Tuesday, December 16
Shadow
Kalli Hotuna: Gagga-gaggan ƴan Bìndìgà 5 da rundunarsu a yankin Jibia sun tuba sun aje makami sun ayyana ba za su kara kai hari ba

Kalli Hotuna: Gagga-gaggan ƴan Bìndìgà 5 da rundunarsu a yankin Jibia sun tuba sun aje makami sun ayyana ba za su kara kai hari ba

Duk Labarai
Gagga-gaggan ƴan bindiga 5 da rundunarsu a yankin Jibia sun tuba sun aje makami sun ayyana ba za su kara kai hari ba Sun kuma mika bindigar AK49 har guda biyu don tabbatar da tubansu An kai ƙarshen zaman tattaunawa tareda da tubabbun yan dindiga a karamar hukumar Jibia ta jahar Katsina. A ranar Juma'a 28/2/2025, ne aka kai ƙarshen zaman tattaunawa da yan dindigar da suka shirya karɓar zaman lafiya a karamar hukumar Jibia a jihar Katsina. Anyi zaman a karkashin jagorancin Chairman na karamar hukumar Jibia da Jibiya Peoples Froum da (NCSOSACK) da rundunar sojin Nigeriya ta jihar Katsina, daga cikin tubabbun yan dindigar da a kayi zaman tattaunawar dasu akwai.1- Audu Lanƙai2- Kantoma3- Ori4- Tukur Dan Najeriya5- Bammi. A yayin zaman an tattauna batutuwa da da dama da kuma shimf...
Yan bìndigà sun sace dalibai 4 maza na Jami’ar FUDMA a jihar Katsina

Yan bìndigà sun sace dalibai 4 maza na Jami’ar FUDMA a jihar Katsina

Duk Labarai
Wasu 'yan bindi-gà masu garkuwa da mutane sun kutsa gidan ƙwanan daliban Jami'ar gwamnatin Tarayya ta FUDMA da ke garin Dutsin-ma, a jihar Katsina, inda suka yi awon gaba da dalibai 4 maza zuwa daji don neman fudin fansa. Lamarin ya faru a daren ranar Lahadi 2 ga watan March 2025 a rukunin gidajen dake unguwar bayan gidan Radio kusa da mazaunin jami'ar na wucin gadi. Ya zuwa yanzu dai ba a san inda aka nufa da daliban ba. Kalli bidiyon anan MUN DAUKO RUBUTUN DAGA SHAFIN KATSINA REPORTS
Ni zan kayar da Tinubu a zaben shekarar 2027>>Inji Sowore bayan da ya shiga aka yi gudun fanfalaki dashi

Ni zan kayar da Tinubu a zaben shekarar 2027>>Inji Sowore bayan da ya shiga aka yi gudun fanfalaki dashi

Duk Labarai
Dan takarar shugaban kasa na Jam'iyyar AAC a zaben shakerar 2019 da 2023, Omoyele Sowore kuma mawallafin jaridar Sahara Reporters ya shiga gudun yada kanin wani da aka yi a Abuja. Ya bayyana cewa shine zai kayar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da sauran 'yan takarar shugaban kasa a zaben 2027. Yace ya kamata Gwammati ta baiwa bangaren wasannin motsa jiki muhimmanci inda yace suma zasu iya kawo kudaden shiga kamar yanda fetur ke kawowa kasarnan.
Magidanci ya kkàshe Matarsa saboda rikicin abincin shan ruwa a jiya bayan an kai Azumin farko a jihar Bauchi

Magidanci ya kkàshe Matarsa saboda rikicin abincin shan ruwa a jiya bayan an kai Azumin farko a jihar Bauchi

