Saturday, December 13
Shadow
Bayan da ya sha matsa a hannun DSS, Shugaban Kungiyar daliban Najeriya a karshe ya yadda ya karyata kansa kan zargin da yawa dan shugabab kasa, Seyi Tinubu cewa ya sa an masa dukan kawo wuka

Bayan da ya sha matsa a hannun DSS, Shugaban Kungiyar daliban Najeriya a karshe ya yadda ya karyata kansa kan zargin da yawa dan shugabab kasa, Seyi Tinubu cewa ya sa an masa dukan kawo wuka

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} A karshe dai, Shugaban Kungiyar daliban Najeriya, Atiku Abubakar Isah ya fito ya wanke dan shugaban kasa, Seyi Tinubu kan zarge-zargen da ya masa. A baya dai An ga Bidiyon Atiku yana cewa Seyi Tinubu ya masa tayin karbar Naira Miliyan 100 dan ya goyi bayan babansa, Bola Ahmad Tinubu. Yace amma yaki amincewa shine Seyi Tinubun ya dauki nauyin 'yan daba suka lakada masa duka. Saidai bayan wannan zarge-zargen ne hukumar 'yansandan farin kasa, DSS suka kama shugaban daliban, kam...
‘Yan Bìndìgà sun kàshè soja me mukamin Kyaftin da wani soja daya a Borno

‘Yan Bìndìgà sun kàshè soja me mukamin Kyaftin da wani soja daya a Borno

Duk Labarai
''Yan Bindiga da ake kyautata zaton mayakan Bòkò Hàràm ne sun kashe soja me mukamin Kyaftin a garin Izge na karamar hukumar Gwoza ta jihar. Lamarin ya farune da safiyar ranar Laraba da misalin karfe 1 na dare. Hakanan aun kuma kashe soja daya. Sarkin Gwoza, Alhaji Mohammed Shehu Timta ya tabbatar da faruwar lamarin. Saidai sojojin da 'yan Bijilante da mutanen Gari sun yiwa 'yan Bòkò Hàràm din Rubdugu inda suka kashe 3 daga ciki, sauran suka tsere suka bar makamansu da Mashina 10. Sojoji dai na bin sahun wanda suka tsere.
Gwamna Zulum ya hana sayar da giya a jihar Borno

Gwamna Zulum ya hana sayar da giya a jihar Borno

Duk Labarai
Gwamnan jihar Borno Babagana Zulum ya bayar da umarnin haramta sayar da barasa ko kuma giya a Maiduguri babban birnin jihar. Zulum ya ce an ɗauki matakin ne saboda yadda ake samun ƙaruwar rikici tsakanin masu adawa da juna a ƙungiyoyin asiri, da karuwanci, da ta'ammali da miyagun ƙwayoyi, da kuma ayyakan daba. "Na ji daɗi da na ga sojoji da ƴansanda da sauran ɓanagarorin tsaro na nan, saboda mafi yawan wadan nan abubuwa... wasu ne daga cikin sojojin da aka sallama daga aiki, da sauran jami'an tsaro da aka kora, da ma wasu daga cikin jami'an soji da ke aiki, da ma fararen hula," in ji Zulum. "Babu wani sabon abu a wannan doka, idan har muna son mu tsaftace birnin Maiduguri, to babu wanda za a bari."
Yan Nigeria kuji tsoron Allah ku daina Zargin Tinubu da cire Tallafin Man fetur, Saboda Bola Tinubu Ba shine ya cire Tallafin Man fetur Ba, Buharine>>inji Kawu Sumaila

Yan Nigeria kuji tsoron Allah ku daina Zargin Tinubu da cire Tallafin Man fetur, Saboda Bola Tinubu Ba shine ya cire Tallafin Man fetur Ba, Buharine>>inji Kawu Sumaila

Duk Labarai
Yan Nigeria kuji tsoron Allah ku daina Zargin Tinubu da cire Tallafin Man fetur, Saboda Bola Tinubu Ba shine ya cire Tallafin Man fetur Ba Yakamata yan Su Sannan Wannan, inji Kawu Sumaila Kada ku yanke Hukunci Naƙin ƙara Zaɓar Bola Tinubu Sabida cire Tallafin Man fetur Sam-Sam Tinubu Ba shine ya cire Tallafin Man fetur Ba Shi kawai Bayyanawa Yayi. Menene ra'ayinku?
Wata Sabuwa: An gano Makudan kudaden da shugaba Tinubu ya ware Kusa Tiriliyan 2 na gyaran Titunan Najeriya, Fiyade da rabin kudin Legas da kudancin Najeriya za’awa aiki dasu inda Arewa ta samu kaso kadan

