Sunday, December 21
Shadow
Kaf masu neman takarar shugabancin Najeriya babu Gwani wanda ya cancanta kamar ni>>Inji Peter Obi

Kaf masu neman takarar shugabancin Najeriya babu Gwani wanda ya cancanta kamar ni>>Inji Peter Obi

Duk Labarai
Dan takarar shugaban kasa a karkashin jam'iyyar Labour party a zaben shekarar 2027, Peter Obi ya bayyana cewa, babu Dimokradiyya a mulkin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. Ya bayyana cewa idan aka lura da abinda ya faru a jihar Rivers da zaben jihar Edo za'a iya gane cewa, babu Dimokradiyya a Najeriya. Peter Obi ya bayyana hakane a wata ganawa da aka yi dashi a Arise TV. Yace shiyasa yake ta neman ya zama shugaban kasa, saboda ya gyara wannan matsalar, yace a kaf cikin masu neman takarar shugaban kasar, babu gwani wanda ke da kwarewa kamarsa saboda yayi aiki da kamfanoni kuma ya zama gwamna.
Wata Sabuwa: Kakakin Jam’iyyar PDP ya koma jam’iyyar APC

Wata Sabuwa: Kakakin Jam’iyyar PDP ya koma jam’iyyar APC

Duk Labarai
Kakakin jam'iyyar PDP a jihar Legas, Hakeem Amode ya koma jam'iyyar APC. Ya bayyana hakane a wata ganawa da manema labarai tare da masoyansa a Ikeja ranar Litinin. Sun bayyana cewa, tsohon shugaban jam'iyyar PDP na jihar, Abdul-Azeez Adediran (Jandor), da ya koma APC ne ya dauki hankulansu suka koma jam'iyyar APC. A jawabinsa yace duka jam'iyyar PDP a jihar daga sama har kasa sun koma APC inda yace saboda jam'iyyar PDP ta tasa alkibla.
An kaddamar da shafin Yanar gizo na masoya Shugaba Tinubu, da ke da ra’ayin sake zabensa a 2027 duk wanda ke da ra’ayi yana iya zuwa yayi rijista

An kaddamar da shafin Yanar gizo na masoya Shugaba Tinubu, da ke da ra’ayin sake zabensa a 2027 duk wanda ke da ra’ayi yana iya zuwa yayi rijista

Duk Labarai
Kungiyar masoya shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu sun kaddamar da shafin yanar gizo na wadanda kw da ra'ayin sake zaben shugaban kasar a shekarar 2027. Kungiyar me suna the BAT Ideological Group ta bayyana cewa, ta yi hakanne dan hada bayanan masoya shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da wanda suke son sake zabensa. Kungiyar tace kuma hakan zai saukaka maganar ace sai mutum ya je Abuja dan za'a yi meeting ko dan zai yi rijista. Tace kuma hakan zai saukaka mata yada manufar shugaban kasar ga al'umma. Shugaban kungiyar, Bamidele Atoyebi ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.
An kama wannan mutumin ya saci kwalayen sigari guda 9 daga wani Super Market wanda darajarsu ta kai Naira Dubu 90

An kama wannan mutumin ya saci kwalayen sigari guda 9 daga wani Super Market wanda darajarsu ta kai Naira Dubu 90

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, jami'an tsaro a jihar Legas karkashin rundunar RRS dake Falomo a Ikoyi sun kama wani mutum da kwalayen sigari guda 9 da ya sata daga wani babban shagon da ake cewa, Super Market. An kiyas ta cewa darajar kwalayen sigarin da ya sata zasu kai Naira Dubu 90. Hukumar 'yansandan tace ta kama wanda ake zarginne da misalin karfe 5:30 pm na yammacin ranar Labadi. Hukumar 'yansandan tace kowane kwalin sigari ana sayar dashi akan Naira dubu 10 wanda jimulla kudin sigarin da ya sata Naira dubu 90 kenan. Sunce Tuni suka mikashi ga hukumar 'yansanda ta Falomo.
Karya Ake min, ni bance ‘yan Bìndìgà sun kaiwa Janar Buratai hari ba>>Inji Sanata Ali Ndume

Karya Ake min, ni bance ‘yan Bìndìgà sun kaiwa Janar Buratai hari ba>>Inji Sanata Ali Ndume

Duk Labarai
Sanata Ali Ndume daga jihar Borno ya bayyana cewa, karya ake masa shi baice an kaiwa tsohon shugaban sojojin Najeriya, Janar Tukur Yusuf Buratai hari ba. Rahotanni sun watsu cewa, Sanata Ali Ndume ya ce an kaiwa Buratai hari a ranar Juma'ar data gabata inda ya tsallake rijiya da baya. Saidai a bayanin Sanata Ali Ndume bayan da wancan labari ya watsu shine shi bai ce haka ba, cewa yayi an kaiwa garin Buratai hari ne ba tsohon shugaban sojojin ba. Mayakan kungiyar dake ikirarin Jìhàdì ta Bòkò Hàràm dai sun dawo gadan-gadan inda suke kaiwa jami'an tsaro hare-hare akai-akai inda wasu rahotannin ke cewa ma sun fi sojojin Najeriya makaman yaki.
Duk da karin kudin wutar Lantarki da kamfanonin wutar Najeriya suka yi, aun tafka Asara

Duk da karin kudin wutar Lantarki da kamfanonin wutar Najeriya suka yi, aun tafka Asara

