Saturday, December 13
Shadow
Sarki Sanusi ya umarci hakimai da su shigo cikin Kano domin hawan Babbar Sallah

Sarki Sanusi ya umarci hakimai da su shigo cikin Kano domin hawan Babbar Sallah

Duk Labarai
Sarki Sanusi ya umarci hakimai da su shigo cikin Kano domin hawan Babbar Sallah. Majalisar Masarautar Kano ta fitar da wata takarda mai dauke da umarni ga dukkan Hakimai da 'Yan Majalisa na masarautar da su hallara a Birnin Kano domin halartar bikin hawan Babbar Sallah da za a gudanar cikin makon gobe. A wata takardar sanarwa da Sakataren Majalisar Masarautar Kano, Alhaji Abba Yusuf Danmakwayon Kano ya rattabawa hannu, an bukaci Hakimai da sauran shugabannin gargajiya da su iso Kano tare da dawakan su da mahayan su a ranar Laraba, 8 ga Dhul Hijjah, 1446 Hijira, wanda ya yi daidai da 4 ga Yuni, 2025. Bayan haka, ana sa ran za su halarci Fadar Mai Martaba Sarkin Kano a ranar Alhamis, 9 ga Dhul Hijjah, wato 5 ga Yuni, 2025 da misalin karfe 11:00 na safe, domin karbar umarni da ba...
Sauyin yanayi da rashin bin ƙa’idar gini ne suka haddasa ambaliyar Mokwa – Gwamnatin Najeriya

Sauyin yanayi da rashin bin ƙa’idar gini ne suka haddasa ambaliyar Mokwa – Gwamnatin Najeriya

Duk Labarai
Gwamnatin Najeriya ta ce sauyin yanayi da rashin bin ƙa'idar gine-gine da rashin gyara magunan ruwa ne suka haddasa mummunar ambaliyar da ta auku a garin Mokwa na jihar Neja. Ministan albarkatun ruwa da tsaftar muhalli na ƙasar, Farfesa Joseph Utsev ne ya bayyana haka a Abuja babban birnin ƙasar, yayin da yake bayani kan ambaliyar da auka wa garin Mokwa na jihar Neja. Ministan ya ce ba ɓallewar madatwar ruwa ba ce ta haifar da ambaliyar, yana mai alaƙanta matsalar da ƙaruwar tasirin sauyin yanayi, da kuma ruwan sama da ya wuce kima. Ya ƙara da ce tawagar ƙwararru daga ma'aikatarsa da kuma sauran hukumomi na garin domin auna irin ɓarnar da lamarin ya haifar. Mista Utsev ya buƙaci gwamnatocin jihohi da masu ruwa da tsaki su riƙa la'akari da gargaɗin da hukumomi ke fitarwa tare da...
Ƴansandan sun hana hawan sallah a Kano

Ƴansandan sun hana hawan sallah a Kano

Duk Labarai
Rundunar ƴansandan jihar Kano tare da hadin gwiwar sauran hukumomin tsaro a jihar sun ɗauki matakin haramta bukukuwan hawan salla a Kano. Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ƴansandan jihar SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar ya ce hukumomin tsaron sun ɗauki matakin ne sakamakon dalilai na tsaro. Matakin na zuwa ne bayan da wata takarda da aka yi amanna daga fadar Sarki Muhammadu Sanusi II ta fito, ta yi kira da hakimai da su shiga birnin Kano domin gudanar da bukukuwan hawan Sallah. Ko a lokacin bukukuwan ƙaramar sallah ma hukumomin tsaron jihar sun haramta hawan sallah, saboda bayanan sirrin da suka ce sun samu na wasu ''ɓata-gari'' da ke son amfani da bukukuwan hawan sallar wajen tayar da zauen tsaye a jihar. ''Kan haka ne hukumomin tsaron suka sake ɗaukar matakan haramta...
Gwamna Abba Kabir Ya Bada Gudummuwar Naira Miliyan Biyar Ga Farfesan Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo Dake Sokoto Da Ake Nema Wa Taimako Rashin Lafiya

Gwamna Abba Kabir Ya Bada Gudummuwar Naira Miliyan Biyar Ga Farfesan Jami’ar Usmanu Ɗanfodiyo Dake Sokoto Da Ake Nema Wa Taimako Rashin Lafiya

Duk Labarai
Gwamna Abba Kabir Ya Bada Gudummuwar Naira Miliyan Biyar Ga Farfesan Jami'ar Usmanu Ɗanfodiyo Dake Sokoto Da Ake Nema Wa Taimako Rashin Lafiya Gwamnan Jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf Ya Baiwa Farfesa Abubakar Roko Na Jami'ar Usmanu Ɗanfodiyo Dake Sokoto Gudummuwar Naira Miliyan Biyar Dake Fama Da Jinya, Domin Zuwa Neman Lafiya A Kasashen Waje. Allah Ya Ba Shi Lafiya Ya Kuma Saka Wa Gwamna Abba Kabir Yusuf Da Alheri! Daga Jamilu Dabawa
Ya kamata Najeriya ta gina katanga a kan iyakokinta>>Inji Shugaban Sojojin Najeriya, Christopher Musa

Ya kamata Najeriya ta gina katanga a kan iyakokinta>>Inji Shugaban Sojojin Najeriya, Christopher Musa

