'Yansandan Najeriya sun fara koyan yaren kasar China.
An gansu a wani Bidiyo wata 'yar kasar China na koya musu yaren har suna ta Dariya.
Rahoton yace ana koya musu ne kasancewar 'yan China sun yi yawa a Najeriya.
https://twitter.com/Uno_009/status/2098724360823406918
Babban me baiwa shugaban kasa shawara akan harkar siyasa, Ibrahim Masari ya je garin Malunfashi akan jirgi me saukar Angulu.
Lamarin ya dauki hankula a kafafen sada zumunta inda akai ta Muhawara.
https://twitter.com/ishaqsamaila5/status/2098720375869767728
Ana zargin Daya daga cikin manyan yaran dan takarar Gwamnan jihar Gombe, Farfesa Sheikh Isa Ali Pantami, watau Abba Pantami da yin wallafa a shafinsa na sada zumunta inda ya rubuta cewa, Idan Pantami ya ci zaben gwamnan jihar Gombe zai hana Maulidi.
Screenshot na rubutun nasa yana ta yawo a kafafen sada zumunta inda ake ta sharhi akai.
Inda a shafin Tauraron fina-finan Hausa Baba Sadiq aka fara ganin screenshot din wanda daga baya ya ci gaba da yaduwa.
Zuwa yanzu dai Abba Pantami bai ce komai kan lamarin ba.
Wannan wani me sayar da wayoyine da ya bude shago ya tarar an fasa shagon a kwashe masa kudi wayoyi da kwamfutoci.
Ya dora hannu akansa yana ihu yana fadar ya shiga uku ya lalace.
Lamari ya farune a kasuwar Ilesha dake jihar Osun
https://twitter.com/General_Somto/status/2098689994302885897
Gwamnatin jihar Benue ta kwace motoci 23 daga hannun Tsohon Gwamnan jihar Benue, Samuel Ortom bayan da ya kwashe su ya tafi dasu gidansa.
An ga yanda aka yi Amfani da Janwai wajan dauke motocin daga gidan tsohon Gwamnan.
Saidai Ortom yace wadannan motocin halas dinsa ne, Gwamnati ce ta mallaka masa
https://twitter.com/Onsogbu/status/2098442953567940666
Diyar tsohon gwamnan Kano, Fatima Umar Ganduje kenan a wadannan hotunan nata da suka dauki hankula
Ta dauki hotunan ne a kasar Ingila inda suke yawon shakatawa ita da mijinta sannan ta wallafa a shafinta na sada zumunta.
Yayin da wasu ke yaba mata, wasu na cewa Allah ya shirya.
Matashi ya zo da sauri ya kama sahun gaba ta yadda ba zai yi nesa da liman ba sosai, bayan an idar da sallah sai Sheikh Lukuwa Sokoto ya juyo ya fuskanci mutanen cikin masallaci sai aka fara zuwa ana gaisawa da shi, caraf sai matashin nan ya je kusa da malam don su gaisa, nan ne ya samu damar yiwa malam abinda bai kamata ba InnaliLLAH wa'inna ilaihi rajiun!
Cikin ikon Allah hanzarin da mutane suka yi wajan kaiwa malam dauki yasa matashin bai yi nasarar abinda yaje aikatawa ba, sai mutane suka kawo ɗauki aka kama shi kuma aka yi nasarar aika matashin lahira.
Wannan shi ne abin da ya faru, muna fata wannan zai zama izina ga sauran malamai da limamai sannan ƴan agaji da masu tsaron malamai da limamai su ma su zama masu lura da irin wannan salo.
Sannan rahoto ya zo cewa sauran masu i...
Wannan wata Kirista ce data yi kuskuren aikawa cocinta Naira Miliyan daya da dubu dari shidda da dubu arba'in da naira dari Biyu, 1,640,200.
Ta fito kafafen sada zumunta tana ta kuka tana fadin cewa wallahi kudin bana sadaka bane, kudin aiki ne aka bata kuma mutane nata damunta.
Tace idan akwai wanda yasan wanda ke kula da susun bankin cocin nata ya taimaka mata a musu magana su mayar mata da kudinta.
https://twitter.com/dammiedammie35/status/2098555590125490381
Bidiyon dan takarar shugaban kasa, Peter Obi da matarsa suna soyayya ya dauki hankulan mutane.
An gansu suna kama hannun juna da dai sauran abubuwa irin na masoya.
https://twitter.com/General_Somto/status/2098475463395971100
Wani matashi da ya afkawa Sheikh Musa Lukuwa a masallacin juma'arsa ya gamu da ajalinsa a wajan mabiyan malamin.
https://twitter.com/Bashar_G_Sokoto/status/2098453572606153138
Lamarin ya farune a masallacin malamin dake unguwar Mabera dake Jihar Sokoto bayan Sallar Juma'a.
Rahotanni sun ce an sallami Malam daga asibitin da ak kaishi dan bashi kulawar gaggawa bayan faruwar lamarin.