Monday, December 15
Shadow
Kalli Bidiyon: Kungiyar ‘yan Kwallo na mata na Chelsea suma suna chashewa da wakar Shake Body ta Skales

Kalli Bidiyon: Kungiyar ‘yan Kwallo na mata na Chelsea suma suna chashewa da wakar Shake Body ta Skales

Duk Labarai
Bayan Lamine Yamal na Barcelona ya hau kan wakar Shake body ta mawakin Najeriya Skales, Wakar ta watsu sosai a Duniya. A bayabayannan, Kungiyar kwallon kafa ta mata ta Chelsea suma sun Chashe da wanann waka a dakin canja kaya. https://twitter.com/ChelseaFCW/status/1924415423425954121?t=fnfZmAw6UeSKouiHS0GXxA&s=19 Wakar dai ta samu an saurareta sau 324k a Spotify
Yanda Mutanen Karkara suka fi na Birni zuwa aikin Hajjijn bana ya kawo cece-kuce

Yanda Mutanen Karkara suka fi na Birni zuwa aikin Hajjijn bana ya kawo cece-kuce

Duk Labarai
Hajjin Bana ya zo da sabon salo a Najeriya inda mafi yawan wadanda ake gani na zuwa Mutanen karkara ne. Hakan ya dauki hankula musamman ganin yanda zuwan Hajjin banan yayi tsada inda mutanen Birni da yawa basa iya biya. Wasu dai na alakanta lamarin da cewa mutanen kauye akwai Noma da kiwo a yayin da wasu kuma ke zargin wasu na amfani da kudaden garkuwa da mutanene. A hajjin na bana dai an kama 'yan Bindiga da suke shirin zuwa aikin Hajji a Abuja da Sokoto wanda hakan ya saka shakku a zukatan mutane.
Wannan matashiyar me suna Zainab ta yi ridda ta koma Kirista a jihar Zamfara

Wannan matashiyar me suna Zainab ta yi ridda ta koma Kirista a jihar Zamfara

Duk Labarai
Wata matashiya me suna Miss Zainab Muhamadu a jihar Zamfara ta yi ridda ta koma Kirista inda Tuni aka kai ta Kotun shari'ar Musulunci a jihar. Zainab ta zama Kirista ne bayan da ta hadu da wani dan bautar kasa me suna Pastor Samuel da aka kai shi aiki jihar. Sun shaku sosai har daga karshe ya mayar da ita Kirista. Saidai Tuni an kamata inda a ranar juma'ar nan me zuwa za'a fara mata shari'a a kotun musulunci dake jihar Zamfara. Saidai tuni lauyoyi da kungiyoyin kare hakkin bil'adama sun taso inda suke cewa ba'a mata adalci ba, tana da 'yancin yin duk addinin da take so.
Ko da taimakonku ko babu zamu ci gaba da Yàkì sai mun ga bayan Kungiyar Hàmàs>>Netanyahu ya mayarwa da Amurka Martani kan kiran da ta mai ya daina Kàshè Falasdiynawa

Ko da taimakonku ko babu zamu ci gaba da Yàkì sai mun ga bayan Kungiyar Hàmàs>>Netanyahu ya mayarwa da Amurka Martani kan kiran da ta mai ya daina Kàshè Falasdiynawa

Duk Labarai
Firaiministan Israyla, Benjamin Netanyahu ya bayyanawa kasar Amurka cewa ko da ita ko ba taimakonta zai ci gaba da yaki a Gaza. Hakan na zuwane bayan da Dangantaka ke kara yin tsami tsakanin Amurka da Israyla. Rahotanni sun ce shugaban Amurka, Donald Trump na matsawa Benjamin Netanyahu akan ya dakatar da yakin amma sai ma kara kaimi yake. Hakanan shuwagabannin kasashen Turawa ma sun fara nuna rashin goyon bayansu ga yakin inda suka gargadi Netanyahu amma duk yayi kunnen uwar shegu.
Gwanin Ban Tausai: Ji Yanda ‘yan Achaba sukawa wani Bakanike kìsàn gilla a Sule ja saboda ya buge wani me Achaba dan Uwansu ya ji Rauni

Gwanin Ban Tausai: Ji Yanda ‘yan Achaba sukawa wani Bakanike kìsàn gilla a Sule ja saboda ya buge wani me Achaba dan Uwansu ya ji Rauni