Duk Labarai
DA DUMI-DUMI: Miji Ya Kashe Matarsa a Bauchi Saboda Abincin Buda Baki. Rundunar ‘Yan Sanda Ta Fara Bincike Kan Kisan Wasila Abdullahi Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi ta fara bincike kan wani mummunan lamari da ya faru a daren Asabar, 1 ga Maris, 2025, inda wani attajiri mai suna Alhaji Nuru Isah, mai shekaru 50, ya buge matarsa, Wasila Abdullahi, mai shekaru 24, har lahira. Bayanan da aka tattara sun nuna cewa rikici ya barke tsakanin ma’auratan ne a gidansu da ke kusa da makarantar GG Bauchi a unguwar Fadamam Mada, kan yadda za a raba kayan abinci da ‘ya’yan itatuwa don buda baki a watan Ramadan. Wani makwabci ya ce takaddamar ta rikide zuwa fada, inda Alhaji Nuru Isah ya dauki sanda ya bugi matarsa, wanda hakan ya sa ta fadi sumammiya. Bayan haka, an garzaya da ita asibitin...
Dalilin da yasa na koma Jam’iyyar APC>>Shehu Sani

Dalilin da yasa na koma Jam’iyyar APC>>Shehu Sani

Duk Labarai
Sanata Shehu Sani ya bayyana dalilin da yasa ya koma Jam'iyyar APC. Sanata Sani ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi a gidan talabijin na ChannelsTV. Yace Gwamnan jihar Kaduna, Malam Uba Sani ne ya jawoshi ya koma Jam'iyyar ta APC. Yace dama can yana daga cikin wadanda suka kafa jami'iyyar a Kaduna har aka ci zabe. Yace sun samu rashin jituwa da Gwamna El-Rufai ne a wancan lokacin shiyasa suka bar Jam'iyyar kuma yanzu Gwamna Uba sani ya dawo dasu.
Ashe ba yau aka fara ba: Yanda wata mata ta taba Fallawa Sanata Godswill Akpabio mari bisa zargin cewa ya bata makudan kudi dan ta amince yayi lalata da ita

Ashe ba yau aka fara ba: Yanda wata mata ta taba Fallawa Sanata Godswill Akpabio mari bisa zargin cewa ya bata makudan kudi dan ta amince yayi lalata da ita

Duk Labarai
A yayin da dambarwar sanata Natasha Akpoti da Godswill Akpabio ke ci gaba da bayyana inda take zarginsa da cewa ya nemi yin lalata da ita. An koma baya a tarihi a lokacin Sanata Godswill Akpabio yana ministan Ma'aikatar harkokin Niger Delta, Tsohuwar shugabar riko ta hukumar raya yankin Niger Delta watau NDDC, Joy Nunieh ta zargeshi da cewa ya nemi yin lalata da ita. A wancan lokacin har fallaasa mari ta yi inda tace dalili shine ya bata kudi wai ta yadda yayi lalata da ita. Matar dai itama ta bayyana wannan zargi ne a gidan talabijin na Arise TV inda tace yana tunanin zai iya canja mata tunani da kudi? Tace itace mace ta farko data taba falla masa mari amma yaki gayawa mutane kuma tana zarginsa da neman yin lalata da ita. Saidai a wancan lokacin Akpabio yace bata da lafiya ...
An kama Fasto da yin mu’ujizar karya inda yace ya mayar da wata mata me kudi amma sai bayan kwanaki aka ganta tana sayar da Lemun Kwalba

An kama Fasto da yin mu’ujizar karya inda yace ya mayar da wata mata me kudi amma sai bayan kwanaki aka ganta tana sayar da Lemun Kwalba

Duk Labarai
Wani fasto me suna Ebuka Obi ya shiga idon Duniya bayan da aka kamashi yana yiwa mabiyansa karya ta hanyar mu'ujizar karya. Faston dai ya kai wata mata cocinsa me suna Zion Prayer Movement Outreach inda ta yi ikirarin cewa da tana da 300,000 amma data hadu da faston kudinta sun yi albarka har ta sayi gidan Miliyan 500 a Lekki jihar Legas. Saidai kwanaki bayan yin wannan ikirari, An ga matar tana sayar da lemun Kwalba. Matar dai har wani gida ta je ta nuna wanda tace nata ne amma daga baya me gidan sai da ya kamata akan ikirarin da ta yi na gidansa. A baya dai, Faston ya taba yin ikirarin warkar da marigayi dan fim din Kudu, John Okafor wanda aka fi sani da Mr. Ibu daga cutar dake damunsa amma kuma sai gashi daga baya dan fim din ya mutu. Faston dai na ikirarin cewa shi annab...
Kalli Bidiyo: Bill din NEPA yana cikin bashi da ake bin mutum idan ya mutum>>Inji Dr. Bashir Aliyu Al-Furqan

