Monday, December 15
Shadow
Sanata Natasha Akpoti taki mikewa tsaye kamar kowane sanata bayan da Sanata Godswill Akpabio ya shiga majalisar

Sanata Natasha Akpoti taki mikewa tsaye kamar kowane sanata bayan da Sanata Godswill Akpabio ya shiga majalisar

Duk Labarai
Sanata Natasha Akpoti ta ki mikewa tsaye kamar kowane 'yar majalisa bayan da kakakin majalisar, Sanata Godswill Akpabio da take zargin ya nemi yin lalata da ita ya shiga majalisar. A daidai wannan lokacin, bulaliyar majalisar, Sanata Mohammed Monguno ya gargadi sanata Natasha Akpoti da cewa dokar majalisar ce idan kakakin majalisar na shiga kowa sai ya mike. Ya jawo hankalinta da cewa ya kamata ta rika mutunta dokar majalisar ba tare da la'akari da wani abuba.
Najeriya ta ƙara yawan man da take haƙowa – Rahoto

Najeriya ta ƙara yawan man da take haƙowa – Rahoto

Duk Labarai
Najeriya ta ƙara yawan man fetur da take haƙowa zuwa ganga 70,000 a kowace rana fiye da adadin da ƙungiyar OPEC ta sanya mata, kamar yadda nazarin kamfanin dillancin labarai na Reuters ya nuna. A cewar nazarin, man da ƙasashe mambobin ƙungiyar OPEC - ta masu arzikin man fetur - su ka fitar a watan Fabrairu ya ƙaru, inda Iran ke kan gaba, duk da ƙoƙarin da Amurka ke yi na daƙile fitar da man. Najeriya ta ƙara adadin man da take fitarwa da ya zarce adadin da ƙungiyar ta ware mata. Ƙungiyar ta OPEC ta haƙo gangan miliyan 26 da 74,000 a kowace rana a watan da ya gabata, inda aka samu ƙarin ganga 170,000 a kullum idan aka kwantanta da watan Janairu, a cewar nazarin na Reuters. Ƙungiyar OPEC+ - wadda ta haɗa da ƙasashen OPEC da Rasha da sauran ƙawaye - na son rage yawan man da suke h...
Da Duminsa: An dakatar da sanata Natasha Akpoti daga ayyukan majalisa na tsawon watanni 6, an dakatar da Albashinta an kuma janye jami’an tsaron dake bata kariya saboda karya dokar majalisa

Da Duminsa: An dakatar da sanata Natasha Akpoti daga ayyukan majalisa na tsawon watanni 6, an dakatar da Albashinta an kuma janye jami’an tsaron dake bata kariya saboda karya dokar majalisa

Duk Labarai
A zaman majalisar tarayya na yau, Alhamis, majalisar ta dakatar da sanata Natasha Akpoti na tsawon watanni 6. Tun farko dai shugaban kwamitin ladaftarwa na majalisar, Sanata Neda Imasuen ne ya bayar da shawarar dakatar da sanata Natasha Akpoti na tsawon watanni 6 sannan a dakatar da albashinta da kuma janye jami'an tsaron dake bata kariya. Yace ya kamata a dauki wannan mataki ne saboda sanata Sanata Natasha Akpoti ta karya dokokin majalisar sannan an gayyaceta zuwa gaban kwamitin ladaftarwa saidai ta ki amsa gayyatar. A karshe dai majalisar ta amince da dakatar da sanata Sanata Natasha Akpoti na tsawon watanni 6 sannan kuma jami'an tsaro sun tasa keyarta zuwa waje. Saidai kamin ta fita tace wannan rashin adalcin ba zai dore ba. kalli Bidiyon anan
Har Majalisa Sanata Natasha Akpoti ta zo mana da Mijinta suka sumbaci juna, su rasa inda zasu je su yi hakan sai a gaban mu, Tana zargin Sanata Godswill Akpabio da nemanta ne kawai dan daukar hankalin mutane>>Inji Majalisar Dattijai

Har Majalisa Sanata Natasha Akpoti ta zo mana da Mijinta suka sumbaci juna, su rasa inda zasu je su yi hakan sai a gaban mu, Tana zargin Sanata Godswill Akpabio da nemanta ne kawai dan daukar hankalin mutane>>Inji Majalisar Dattijai

Duk Labarai
Majalisar dattijai ta bayyana cewa, Sanata Natasha Akpoti ta zargi kakakin majalisar da neman yin lalata da itane kawai dan ta dauki hankulan nmutane. Kakakin majalisar, Yemi Adaramodu ne ya bayyana haka a hirar da kafar ChannelsTV ta yi dashi. Yace har kofar majalisa Sanata Natasha Akpoti ta je ta yi kiss ita da mijinta. Yace ba yace hakan ya sabawa doka bane amma ai ana barin halas dan kunya dan kuwa hakan ya sabawa al'ada da dabi'ar mutanen kasarnan. _Yace Sanata Natasha Akpoti ta yi zargin Sanata Godswill Akpabio ya nemeta da lalata ne kawai dan ta dauki hankalin mutane.
Labari me Dadi: Za’a sake rage farashin man fetur

Labari me Dadi: Za’a sake rage farashin man fetur

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, akwai yiyuwar farashin man fetur zai sake sauka saboda farashin danyen man fetur din wanda daga cikinsa ake fitar da man fetur din yana ci gaba da sauka. Hakan zai kuma kara tabbata ne muddin aka ci gaba da samun karuwar karfin kudin Naira. Farashin danyen mai ya fadi ne saboda sanarwar da kungiyar OPEC ta fitar cewa zata kara yawan man fetur din da take hakowa
Najeriya ta zo ta shida a cikin kasashen da aka fi aikata ayyukan tà’àdàncì a Duniya na shekarar 2025

