Monday, December 15
Shadow
Bayanan Sirri da suka fito na karawa Dogarin shugaba Tinubu Mukami sun jawo cece-kuce sosai

Bayanan Sirri da suka fito na karawa Dogarin shugaba Tinubu Mukami sun jawo cece-kuce sosai

Duk Labarai
Bayanan sirri sun fito da suka bayyana cewa, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya amince a karawa dogarinsa mukami zuwa Brigadier General. Sannan kuma a barshi ya ci gaba da gadinsa, kamar yanda wata wasika da Nuhu Ribadu ya aikawa shugaban sojoji ta bayyana. An dai bayyana cewa, Wasikar ta sirri ce, saidai zuwa Yanzu Gwamnati bata ce uffan ba akanta. Rahotanni dai sun ce idan hakan ta tabbata to an saba doka domin za'awa dogarin na shugaba Tinubu karin mukami ne fiye da sauran abokan karatunsa.
Kalli Bidiyon: Duk me zargina akan wani abu ya tafi Kotu>>Inji Bello Matawalle

Kalli Bidiyon: Duk me zargina akan wani abu ya tafi Kotu>>Inji Bello Matawalle

Duk Labarai
Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle ya kalubalanci masu zarginsa da hannu akan matsalar tsaro da su tafi kotu. Ministan ya bayyana hakane a wata hira da DLC Hausa ta yi dashi inda yace zargin fatar baki idan ba kotu ce ta tabbatar dashi ba na banza ne. https://twitter.com/musa_kiliya/status/2000138006477390209?t=eIrjOzHaGqxsDCh9gUKqIg&s=19 Zarge-zarge dai sun yi yawa akan Ministan inda da yawa suke kiran da ya sauka daga mukamin nasa.
Allah kasa kada in kai matsayin da sai Annabi(Sallallahi Alaihi Wasallam) ya cece ni Ranar tashin Qiyama>>Inji Dr. Hussain Kano

Allah kasa kada in kai matsayin da sai Annabi(Sallallahi Alaihi Wasallam) ya cece ni Ranar tashin Qiyama>>Inji Dr. Hussain Kano

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama, Dr. Hussain Kano ya roki Allah cewa Allah sa kada ya kai matsayin da sai Annabi (Subhanallahi Alaihi Wasallam) ya ceceshi ranar Tashin Qiyama. Yayi inkari ga masu neman ceton Annabi a wajan Maulidi inda yace hakan shirka ce me iya kai mutum ga wuta wanda kuma Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ba za iya ceton me yin hakan ba. https://www.tiktok.com/@dr.hussainkano5/video/7583771231518772491?_t=ZS-92Dvt4alenA&_r=1
Naira milo 150 ko takalmi ba zata sai min ba>>Inji Primate Elijah Ayodele

Naira milo 150 ko takalmi ba zata sai min ba>>Inji Primate Elijah Ayodele

Duk Labarai
Malamin Kirista, Primate Elijah Ayodele ya bayyana cewa, Naira Miliyan 150 ko takalmi ba zata sai mai ba. Ya bayyana hakane a cocinsa sannan a matsayin martani ga Ministan wuta, Bayo Adelabu wanda ke son tsayawa takarar gwamnan jihar Oyo. Shi dai Ministan ya zargi malamin da cewa ya nemi ya bashi Naira Miliyan 150 ya masa Addu'ar neman nasara amma ya kiya shine ya koma yana bata masa suna. Saidai Faston yace kawai Bayo Adelabu yaga ba zai yi nasara bane a zaben me zuwa shine yake soki burutsu.
A tarihi wadanda basu da Addini ne masu bautar Gumaka ke binne gàwàrsù a cikin Akwatin gawa na Gwal, ban san inda Kiristoci suka samo hakan a addinin su ba>>Inji Malam Bashir Ahmad

A tarihi wadanda basu da Addini ne masu bautar Gumaka ke binne gàwàrsù a cikin Akwatin gawa na Gwal, ban san inda Kiristoci suka samo hakan a addinin su ba>>Inji Malam Bashir Ahmad

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Tsohon Hadimin Shugaban kasa, Malam Bashir Ahmad ya bayyana cewa a Tarihi, Wanda basu da addini masu bautar Gumaka ne ke binne gawarwakinsu a cikin akwatin gawa na Zinare. Yace a dokokin Addinin Kiristoci babu inda aka ce a binne gawa a cikin akwatin Zinare. Ya bayyana hakane a matsayin Martani ga wani fasto a jihar Bayelsa da ya binne Mahaifiyarsa a cikin akwatin gawa na Naira Miliyan 150 wanda aka ce da gwal aka yishi. https://twitter.com/BashirAhmaad/status/200018623266445...
Sarkin Wakar Daura ne aka baiwa Rarara ba Sarkin wakar kasar Hausa ba>>Inji Babban Yaron Naziru Sarkin Waka, Abba C Sale

Sarkin Wakar Daura ne aka baiwa Rarara ba Sarkin wakar kasar Hausa ba>>Inji Babban Yaron Naziru Sarkin Waka, Abba C Sale

Duk Labarai
Babban yaron Naziru Ahmad Sarkin Waka, Abba C Sale ya bayyana cewa, Sarautar Sarkin Wakar kasar Hausa da aka baiwa Rarara ba ta inganta ba. Yace sarkin Daura ne ya bayar da Sarautar dan haka a Kano su ba zasu kira Rarara da Sarkin Wakar Kasar Hausa ba. Yace Sarkij wakar Daura da Katsina ne Rarara. https://www.tiktok.com/@abbacsale2/video/7582265183674961172?_t=ZS-92DX9Q8IjC4&_r=1 Hakan na zuwane jim kadan bayan da Me Martaba sarkin Daura, Umar Farouk Umar ya nada Rarara a matsayin sarkin Wakar kasar Hausa.
Kalli Bidiyon Abin Mamaki, An zargi cewa an saka Fitilun bikin Kirsimeti a wani Masallaci dake kudancin Najeriya

Kalli Bidiyon Abin Mamaki, An zargi cewa an saka Fitilun bikin Kirsimeti a wani Masallaci dake kudancin Najeriya

Duk Labarai
Wani daga kudancin Najeriya yayi zargin cewa, an saka fitilun bikin Kirsimeti a masallaci. Yayi Bidiyon masallacin inda ya wallafa a shafinsa. Saidai da yawa sun ce basu yadda inda wasu ke cewa dama saidai a kudancin Najeriyar ne hakan zai iya faruwa. https://www.tiktok.com/@lucent0019/video/7583271209534622984?_t=ZS-92DVwAuKVrF&_r=1