Thursday, December 18
Shadow
El-Rufai ne ya sani, Inji tsohon Kwamishina a Gwamnatin Jihr Kaduna Bashir Sa’idu da aka kama sa satar kudi

El-Rufai ne ya sani, Inji tsohon Kwamishina a Gwamnatin Jihr Kaduna Bashir Sa’idu da aka kama sa satar kudi

Duk Labarai
Tsohon Kwamishina a jihar Kaduna lokacin mulkin tsohon Gwamnan jihar, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai, watau Alhaji Muhammad Bashir Sa’idu da yanzu haka yake tsare bisa zargin satar kudaden gwamnati, yace Gwamna El-Rufai ne ya sashi duk abinda yayi. Ya bayyana hakane a cikin jawabin da ya baiwa 'yansanda bayan kamashi, kamar yanda wani dansanda da baiso a bayyana sunansa ya gayawa manema labarai kamar yanda jaridar TheNation ta ruwaito. Ana zargin Alhaji Muhammad Bashir Sa’idu da sayar da daloli mallakin jihar ta Kaduna akan farashin da bai kamata ba. Kotu tace ya aikata laifinne a shekarar 2022.
Kuma Dai: Kwanaki kadan bayan da EFCC ta kori jami’anta daga aiki saboda cin hanci da rashawa, Dala $400,000 da Gwalagwalai na miliyoyin Naira sun bace a ofishin EFCC din

Kuma Dai: Kwanaki kadan bayan da EFCC ta kori jami’anta daga aiki saboda cin hanci da rashawa, Dala $400,000 da Gwalagwalai na miliyoyin Naira sun bace a ofishin EFCC din

Duk Labarai
Rahotanni daga ofishin hukumar yaki da rashawa da cin hanci, EFCC sun bayyana cewa an nemi tsabar kudi har dala $350,000 zuwa dala $400,000 ba'a gani ba. Hakanan akwai wasu gwalagwalai na miliyoyin Naira da suma auka bace tare da kudin. Lamarin ya farune a ofishin hukumar dake jihar Legas, kamar yanda kafar PRNigeria ta ruwaito. Hakan na zuwane kwanaki kadan bayan da EFCC ta kori ma'aikata 27 saboda samunsu da rashawa da cin hanci da zamba cikin aminci. Wannan lamari yasa 'yan Najeriya na diga ayar tambaya akan hukumar ta EFCC da aka sani da yaki da rashawa da cin hanci amma da alamu me dokar bacci na neman bugewa da yin gyangyadi. Majiyar tamu tace ta yi kokarin jin ta bakin kakakin EFCC kan wannan sabon lamari amma abu ya faskara.
‘Yan Najeriya sun bayyana cewa man fetur din matatar man Dangote na dadewa kamin ya kare

‘Yan Najeriya sun bayyana cewa man fetur din matatar man Dangote na dadewa kamin ya kare

Duk Labarai
'Yan Najeriya da yawa ne suka bayyana jin dadinsu da amfani da man fetur din matatar man fetur ta Dangote. Da yawa da jaridar Punchng ta yi hira dasu sun ce sun ji dadin amfani da man fetur din na matatar man fetur ta Dangote saboda yana dadewa bai kone ba a mota idan aka kwatantashi da wanda suke amfani dashi a baya. Matatar man fetur ta Dangote ta bayyana cewa, ta yi hadaka da gidajen sayar da man fetur na MRS dan ta rika sayarwa 'yan Najeriya man fetur din da Rahusa. Wasu daga cikin wadanda aka yi hira dasu sun ce gwamnati ta yaudaresu kan matatar man fetur din Dangote inda suka ce man da ake shigowa dashi bashi da inganci.
Kotu ta bayar da belin Mahadi Shehu kan Milyan uku

Kotu ta bayar da belin Mahadi Shehu kan Milyan uku

Duk Labarai
Wata babbar kotun jihar Kaduna ta bayar da belin mai fafutuka Mahdi Shehu kan kudi Naira miliyan uku da kuma mutane biyu da za su tsaya masa a kan wannan kudi. Kotun ta ce wadanda za su tsaya wa dole ne su zama sanannun malamai a Nageriya. Sannan ta kwace fasfonsa kuma tace dolene sai ya rika zuwa wajan jami'an tsaro duk wata ana ganinsa, kuma duk idan ya zama dole sai yayi tafiya, ya sanar da kotun. Kotun tace ta amince ta bayar da belinsa ne saboda a yanzu ba'a tabbatar da laifin daya aikata ba.
Babu lungu da sakon da ba’a shaida salon Mulkina ba a Najeriya>>Shugaba Tinubu