Duk Labarai
Rahotanni daga Suleja Jihar Naija na cewa, Wani bakanike me suna Yusuf Isiaka ya gamu da fushin wasu 'yan Achaba bayan da ya buge wani daga cikinsu har ya ji rauni. Rahoton yace Yusuf yana gida sai me gidanshi ya kirashi ya bashi mota ya je ya gyara masa. Yana kan hanya ne sai ya buge wani dan Achaba wanda a cewar Rahoton dan Achabar ne ya fado masa, dan Achabar yaji rauni. Anan ne 'yan Achaba suka rufar masa da zagi da duka inda daga baya aka sasantasu, yace zai kai kara wajan 'yansanda. Ya hau mota ya ci gaba da tafiya kawai sai ya ji ana ihu Barawo, 'yan Achaba da yawa a bayansa, ganin yawansu yasa bai tsaya ba ya ci gaba da tuki inda su kuma suka ci gaba da binsa suna kara yawa sai da suka kai 50. A karshe sun cin masa suka fiddoshi daga mota suka dakeshi har ya mutu. ...
Gwamnatin Kasar Saudiyya Ta Kama Matar Rìkàķķen Ďàn Bìndiģa Ado Aliero Da Mahaifiyarsa A Yayin Da Suka Je Aikin Hajjì

Gwamnatin Kasar Saudiyya Ta Kama Matar Rìkàķķen Ďàn Bìndiģa Ado Aliero Da Mahaifiyarsa A Yayin Da Suka Je Aikin Hajjì

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Gwamnatin Kasar Saudiyya Ta Kama Matar Rìkàķķen Ďàn Bìndiģa Ado Aliero Da Mahaifiyarsa A Yayin Da Suka Je Aikin Hajjì
Shekara daya bayan da Gwamnatin Tinubu tace an gyarasu ‘Har yanzu matatun man fetur na Fatakwal da Wari basu fara fitar da man fetur ba’

Shekara daya bayan da Gwamnatin Tinubu tace an gyarasu ‘Har yanzu matatun man fetur na Fatakwal da Wari basu fara fitar da man fetur ba’

Duk Labarai
Masu hada-hadar man fetur a Najeriya na kokawa kan yadda suke samun matsala wajen samun fetur daga matatun gwamnati guda biyu da aka gyara kwanan nan—matatar Fatakwal da na Warri—shekara daya bayan da aka bayyana cewa sun fara aiki. Najeriya, wadda ta shafe shekaru tana fama da ƙarancin man fetur, ta kashe kimanin dala biliyan 2.4 tun daga shekara 2021 domin farfaɗo da waɗannan matatun da ke yankin Niger Delta, da nufin dakatar da dogaro da shigo da man fetur daga ƙasashen waje. Sai dai har yanzu, ba su fara fitar da man fetur ba. Kungiyar 'yan kasuwa masu gidajen mai ta Najeriya, PETROAN, ta bayyana wa kamfanin dillancin labaran Reuters cewa sama da mambobinta 6,700 har yanzu na dogaro da shigo da mai daga waje da kuma matatar Dangote. Bisa bayanan ƙungiyar, har zuwa watan Maris ...
Dokar tilastawa ‘yan Najeriya su rika yin zabe ba zata yi aiki ba>>Inji Femi Falana SAN

Dokar tilastawa ‘yan Najeriya su rika yin zabe ba zata yi aiki ba>>Inji Femi Falana SAN

Duk Labarai
Babban Lauyan Najeriya, Femi Falana, SAN ya bayyana cewa, dokar tilastawa 'yan Najeriya sai sun yi zabe ba zata yi aiki ba. Majalisar wakilai ta fara tattaunawa akan wani kudirin doka da kakakin majalisar, Tajuddeen Abbas ya gabatar da ya bukaci kowace dan Najeriya me hankali dole ya rika yin zabe. Dokar dai har ta tsallake karatu na 2. Saidai a nasa jawabin, Femi Falana yace wannan doka ba zata yi aiki ba. Yace dokar Najeriya ta tanadi a baiwa dan Najeriya damar ya yi tunani akan wanda zai zaba sannan doka ta bashi damar ya boye wanda ya kadawa kuri'ar. Yace dan haka wannan doka ba zata yi aiki ba duk da yasan cewa ana kokarin zartas da itane dan karfafawa mutane yin zabe.