Najeriya ta zo ta shida a cikin kasashen da aka fi aikata ayyukan tà’àdàncì a Duniya na shekarar 2025

Duk Labarai
Najeriya ce ta zo matsayi na 6 a cikin kasashen da aka fi aikata ayyukan ta'addanci a Duniya a shekarar 2025. A shekarun 2023 da 2024 Najeriya tana matsayi na 8 ne. Kasar Burkina Faso ce ta zo a matsayi na farko sai kuma kasar Pakistan na biye mata baya inda kasar Syria ta zo ta 3. Mali ce ta 4 sai kasar Nijar ta 5 sai Najeriya ta zo ta 6. Hakanan rahoton yace an samu yawan mutanen da aka kashe ta sanadiyyar ta'addanci a Najeriya wanda yawansu ya kai mutane 565 jimulla.
An sako daliban jami’an da aka yi gàrkùwà dasu a Makurdi

An sako daliban jami’an da aka yi gàrkùwà dasu a Makurdi

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, daliban jami'ar University of Agriculture Makurdi ta jihar Benue da aka yi garkuwa dasu an sakosu. Garkuwa da daliban ya jefa makarantar cikin yanayin damuwa wanda sai da yasa aka kulle makarantar har na tsawon mako guda. https://www.youtube.com/watch?v=I2vvoBY9v7E?si=3IqJB8_RA4UOnFlq Sako daliban yasa an barke da murna a makarantar. kalli Bidiyon lamarin a nan
Gwamnatin Sokoto ta ƙaddamar da tallafin azumi ga masu buƙata ta musamman

Gwamnatin Sokoto ta ƙaddamar da tallafin azumi ga masu buƙata ta musamman

Duk Labarai
Gwamnatin jihar Sokoto da ke arewa maso yammacin Najeriya ta ƙaddamar ta tallafin azumi ga masu buƙata ta musamman a faɗin jihar. Cikin wata sanarwa da gwamnatin jihar ta ftitar, ta ce tallafin - wanda ya ƙunshi rabon kuɗi - zai shafi masu buƙata ta musamman duka ƙananan hukumomin jihar. Yayin da yake jawabi a wajen ƙaddamarwar gwamnan jihar, Ahmad Aliyu ya ce tallafin zai shafi cibiyoyi 27 na masu buƙata ta musamman a fadin jihar. Gwamnan kuma yi kira ga waɗanda za su amfana da tallafin su bayar da haɗin kai domin kauce wa turmutsitsi a wajen raba tallafin
Kwamitin Majalisar Dattawan Najeriya ya yi watsi da ƙorafin Natasha

Kwamitin Majalisar Dattawan Najeriya ya yi watsi da ƙorafin Natasha

Duk Labarai
Kwamitin ɗa'a da ladabtarwa da sauraron ƙorafin jama'a na majalisar dattawan Najeriya ya yi watsi da ƙorafin da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta shigar kan zargin shugaban majalisar, Godswill Akpabio da neman yin lalata da ita. Kwamitin ya bayyana ƙorafin da cewa ''ya zo gaban kwamitin a mace'', saboda rashin bin ƙa'ida wajen shigar da shi. A yayin zaman sauraron ƙorafin, shugaban kwamitin Sanata Neda Imasuen, ya karanto doka ta 40 cikin dokokin majalisar dattijai, inda ya bayyana cewa Sanata Natasha ta sanya hannu kan ƙorafin da kanta maimakon ta bai wa wani ya shigar da shi a madadinta, lamarin da ya lalace. Ya kuma ƙara da cewa batutuwan da ke cikin ƙorafin na gaban kotu a yanzu haka, wanda ya sa ba za a iya tattauna su ba kuma majalisar ba ta da hurumin sauraron su. Tuni d...
Mai Ɗaukar Hoton Da Ya Lashe Kambun Bajinta Na (Guinness World Record) Sa’idu Abdulrahman Ya Gana Da Captin Ahmed Musa

Mai Ɗaukar Hoton Da Ya Lashe Kambun Bajinta Na (Guinness World Record) Sa’idu Abdulrahman Ya Gana Da Captin Ahmed Musa

Duk Labarai
Matashin mai sana’ar ɗaukan hoto ɗan asalin Jihar Yobe, wanda ya samu nasarar lashe kambun bajinta na Duniya kan sana’arsa, (Guinness World Record In Photography), Sa’idu Abdulrahman, ya gana da fitaccen ɗan ƙwallon ƙafan Najeriya, Captin Ahmed Musa MON. Ganawar wadda ta gudana a jiya, matashin ya gabatar wa Captin ɗin kundin nasa na bajinta da ya samu bayan da ya yi nasarar ɗaukan hotuna 897 cikin mintuna 60. Sun tattauna muhimman batutuwa da suka shafi fasaha da ƙirƙire-ƙirƙire da rawar da za su taka wajen tallafa wa masu tasowa cikin ayyukan fasaha a Najeriya ta yadda su ma za su samu damar bayyanawa Duniya irin tasu ƙwarewar. Matashin ya yaba da yadda ya samu Ahmed Musa a matsayin mutum mai nasara a Duniyar ƙwallon ƙafa wanda kuma a kullum yake ƙoƙarin tallafawa masu tasowa da...