Kalli Bidiyo: Bill din NEPA yana cikin bashi da ake bin mutum idan ya mutum>>Inji Dr. Bashir Aliyu Al-Furqan

Duk Labarai
Babban malamin Addinin Islama, Dr. Bashir Aliyu Al-Furqan ya bayyana cewa kudin wuta da ake bin mutum bashi yana cikin bashin da ake binsa wanda kuma ya kamata a biya masa. Malam ya bayyana hakane bayan da wasu suka aika masa Tambaya game da mahaifinsu da ya rasu inda suka ce ana binsa bashin kudin NEPA na Naira dubu dari 4. Malam yace tabbas ya kamata a biya dan kuwa wutar mutum saya yayi ba tasa bace ba dan haka ba da saidai ya sayi Diesel ko Fetur dan ganin haske. Malam yace ko da mutum yana tantamar kudin wutar da yake biya baya shan wutar, yace gara ya zamana kai ne kake bin bashi ba kaine ake bi ba. Kalli Bidiyon anan:
Kotu ta dakatar da JAMB hana dalibai masu shekaru kasa da 16 samun Admission a jami’o’i

Kotu ta dakatar da JAMB hana dalibai masu shekaru kasa da 16 samun Admission a jami’o’i

Duk Labarai
Babbar Kotun jihar Delta ta yi doka inda tace hana 'yan kasa da shekaru 16 samun gurbin karatu a jami'o'in Najeriya da hukumar JAMB ke yi ya sabawa kundin tsarin mulkin kasa. Karar wadda aka sakawa sunan John Aikpokpo-Martins v. Joint Admissions and Matriculation Board (JAMB) & four ohers ta kalubalanci JAMB kan hana 'yan kasa da shekaru 16 shiga jami'a. Mai shari'a, Hon. Justice Anthony O. Akpovi ya amince da bukatar masu kara inda yace hukumar JAMB ta sabawa ka'ida idan tace 'yan kasa da shekaru 16 ba zasu samu gurbin karatu a jami'o'in Najeriya ba. Da wannan hukunci, a yanzu kotun tace duka jami'o'i su rika daukar dalibai da suka cika sharudan dauka gurbin karatu ba tare da la'akari da shekarunsu ba. A ranar 16 October 2024 ne JAMB ta fito da sabuwar dokar hana 'yan kas...
An saci Naira Miliyan 329 daga bankunan Najeriya ta hanyar amfani da BVN na Jabu

An saci Naira Miliyan 329 daga bankunan Najeriya ta hanyar amfani da BVN na Jabu

Duk Labarai
Hukumar dake kula da warware sarkakiyar kasuwanci tsakanin bankunan Najeriya NIBSS ta bayyana cewa an yi amfani da BVN na karya aka sace Naira Miliyan 329 daga bankunan Najeriya. Hukumar tace wasu gungun 'yan Damfara ne suka rika amfani da hotunan mutane hadda 'yan kasashen waje suna basu sunayen 'yan Najeriya suka bude BVN. Rahotan yace bayan an bude BVN din an yi amfani dashi aka bide accounts a bankuna daban-daban na kasarnan wanda dasu ne aka yi amfani aka yi damfarar. An dai kulle wasu daga cikin account din da aka yi amfani dasu wajan yin wannan damfarar sannan an kai rahoton wasu masu POS da aka yi amfani dasu wajan damfarar gurin jami'an tsaro.