnan jihar Filato, Caleb Muftwang. Fasto Tunde Bakare. Dakataccen gwamnan jihar Rivers, Simi Fubara. Gwamnan jihar Osun, Senator Ademola Adeleke. Sai kuma Ministan kasafin Kudi, Atiku Bagudu. masana dai sun ce ganin Tinubu a Legas yafi sauki fiye da ganinsa a Abuja, sannan da maganar zaben 2027 na daga cikin dalilan da 'yan siyasr ke ta tururuwa...
Najeriya tazo ta uku a jerin kasashe mafiya yawan masana’antu a Nahiyar Afrika

Najeriya tazo ta uku a jerin kasashe mafiya yawan masana’antu a Nahiyar Afrika

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa Najeriya ta zo ta 3 a jerin kasashe 10 mafiya yawan masana'antu a Nahiyar Afrika. Kafar The African Exponent ce ta wallafa wannan bayani. Kafar tace ta yi binciken nata ne aka shekaru 10 da suka gabata inda ta bayar da muhimmanci ga kasashen dake da masana'antu mafiya yawa dake samar da abubuwan amfani. Jadawalin kasashen sune kamar haka: South Africa; Egypt; Nigeria; Morocco; Kenya; Algeria; Ethiopia; Ghana; Tunisia; and Zambia.
Bayan Allah sai Tinubu a gurina, dan ko iyalina, da mahaifana basu kaimun Tinubu ba>>Inji Ministan Ayyuka, David Umahi

Bayan Allah sai Tinubu a gurina, dan ko iyalina, da mahaifana basu kaimun Tinubu ba>>Inji Ministan Ayyuka, David Umahi

Duk Labarai
Ministan Ayyuka, David Umahi ya bayyana cewa, bayan Allah sai Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a wajensa. Ya bayyana hakane a yayin ganawa da manema labarai a Abakaliki yayin da yake bayyana irin jinjina da amincin da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bashi. Yace yabon da shugabab kasa, Bola Ahmad Tinubu ya masa yafi mai a bashi Dala Tiriliyan daya. Yace kuma a kullun yana fada idan har ya dora iyalinsa ko danginsa a sama da Allah ko Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu to kada Allah ya biya masa bukatunsa.
Yawan ‘yan majalisar APC ya karu a majalisar tarayya bayan canja sheka da ‘yan PDP da Labour  party da NNPP suka yi ta yi

Yawan ‘yan majalisar APC ya karu a majalisar tarayya bayan canja sheka da ‘yan PDP da Labour party da NNPP suka yi ta yi

Duk Labarai
Yawan 'yan majalisar Jam'iyyar APC a majalisar tarayya ya karu bayan da 'yan jam'iyyar Hamayya suka rika canja sheka kamar farin dango. A yanzu yawan 'yan majalisar dattijai na jam'iyyar APC sun karu zuwa 68 a yayin da yawan 'yan majalisar wakilanta suka karu zuwa 207. Hakan na zuwane yayin da majalisar ta 10 ta cika shekaru 2 da kafuwa. Idan rahotannin dake cewa sanata Senator Neda Imasuen daga jihar Edo dan jam'iyyar Labour party zai canja sheka zuwa jam'iyyar APC suka tabbata, to yawan 'yan majalisar Dattijai na jam'iyyar zai karu zuwa 69 kenan. Hakanan yawan sanatocin APC din zasu karu idan Sanata Ahmed Wadada Aliyu daga jihar Nasarawa wanda ya bar jam'iyyar SDP ya koma jam'iyyar APC. Ana zargin jam'iyyar APC da kokarin mayar da Najeriya tsarin jam'iyya daya.