Monday, April 6
Shadow
An gano Majalisar tarayya ta cusa jimullar Naira Tiriliyan 10.96 a cikin kasafin kudin Najeriya cikin shekaru 4

An gano Majalisar tarayya ta cusa jimullar Naira Tiriliyan 10.96 a cikin kasafin kudin Najeriya cikin shekaru 4

Duk Labarai
Wasu kungiyoyin fafutuka sun yi Allah wadai da majalisar tarayya saboda cusa jimullar Naira Tiriliyan N10.96tn a cikin kasafin kudin Najeriya a tsakanin shekarun 2021 zuwa 2025. Kungiyoyin sun bayyana hakan da cewa bai dace ba inda suka nemi hukumomin yaki da rashawa da cin hanci na Najeriya dasu yi bincike kan wannan zargin. Kungiyoyin da suka yi wannan zargin sune the Socio-Economic Rights and Accountability Project, da kuma the Centre for Anti-Corruption and Open Leadership. Kungiyar BudgIT ce ta fara yin wannan bincike inda tace jimullar ayyukan da aka cusa a cikin kasafin kudin sun kai 30,632.
Duk wanda baya son Gwamnatin Tinubu na iya zuwa ya kàshè kanshi dama mun yi yawa a Najeriya>>Wike

Duk wanda baya son Gwamnatin Tinubu na iya zuwa ya kàshè kanshi dama mun yi yawa a Najeriya>>Wike

Duk Labarai
Ministan babban birnin tarayya, Abuja, Nyesom Wike ya bayyana cewa, duk wanda baya tare da Gwamnatin Tinubu na iya zuwa ya mutu dama mun yi yawa a Najeriya. Yace shi zai bayar da filima a binne duk me son mutuwa. Wike ya bayyana hakane inda yace ya gani a wani gidan talabijin ana sukar sakawa babban dakin taro na Abuja sunan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. Wike yace dalilin da suke bayarwa wai shine me yasa ba'a saka sunan wanda ya gina dakin taron ba. Wike yace wannan maganar banza ce. Yace akwai gurare da aka sakawa sunayen manyan mutane wadanda basu ne suka ginasu ba irin su FIlin Jirgin sama n Murtala dake Kano da

Da Duminsa: Ana sa Ran cikin darennan kasar Ìràn zata yi gwajin makamin Nòkìlìyà

Duk Labarai
Rahotanni daga kafafe da yawa sun ce ana tsammanin kasar Iran zata yi gwajin makamin Nokiliya a cikin darennan. Saidai Iran din bata bayyana hakan a hukumance ba. Idan Iran ta yi gwajin makamin Nokiliya din, to lallai ya tabbata ta mallakeshi kuma za'a kiyayeta. Watakila hakan ya kawo karshen yakin dan gudun kada ta jefawa kasar Israyla. Iran dai ta ki yadda Ayi sulhu dan ta daina shirin mallakar makamin kare dangi.

Labari Me Dadi: Makamin dake tare makamai da kakkabo jirage na kasar Iran ya dawo aiki bayan da Israyla ta musu kutse

Duk Labarai
Bayan da kasar Israyla tawa makaman tare hari da kakkabo jiragen sama na kasar Iran kutse, a yanzu ya dawo aiki tukuru. Harba ya harbo jirgin Israyla F-35 sannan sun kama mace matukiyar jirgin. https://twitter.com/Megatron_ron/status/1933634825602412759?s=19 Iran itace kasa ta Farko a Duniya data taba kakkabo wannan jirgin na Israyla. https://twitter.com/WarMonitors/status/1933630986220106229?t=pjwlPWagZztdqgdFe8h6qQ&s=19 Rahotanni sun ce makamin ya ci gaba da kakkabo jirage marasa matuka na kasar Israyla. https://twitter.com/Megatron_ron/status/1933637359435665787?s=19 Sannan 'yan kasar sun taru sai shewa suke.
Kasar Ìràn na mayar da martani me zafi

Kasar Ìràn na mayar da martani me zafi

Duk Labarai
Rahotanni daga kasar Israyla na cewa, kasar Iran ta cillawa Israylan manyan makamai sosai. Bidiyo ya nuna yanda makaman kasar Iran suka rika keta makaman tsaro na Israeyla suna mata barna. Rahotanni sun ce iran ta jefawa Israyla makamai akalla guda 800. Hare-hare Iran sun lalata gine-gine akalla 9, wasu 100 kuma an lalata su amma ba duka ba. https://twitter.com/I__military/status/1933619888314331601?t=fc-ipnlSknycH8rvKu_wow&s=19 https://twitter.com/I__military/status/1933609851818815936?t=YIOf8EzL4W-Qm3ec8PH-tg&s=19 Daga cikin gine-ginen da aka lalata hadda ginin ma'aikatar tsaro ta kasar Iran din. https://twitter.com/Megatron_ron/status/1933603426396483646?t=Wjkpy8u_t6d0-2I2i-PO1Q&s=19 Lamarin ya firgita mutanen kasar Israyla inda suka rik...
Israyla ta kaiwa tashar Nùkiliya din kasar Ìràn mafi tsaro hari

