Thursday, March 5
Shadow
Kalli Bidiyon: Gwamnan Kaduna ya baiwa malaman Addinin Islama da suka taimaka masa yaci zabe kyautar Tsabar Naira Miliyan 10

Kalli Bidiyon: Gwamnan Kaduna ya baiwa malaman Addinin Islama da suka taimaka masa yaci zabe kyautar Tsabar Naira Miliyan 10

Duk Labarai
Gwamnan jihar Kaduna, Malam Uba Sani ya baiwa Malaman Addinin Musulunci da suka taimaka masa yaci zabe a 2023 tsabar Naira Miliyan 10. Sannan yace a rabawa musu shinkafa kowannensu. Kwamishinan kananan Hukumomi na jihar, Sadiq Mamman Legas ne ya bayyana haka yayin da yake mika kyautar kudin. https://twitter.com/i/status/2026385771251601582
Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: A cikin Azumin Ramadana an kama wata Musulma da dadironta Kirista a Jihar Katsina

Innalillahi wa’inna ilaihi raji’un: A cikin Azumin Ramadana an kama wata Musulma da dadironta Kirista a Jihar Katsina

Duk Labarai
Rahotanni daga Dutsin Ma ta jihar Katsina na cewa, a cikin watan Azumin Ramadana, Hukumar Hisbah ta jihar ta kama wata mata me shekaru 26 tare da dadironta wanda Kirista ne me shekaru 35 a garin Dutsin ma. Rahoton yace an kamasu ne suna zaman dadiro a daki daya duk da ana cikin watan Ramadana. An kamata ne bisa jagorancin Hisbah karkashin shugabanta, Malam Shafi'u Ibrahim. Rahoton dai yace masoyan na zaunene ba tare da aure ba. https://twitter.com/i/status/2026229362165415980
Kalli Bidiyon: Ko dai hadakarsu zata tabbata ne? An ga Bidiyon Kwankwaso da Gawuna

Kalli Bidiyon: Ko dai hadakarsu zata tabbata ne? An ga Bidiyon Kwankwaso da Gawuna

Duk Labarai
An ga wani Bidiyon Kwankwaso da gawuna da suka hadu a filin jirgin sama. Kwankwaso ya mikawa gawuna hannu su gaisa amma Gawuna yaki yadda ya bashi hannu inda ya durkusa har kasa ya gaisheshi. Hakan yasa wasu ke rade-radin ko dai maganar komawar Gawuna NNPP ya fito takarar shugaban kasa zata tabbata ne? https://twitter.com/i/status/2025933941249614145
‘Yan jihar Kogi sun fito sun nuna rashin jin dadinsu kan yanda Gwamnan Kaduna Malam Uba Sani ya ture Gwamnansu Usman Ododo a wajan taron ganawa da manema labarai

‘Yan jihar Kogi sun fito sun nuna rashin jin dadinsu kan yanda Gwamnan Kaduna Malam Uba Sani ya ture Gwamnansu Usman Ododo a wajan taron ganawa da manema labarai

Duk Labarai
Wasu 'yan jihar Kogi sun fito sun nuna rashin jin dadinsu kan yanda gwamnan Kaduna, Malam Uba Sani ya ture gwamnan jiharsu, Usman Ododo. A Bidiyon wanda ya rika yawo a kafafen sada zumunta, wanda kuma hutudole a kawo muku, An ga Gwamna Ododo na tsaye kusa da Gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma kamin Gwamna Malam Uba Sani ya tureshi. Mutanen na jihar Kogi da suke da kungiya a shafinsa X sun bayyana hakan da rashin girmamawa inda suka ce dolene Malam Uba Sani ya fito ya baiwa gwamnan su hakuri. Sun ce wannan abu ya zamarwa gwamnansu abin kunya ana maganarsa ana masa dariya. https://twitter.com/i/status/2026243744165413067
Kalli Bidiyon yanda Gwamnan jihar Kaduna ya ture na Kogi a wajan taron ganawa da manema labarai a fadar shugaban kasa

Kalli Bidiyon yanda Gwamnan jihar Kaduna ya ture na Kogi a wajan taron ganawa da manema labarai a fadar shugaban kasa

Duk Labarai
Wannan Bidiyon yanda Gwamnan jihar Kaduna Malam Uba Sani ya ture na Kogi kenan, watau Usman Ododo a wajan taron ganawa da manema labarai a Abuja. A jiyane shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya shiryawa gwamnonin Najeriya shan ruwa a fadarsa. Gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma a yayin da zai fara ganawa da manema labarai, ya kira Gwamnoni inda yace su zo su bashi karfin gwiwa inda na Delta dana Kogi suka je suka tsaya a kusa dashi. Saidai Gwamnan Kaduna yazo daga baya ya ture gwamnan Kogi gefe shi ya tsaya kusa da Gwamna Hope Uzodinma. https://twitter.com/i/status/2026197689617039649
Me magana da yawun tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai yayi cikakken bayani kan rashin Lafiyar dake damun El-Rufai a ind yake tsare

Me magana da yawun tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai yayi cikakken bayani kan rashin Lafiyar dake damun El-Rufai a ind yake tsare

Duk Labarai
Muyiwa Adekeye me magana da yawun tsohon Gwamnan jihr Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai, yayi cikakken bayani kan halin da El-Rufai ya ke ciki a inda yake tsare a hannun ICPC. Ya bayyana cewa, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai yayi fama da zubar jini ta yancinsa. Sannan an hana matarsa ta kai masa abinci kai tsaye, saidai ta baiwa wani jami'i ya mika masa. Adekeye yace sun mikawa kotu korafin neman a bayar da belin Malam Nasiru Ahmad El-Rufai.