Duk Labarai
Kamfanonin rarraba wutar Lantarki na Najeriya Discos sun bayyana cewa, sun tafka asarar Naira Biliyan N202bn a watanni 3 na farkon shekarar 2025. Hakan na zuwane duk da kara kudin wutar da kamfanonin Discos din suka yi. Rahoton yace an yi karin kudin wutar da kaso 106.68 cikin 100. Rahoton yace kamfanonin wutar Lantarkin da ake dasu guda 12 sun aikawa da mutane bill din wuta na Naira Biliyan N761.91bn a tsakanin watan Janairu zuwa Maris. Saidai naira Biliyan N559.3bn ce kwastomomin suka iya biya a matsayin kudin wutar. Hakan na nufin ba'a biya Naira Biliyan N202.61bn na kudin wutar. Idan aka kwatanta da shekarar 2024, inda kamfanonin wutar suka aikawa kwastomomin bill din Naira Biliyan N368.65bn amma suka karbi Naira Biliyan N291.62bn, basu karbi Naira Biliyan N77.03bn ba...
Hadimin Shugaba Tinubu, Aliyu Audu ya ajiye mukaminsa, shine na 3 da ya ajiye mukaminsa a mulkin Tinubu

Hadimin Shugaba Tinubu, Aliyu Audu ya ajiye mukaminsa, shine na 3 da ya ajiye mukaminsa a mulkin Tinubu

Duk Labarai
Hadimin shugaban kasa, me bashi shawara akan harkar jama'a, Aliyu Audu ya ajiye aikinsa na baiwa shugaban kasar ahawara. Ya bayyana hakane a sakon da ya aikawa shugaban kasar a cikin wasika ranar 8 ga watan Yuni inda yace yana godiya matuka da damar da shugaban kasar ya bashi na bautawa kasarsa. Ya yabawa tsohon hadimin shugaban kasar, Ajuri Ngilale wanda yace ta sanadiyyarsa ne ya samu wannan mukami. Shima dai Ajuri Ngilale ajiye mukaminsa yayi daga Gwamnatin Tinubu. Hakanan bayanshi, akwai Hakeem Baba Ahmad da shima ya ajiye mukamin nasa.
Kalli Hoton Sojan da me kwacen waya ya Kàshè a Kaduna

Kalli Hoton Sojan da me kwacen waya ya Kàshè a Kaduna

Duk Labarai
Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan da ya nemi ya miƙa masa wayar da ke hannunsa. Wata sanarwa da rundunar sojin Div 1 da ke Kaduna ta fitar ta ce Lt Commodre M Buba da ke kwas na shiga layin manyan sojoji ya samu fanco a tayar motarsa abin da ya tilasta masa tsayawa a daidai gadar sama ta Kawo da ke Kaduna, inda fitowarsa ke dawuya sai wani ya zo ya same shi ya nemi ya ba shi wayarsa. Sai sojan ya nemi sanin dalilin bayar da wayar abin da ya sa mutumin ya fitar da wuƙa ya caka masa a ƙirji. Wani ɗn sintiri ya yi ƙoƙarin ceton sojan amma shi ma mutum ya daɓa masa wuƙar a hannunsa. An kai Lt Commodore asibitin Manalal amma kuma rai ya yi halinsa. Sai dai kuma mutanen da ke kusa da wurin da abin ya faru sun yi wa makashin tara-tara inda suka hallaka shi shi ma....
Kungiyar Dattawan Arewa ta gargadi Shugaba Tinubu kan 2027

Kungiyar Dattawan Arewa ta gargadi Shugaba Tinubu kan 2027

Duk Labarai
Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya ta yi kira shugaba Tinubu da manyan muƙarraban gwamnatinsa da su mayar da hankali wajen ganin sun kyautata rayuwar ƴan Najeriya maimakon gangamin yaƙin neman a sake zaɓen Tinubu a 2027, inda a cewar ƙungiyar hakan ya yi wuri. A wata sanarwa da kakakin ƙungiyar na ƙasa, Farfesa Tukur Muhammad-Baba ta taya Musulmi murnanr Babbar Sallah, ƙungiyar ta bayyana rashin jin daɗinta dangane da taɓarɓarewar tsaro da tsadar rayuwa da rashin wutar lantarki da matsalolin lafiya, ilimi da karyewar darajar Naira da tashin farashin kayan abinci. Ƙungiyar ta kuma nuna takaicinta yadda duk da irin waɗannan ƙalubale amma jam'iyyar APC ta fi mayar da hankali kan gangamin yaƙin neman zaɓen Tinubun a 2027. Idan dai ba a manta ba a watan da ya gabata ne dukkani...
Bayani dalla-dalla game da mummunan hàdàrin motar da ya faru da Adam A. Zango da halin da yake ciki a yanzu

Bayani dalla-dalla game da mummunan hàdàrin motar da ya faru da Adam A. Zango da halin da yake ciki a yanzu

Duk Labarai
Jarumi Adam A. Zango Yayi Haɗarin Mota Akan Hanyar Kano Zuwa Kaduna. {"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Daga Abubakar Shehu Dokoki Fitaccen Jarumin Masana'antar shirya Fina-finai ta Kannywood Adam A. Zango, ya gamu da haɗarin mota akan hanyarsu daga Kaduna Zuwa Kano, wanda hakan ya tada hankalin dayawa daga cikin Masoyansa, dakuma mabiyan Jarumin. Bayyanar saƙon nuna godiya daga Adam A. Zango bisa addu'o'i da ake masa da kuma fatan alkairi, kamar yadda ya bayyana a shafinsa na Facebook, hakan ya sanyaya zuciyar...