Monday, April 6
Shadow
Kamata yayi ka yi hakuri ka barwa dan kudu ya tsaya takara a 2027>>Wasu ‘yan PDP daga kudu suka gayawa Atiku

Kamata yayi ka yi hakuri ka barwa dan kudu ya tsaya takara a 2027>>Wasu ‘yan PDP daga kudu suka gayawa Atiku

Duk Labarai
Atiku Abubakar 2011 President campaign Photo by www.mortenfauerby.dk ©mortenfauerby 2010 - all rights reserved Wasu 'yan PDP daga Kudancin Najeriya sun baiwa Atiku Abubakar bakin cewa ya hakura da maganar tsayawa takara a shekarar 2027 ya barwa dan kudu. Sun ce ba ma Atiku kadai ba, duk wani dan Arewa kamata yayi ace ya hakura da tsayawa takara a barwa dan kudu ya tsaya takarar shugaban kasa a shekarar 2027. Kungiyar tace dama can Atiku ne ya fara jawowa jam'iyyar PDP koma baya a shekarar 2014 inda ya jagoranci gwamnoni 5 suka fice daga jam'iyyar suka koma APC suka juyawa Goodluck Jonathan baya. Shugaban kungiyar, Dennis Shima ne ya fadi haka inda yace ya kamata a bar dan kudu ya kammala shekara 8 kamar yanda Buhari yayi
Gwamnatin Jihar Akwa-Ibom ta tilastawa ma’aikatan Lafiya shiga jarjejeniya da rantsuwa cewa idan ta dauki nauyinsu suka yi karatu ba zasu tsere zuwa kasashen waje ba

Gwamnatin Jihar Akwa-Ibom ta tilastawa ma’aikatan Lafiya shiga jarjejeniya da rantsuwa cewa idan ta dauki nauyinsu suka yi karatu ba zasu tsere zuwa kasashen waje ba

Duk Labarai
Gwamnatin jihar Akwa-Ibom ta bukaci ma'aikatan lafiya a jihar da su sha rantsuwa cewa ba zasu tsere ba idan ta dauki nauyinsu suka je suka yi karatu. Shugaban ma'aikatan jihar, Elder Effiong Essien ne ya bayyana hakan inda yace zasu dauki ma'aikatan lafiya 600. Yace wannan bukata dolece saboda a tabbatar da cewa ma'aikatan lafiyar sun gudanar da aiki daidai da yawan kudin karatun da aka kashe a kansu.
Jarumin Maza, ya auri mata 3 cikin kwana 3

Jarumin Maza, ya auri mata 3 cikin kwana 3

Duk Labarai
Wani dan kasar Ghana dake zaune a birnin Dubai na hadaddiyar daular larabawa me suna Nicholas Mbir ya auri mata 3 a cikin kwanaki 3. Sunayen matan da ya aura sune kamar haka: Angelina Prah, Grace Agyarko, sai Esther Abass. An daura aurenne ranar April 26, 2025 a garin Winneba dake kasar ta Ghana. Da yawa sun jinjina masa.
Duk Arewa Babu Dan siyasar da ya kai Kwankwaso Butulci>>Inji Dan Balki Kwamanda

Duk Arewa Babu Dan siyasar da ya kai Kwankwaso Butulci>>Inji Dan Balki Kwamanda

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":["local"],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} A wata hira da ya yi da gidan radiyon jakadiya ɗan siyasar ya bayyana irin salon siyasar madugun Kwankwasiyya, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso da cewa ya butulce wa duk waɗanda suka taimake shi a siyasa, saboda haka canza shekar da ’yan majalissar jam'iyyarsa suka yi alama ce ta rasin ingantaccen shugabanci na jagoran na Jam'iyyar NNPP.
Ba mu damu da manyan ƴan siyasa a SDP ba, mun fi buƙatar ƴan dangwale – El-Rufai

Ba mu damu da manyan ƴan siyasa a SDP ba, mun fi buƙatar ƴan dangwale – El-Rufai

Duk Labarai
Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya ce sabuwar jam'iyyar da ya koma, SDP, ta fi buƙatar ta tara mambobi daga tushe ba wai manyan ƴan siyasa ba. El-Rufai, wanda ya fice da ga jam'iyyar APC a watannin baya, ya baiyana hakan ne bayan wani taron masu ruwa da tsaki da ya gudanar a jihar Kano a yau Litinin. A cewar sa, SDP jam'iyya ce da ke rajin farfaɗo da dimokuraɗiyya tun daga tushe domin gyaran Nijeriya. "Mu ba mu damu da tara manyan ƴan siyasa a SDP ba. Mun fi son mu ga kamar mutane miliyan 3 sun yi rijista a SDP. "SDP jam'iyya ce da za ta baiwa kowa dama iri ɗaya. Ba za mu bari wani mutum ɗaya ya riƙa iko da jam'iyyar ba. "So mu ke yi mu gyara dimokuraɗiyyar kasar nan," in ji El-Rufai, yayin da ya ke amsa tambayoyi daga manema labarai. Hakazalika El-Rufai ya ce...
An kàshè shanu 37 a jihar Plateau