Duk Labarai
Babban hafsan sojin Najeriya, Janar Christopher Musa ya nuna buƙatar gina katanga a ilahirin iyakokin ƙasar da maƙwaftanta domin kare kwararar masu ɗauke da makami zuwa cikinta. Yanzu haka dakarun sojin Najeriya na fafutikar ganin sun yaƙi matsalar tsaro da ke addabar ƙasar, musamman rikicin Boko Haram da ƙasar ta kwashe shekara 16 tana fama da shi a arewa maso gabas. Mayaƙan ƙungiyar - wadda ta samo asali daga kungiyar IS reshen yammacin Afirka - sun kashe jami'an tsaro da dubban fararen hula, yayin da rikicin ya tagayyara miliyoyi. Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ambato Janar Christopher Musa a wani taron tsaro da ke gudana a Abuja yau Talata a Abuja na cewa "kula da kan iyakoki abu ne mai muhimmanci," inda ya bayar da misali da iyakar ƙasar Pakistan mai katangar da ke ...
Da gangan wasu mugayen ‘yan Najeriya ke kara farashin kaya dan kawai su bata min suna>>Gwamnatin Tinubu

Da gangan wasu mugayen ‘yan Najeriya ke kara farashin kaya dan kawai su bata min suna>>Gwamnatin Tinubu

Duk Labarai
Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta bayyana cewa da gangan wasu 'yan Najeriyar ke karawa kayan da suke sayarwa farashi dan kawai su batawa gwamnatinsa suna. Hadimin shugaban kasar me bashi shawara akan tattalin arziki, Tope Fasua ne ya bayyana hakan. Yace banda alkaluma tattalin arziki, akwai sauran abubuwan da ke sanya farashin kayan masarufi su tashi a Najeriya, hadda muguntar wasu 'yan kasar. Ya bayyana hakane a shafinsa na Facebook yayin da yake martani ga wani rahoto dake cewa wani gidan mai yana biyan ma'aikatansa Naira Dubu 10.
Ba kamar yanda ake cewa mun Kàshè ‘yan sa kai da yawa ba a Zamfara, Guda biyu ne kawai suka mùtù bayan jirgin saman mu yayi kuskuren jefa musu Bàm da tunanin cewa ‘yan Bìndìgà ne>>Hukumar Sojojin Najeriya

Ba kamar yanda ake cewa mun Kàshè ‘yan sa kai da yawa ba a Zamfara, Guda biyu ne kawai suka mùtù bayan jirgin saman mu yayi kuskuren jefa musu Bàm da tunanin cewa ‘yan Bìndìgà ne>>Hukumar Sojojin Najeriya

Duk Labarai
Rundunar sojin sama ta Najeirya ta tabbatar da kai hare-hare ta sama a jihar Zamfara da ke arewacin ƙasar, tana mai cewa dakarun sa-kai biyu sun rasu yayin da take harar 'yanfashin daji. A jiya Litinin ne mazauna ƙaramar hukumar Maru suka shaida wa BBC Hausa cewa jirgin yaƙin sojin ya kashe 'yan sa-kai, yayin da ƙungiyar kare haƙƙi ta Amnesty International ta ce mayaƙa 20 aka kashe a lokacin da suke bin sawun 'yanbindigar da suka kai musu hari da sace wasu mutane. Kakakin rundunar Ehimen Ejodame ya ce hare-haren da suka kai bayan samun bayanan sirri sun yi sanadiyyar kashe 'yanbindigar 20. "A martanin da muka mayar cikin gaggawa ranar 31 ga watan Mayu, dakarunmu sun kashe sama da 'yanta'adda 20 tare da lalata babura fiye da 21," a cewarsa yayin wani taron manema labarai&...
Kalli Hotuna: An kàshè sojojin Isra’ila uku a Gàzà

Kalli Hotuna: An kàshè sojojin Isra’ila uku a Gàzà

Duk Labarai
Rundunar sojin Isra'ila ta fitar da sunayen dakarunta uku da ta ce an kashe a arewacin Zirin Gaza ranar Litinin. Mutanen uku da ke da shekaru 20 da ɗoriya sun fito daga bataliya ɗaya - an ce biyu daga ciki likitoci ne, na ukun kuma kwamanda, a cewar wata sanarwa da rundunar sojin ta IDF ta fitar. Jaridar Times of Israel ta bayar da rahoton cewa an kashe su ne sakamakon wani bam da ya tashi da su lokacin da suke tsaka da fafatawa da mayaƙan ƙungiyar Hamas a yankin Jabalia.
Sanata Kalu ya fasakwai inda ya Bayyana masu daukar nauyin Ayyukan tà’àddàncì a Najeriya

Sanata Kalu ya fasakwai inda ya Bayyana masu daukar nauyin Ayyukan tà’àddàncì a Najeriya

Duk Labarai
Sanata Orji Uzor Kalu dake wakiltar mazabar Abia North a majalisar Dattijai ya bayyana cewa wasu 'yan siyasa ne da manyan ma'aikatan Gwamnati da 'yan Kasuwa ke daukar nauyin ayyuka Kungiyar Bòkò Hàràm. Ya bayyana hakanne a hirar da aka yi dashi a gidan Talabijin na Channels TV. Yace kuma masu yin hakan suna yi ne dan kawai su hana shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu iya gudanar da Gwamnatinsa yanda ya kamata. Yace amma ba ta haka bane ake karbar mulki, yace yawanci suna yi ne dan su kwace mulki daga hannun Tinubu ba kudi bane a gabansu.