Wata Sabuwa: An gano Makudan kudaden da shugaba Tinubu ya ware Kusa Tiriliyan 2 na gyaran Titunan Najeriya, Fiyade da rabin kudin Legas da kudancin Najeriya za’awa aiki dasu inda Arewa ta samu kaso kadan

Duk Labarai
A zaman majalisar Zartaswa na Ranar Litinin din data gabata, ta Amince da fitar da Naira Biliyan N787.14 da Dala Miliyan $651.7 dan yin gyaran Tutuna a fadin Najeriya. Saidai binciken tsanaki da Dan Gidan Tanko Yakasai yayi ya nuna cewa Gaba dayan Dala miliyan $651.7, kusan Naira Tiriliyan daya duk Legas za' kashewa. Hakanan daga cikin Naira Biliyan N787.14 ita kuma Naira Biliyan N420Billion sama da kaso 50 cikin 100 na kudin kenan, Kudancin Najeriya za'a kashewa. https://twitter.com/dawisu/status/1919652843373441175?t=Zz8CdbwI_NdBm7UFbZ2FUw&s=19 Hakan na nufin gaba daya baifi Naira Biliyan dari 3 bane za'a kashewa Arewa. Dama dai a baya An so canja fasalin rabin kudin Haraji dan baiwa jihar data fi kawo kudi rabo me tsoka.
Dalla-Dalla: Yaronnan dan shekaru 18 da ya dirkawa mata 10 ciki yayi bayanin dabarar da yakewa matan suna yadda dashi

Dalla-Dalla: Yaronnan dan shekaru 18 da ya dirkawa mata 10 ciki yayi bayanin dabarar da yakewa matan suna yadda dashi

Duk Labarai
Yaronnan dan jihar Anambra wanda aka ruwaito ya dirkawa mata 10 ciki a cikin watanni 5 yayi bayani dalla-dalla game da irin dabarar da yake amfani da ita wajan yaudarar matan suna yadda dashi. Yaron mai shekaru 18 an daukoshi daga kauyene aka kaishi wajan wani dan kasuwa dan ya koya masa kasuwanci. Saidai yaron ya dirkawa diyar me gidan ciki sannan ya dirkawa yarinyar shagon me gidan nasa ciki. Megidan ya koreshi inda ya mayar dashi kauye, saidai watanni biyu bayan mayar dashi kauyen, a camma ya dirkawa mata 8 ciki. Kwamishiniyar mata da walwala ta jihar Anambra, Ify Obinabo tace mahaifiyar yaron ce da kanta ta kaishi kara wajenta. Tace abin ya bata mamaki dan hakane ma ta kira yaron take tambayarsa shin wai yana da wani lakani ne ko Asiri da yake amfani dashi wajan yaudarar ma...
“Babu ƙanshin gaskiya a cewar da ake yi ƴan ta’adda na da makaman da su ka fi na jami’an tsaron Nijeriya” Inji Ministan Tsaron Nijeriya Muhammad Badaru Abubakar.

“Babu ƙanshin gaskiya a cewar da ake yi ƴan ta’adda na da makaman da su ka fi na jami’an tsaron Nijeriya” Inji Ministan Tsaron Nijeriya Muhammad Badaru Abubakar.

Duk Labarai
“ Babu ƙanshin gaskiya a cewar da ake yi ƴan ta'adda na da makaman da su ka fi na jami'an tsaron Nijeriya” Inji Ministan Tsaron Nijeriya Muhammad Badaru Abubakar. A Cikin Shekaru Biyu Na Gwamnatin Tinubu An Sami Cìkakken Tsaro Akan Hanyar Abuja Zuwa Kaduna, Wanda A Baya Ya Taɓa Kasancewa Tungar Masu Ģarkuwa Da Mutane, Inji Ministan Tsaro, Badaru "Daga watan Mayun 2023 zuwa yanzu mun yi nasarar murƙushe ƴan ta'adda har 13,000, kazalika an kawar da shugabannin Boko Haram sama da 300 "A Maiduguri, a baya da an ce Gambaru, Bama, ka san an ambaci hanya mai hatsarin gaske, amma a yanzu hakan ya zama tarihi, duk wannan ya faru ne a cikin shekaru 2 na wannan gwamnatin". Sojojin Nijeriya Sun Cancanci Lambar Yabo Fiye Da Wanda Ake Yi Musu A Yanzu, Duba Da Yadda Suke Yin Nasara Àka...