An kàshè shanu 37 a jihar Plateau

Duk Labarai
Akalla shanu 37 aka harbe a ƙauyen Tashek da ke ƙaramar hukumar Riyom ta jihar Plateau a jiya Lahadi. A cewar shugaban reshen jihar na kungiyar Miyetti Allah , Ibrahim Yusuf Babayo, lamarin ya faru ne kusan ƙarfe 1:00 na rana. Wannan harin na baya-bayan nan ya faru ne kasa da mako guda bayan wani hari makamancin haka a ƙauyen Tanjol, wanda ma yana cikin ƙaramar hukumar Riyom, inda 'yan bindiga suka budewa makiyaya wuta, suka jikkata makiyaya biyu tare da kashe shanu biyar. Shugaban kungiyar ya bayyana harin a matsayin wanda ba tare da wani dalili ba, yana mai cewa lamarin wani ƙulli ne na masu aikata hakan domin cimma wani ɓoyayyen buri. Babayo ya ce, “'Yan bindiga sun mamaye yankin suka fara harbin shanun da ke kiwo, wanda ya kai ga mutuwar shanu 37 da kuma raunata wani makiya...
Gwamnatin taraiya ta umurci WAEC da NECO su koma zana jarrabawa ta na’ura mai ƙwaƙwalwa

Gwamnatin taraiya ta umurci WAEC da NECO su koma zana jarrabawa ta na’ura mai ƙwaƙwalwa

Duk Labarai
Gwamnatin taraiya ta umurci WAEC da NECO su koma zana jarrabawa ta na'ura mai ƙwaƙwalwa. Gwamnatin Taraiya ta umurci Hukumar Shirya Jarabawa ta Afirka ta Yamma (WAEC) da Hukumar Jarabawa ta Kasa (NECO) da su fara gudanar da dukkan jarabawarsu ta hanyar amfani da Kwamfuta (CBT) daga shekarar 2026. Ministan Ilimi, Dakta Tunji Alausa, ne ya bayyana hakan yayin da yake sa ido kan jarabawar da ake gudanarwa tare da jami'an JAMB, a Bwari, ranar Litinin. Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa fiye da dalibai miliyan biyu ne suka yi rajistar jarabawar da ake gudanarwa a fiye da cibiyoyi 800 a fadin kasar nan. Alausa ya bayyana cewa daga watan Nuwamba mai zuwa, WAEC da NECO za su fara gudanar da jarabawarsu ta bangaren tambayoyi (objective) ta hanyar CBT. A ...
Kwangila Kazantaccen Abu ce sam bai dace ace malami ya shiga harkar Kwangila ba a Najeriya>>Sheikh Maqari

Kwangila Kazantaccen Abu ce sam bai dace ace malami ya shiga harkar Kwangila ba a Najeriya>>Sheikh Maqari

Duk Labarai
Babban malamin addinin Islama Sheikh Ibrahim Maqari ya bayyana cewa kwagila kazantaccen abu ce da bai dace ace an samu malami yana yin ta ba. Ya bayyana hakane a wani faifan Bidiyon sa da ya watsu sosai a kafafen sadarwa. Malam yace a baya yana tunanin Shubuhar da ke cikin kwangila wani kasone, saidai yace wani masanin harkar Kwangila ya sanar dashi cewa kaso 100 bisa 100 na kwangila haka take. Yace yawanci ana bayar da itace a farashi sama dana kayan da za'a siya kuma dolene sai an baiwa wanda ya bayar da kwangilar kasonsa. Yace to irin wannan ai bai kamata ace malami ya shiga wannan harka a.
Kai ma ka taimaka wajen ƙara talauci a Najeriya’>>Gwanati ta mayarwa Peter Obi Martaninkan cewar da yayi talauci ya karu

Kai ma ka taimaka wajen ƙara talauci a Najeriya’>>Gwanati ta mayarwa Peter Obi Martaninkan cewar da yayi talauci ya karu

Duk Labarai
‘Kai ma ka taimaka wajen ƙara talauci a Najeriya’ — Sanwo-Olu ya kalubalanci Obi kan maganganunsa a jami'a a Amurka. Babajide Sanwo-Olu, gwamnan jihar Legas, ya soki Peter Obi, ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour Party (LP) a 2023, kan maganganun da ya yi game da hauhawar talauci a Najeriya. A ranar Alhamis da ta gabata, Obi, tsohon gwamnan Anambra, ya yi jawabi a jami'ar Johns Hopkins a Amurka kan taken: ‘Siyasa da Sauyi a Najeriya’. A cikin jawabin, Obi ya bayyana cewa Najeriya na da mafi yawan talakawa fiye da Indonesia, China da Vietnam. Obi ya wallafa wani ɓangare na jawabin nasa a shafin X. Sanwo-Olu, a cikin wata sanarwa, ya soki Obi kan "mugun ɗabi’a" da ke "ɓata suna da darajar Najeriya a idon duniya." Gwamnan Legas ya ce la'akari da abin da Obi ya cim...
Mataimakin shuaban kasa, Kashim Shettima ya isa Jihar Delta dan karbar gwamnan jihar da ya koma APC

Mataimakin shuaban kasa, Kashim Shettima ya isa Jihar Delta dan karbar gwamnan jihar da ya koma APC

Duk Labarai
Mataimakin shuaban asa, Kashim Shettima ya isa birnin Asaba na jihar Delta dan karbar gwamna jihar, Sheriff Oborevwori da ya kom jam'iyyar APC. Gwamnonin Kaduna, Nasarawa, Kogi, Sokoto, Gombe, Legas, da Yobene suka tarbi mataimakin shugaban kasar ayan isarsa birnin Asaba. A ranar 23 ga watan Afril ne gwamna Sheriff Oborevwori ya canja sheka daga PDP zuwa APC.