Israyla ta kaiwa tashar Nùkiliya din kasar Ìràn mafi tsaro hari

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Rahotanni daga kasar Iran na cewa, jiragen yakin kasar Israyla na ci gaba da ludugen wuta a kasar. Rahotanni sun ce yanzu haka jiragen sun yiwa tashar Nùkiliya mafi tsaro a kasar Iran me suna FORDO luguden bamabamai inda rahotanni suka ce an ji karar fashewar abubuwa har sau biyu. Ita dai wannan tashar Nokiliya a karkashin kasa take kuma an ginata ne da cewa bam din Buñkèr Bustèr ba zai iya lalata ba watau bam me tono kasa. Rahotanni sin ce taba wannan gurin zai iya harzuka ka...
Allah Sarki: ‘Yan Tàwàyèn Hòùthì daga kasar Yèmèn sun zama na farko a Duniya da suka goyi bayan Ìràn ba da baki ba, yanzu haka sun cillawa Israyla makami kuma Israylan ta kasa tareshi

Allah Sarki: ‘Yan Tàwàyèn Hòùthì daga kasar Yèmèn sun zama na farko a Duniya da suka goyi bayan Ìràn ba da baki ba, yanzu haka sun cillawa Israyla makami kuma Israylan ta kasa tareshi

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Rahotanni daga kasar Israyla na cewa, 'yan Tawanyen Houthì na kasar Yemen sun jefa mata makami me linzami. Duk da yake cewa, sojojin kasar, IDF sun ce zasu tare amma sun kasa tareshi, sai da ya sauka. Zuwa yanzu dai ba'a tabbatar da irin barnar da makamin yayi ba. Hoùthì dai na daga cikin masu goyon bayan kasar Ìran a ko da yaushe
Sai da na gayawa Shugaban Amurka cewa zamu kaiwa Ìràn hari kuma ya amince min>>Benjamin Netanyahu ya karyata kasar Amurka kan ikirarin cewa bata da hannu a kaiwa Ìràn hari

Sai da na gayawa Shugaban Amurka cewa zamu kaiwa Ìràn hari kuma ya amince min>>Benjamin Netanyahu ya karyata kasar Amurka kan ikirarin cewa bata da hannu a kaiwa Ìràn hari

Duk Labarai
Firaiministan Israyla, Benjamin Netanyahu ya bayyana cewa sai da ya sanar da shugaban kasar Amurka, Donald Trump kamin ya kaiwa Iran hari. Yace kuma Trump ya amince. Yace amma ba zai ari bakin Trump ya ci mai albasa ba, zai faa da bakinsa. A baya dai, Sakataren harkokin wajen Amurkar, Marco Rubio ya bayhana cewa, basu da hannu a kaiwa kasar Ìràn hari.
Kasar Ìran tace ta fice daga tattaunawar sulhun mallakar makamin kare dàngì

Kasar Ìran tace ta fice daga tattaunawar sulhun mallakar makamin kare dàngì

Duk Labarai
Kasar Iran ta sanar da ficewa daga tattaunawar sulhu kan mallakar makamin kare danginta. Kafafen yada labarai na kasar Iran din sun tabbatar da hakan inda hakan ke zuwa yayin da shugaban kasar Amurka, Donald Trump ke gargadin Iran din da ta yadda a ci gaba da tattaunawa ko hare-haren da za'a kai mata nan gaba yafi na yanzu muni. A ranar Lahadi me zuwane dai ake tsammanin cewa za'a ci gaba da tattaunawar Sulhun amma yanzu Iran tace ta fice daga tattaunawar. Hakan na iya kara kazanta fadan inda kasar Amurka na iya shigowa cikin fadan.
Tsohon Tsageran Naija Delta, Tampolo yawa shugaban kasa, Tinubu alkawarin kuri’u Miliyan 10 a zaben 2027

Tsohon Tsageran Naija Delta, Tampolo yawa shugaban kasa, Tinubu alkawarin kuri’u Miliyan 10 a zaben 2027

Duk Labarai
Wata kungiya karkashin tsohon tsageran Naija Delta, Tampolo ta yiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu alkawarin kuri'u dubu 10 a zaben 2027. Daya daga cikin shuwagabannin kungiyar me suna Comrade Sunday Adekanbi ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar a ranar 'yancin Najeriya a Abuja inda ya jawo hankalin 'yan Najeriya da su shiga kungiyar. Yace a shekaru 2 da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya yi yana Mulki, ya dora Najeriya a Turbar ci gaban tattalin arziki. Yace zasu yi aiki bisa jagorancin Tampolo dan tattaro kan 'yan Najeriya su goyi bayan gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a shekarar 2027.