Babu lungu da sakon da ba’a shaida salon Mulkina ba a Najeriya>>Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, babu lungu da sako na kasarnan da ba'a shaida salon mulkinsa ba a Najeriya. Shugaban ya bayyana hakane ta bakin me bashi shawara akan harkar sadarwa, Daniel Bwala a yayin da ake hira dashi a gidan talabijin na TVC. Bwala yace shugaba Tinubu a yayin da yazo kan mulki akwai jihohi kusan 19 dake fama da matsalar karancin kudi wanda cire tallafin man fetur da Tinubu yayi gwamnati ta samu karin kudin shiga sosai yasa jihohin suka farfado daga hanyar talaucewa da suka kama. Bwala ya kara da cewa, an samu ci gaba sosai kuma kowane lungu da sako na kasarnan sun shaida hakan. Yayi kira ga gwamnonin dasu tabbatar da sun bayar da ci gaban da ake bukata a jihohinsu.
Khalifa Aminu, fasihin yaron nan dan jihar Kano mai ƙere-ƙere, ya ƙirƙiri wata sabuwar na’ura mai nuna yanayin jini da jikin ɗan adam

Khalifa Aminu, fasihin yaron nan dan jihar Kano mai ƙere-ƙere, ya ƙirƙiri wata sabuwar na’ura mai nuna yanayin jini da jikin ɗan adam

Duk Labarai
. Ga bayanin na'urar nan da ya wallafa a shafin sa na Facebook. " Wannan shine sabon 'project' dina mai ban mamaki da ban al ajabi wato 'Scan blood & temperature device'. "Wato na'urar mai gano bugun jini da yanayin jiki. Wannan na'urar za ta iya temaka wa mutane da dama wajan kare lafiyar jikinsu. "Ita dai wannan na'urar ana saka ta a hannu ne. Bayan ka saka ta a hannu to duk inda ka shiga idan zafi yai yawa a wajen ko sanyi ko yanayin iskar da ka ke shaƙa to za tayi scaning din jikin ka ta ga yanayin 'temperature' din da jikin ka ya ke bukata idan wannan yanayin iskar ko zafi ko sanyi su kai yawa nan take za ta sanar da kai kabar wajen idan ba haka ba zaka iya cutuwa. "Sannan za ka iya scan din jinin jikin ka don ka ga lafiyar ka kalau ko ba ka da lafiya. " Wann...
An gano ƙanƙara mai shekara fiye da miliyan ɗaya a duniya

An gano ƙanƙara mai shekara fiye da miliyan ɗaya a duniya

Duk Labarai
Masana kimiyya a nahiyar Turai sun gano ƙanƙarar da watakila ake ganin ita ce mafi daɗewa a duniya a yankin Antarctica. Tawagar masu binciken ta haƙo silindar ƙanƙarar mai tsawon kusan kilomita uku wanda ke ɗauke da tsohon kumfa da kuma ɓurɓushi da aka daina ganin irinsa tun fiye da shekara miliyan guda. Masanan na fatan cewa yin nazarin tarihin yanayin zafi da matakan iskar gas zai taimaka musu wajen hasashen sauyin yanayi a nan gaba. Tuni dai masu binciken suka yayyanka ginshiƙin ƙanƙarar zuwa sassa masu tsayin mita ɗaiɗai domin faɗaɗa bincike a cibiyoyin bincike a faɗin nahiyar Turai.
Tinubu ya yi alhinin sojojin Najeriya da suka mùtù a harin Damboa

Tinubu ya yi alhinin sojojin Najeriya da suka mùtù a harin Damboa

Duk Labarai
Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya yi alhinin rasuwar dakarun ƙasar, da aka kashe a harin da mayaƙan Boko Haram ta kai wani sansanin soji da ke ƙauyen Sabon Gida, cikin ƙaramar hukumar Damboa a jihar Borno. Cikin wata sanarwa da fadar gwamnatin ƙasar ta fitar, ta ce Tinubu ya jajanta wa rundunar sojin ƙasar sakamakon mutuwar dakarunta shida a harin. Haka kuma shugaban ƙasar, ya buƙaci a gudanar da cikakken bincike domin gano abin da ya haddasa harin, domin ɗaukar matakan hana faruwar makamancinsa a nan gaba''. A ranar Asabar ne mayaƙan ISWAP suka ƙaddamar da hari da asuba kan sansanin sojin inda suka yi arangama da sojoji, lamarin da ya yi sanadiyyar mutuwar sojojin ƙasar shida da mayaƙa fiye da 30. Shugaba Tinubu ya kuma yaba wa sojojin ƙasar bisa jajirewar da suka yi, har ta k...