Monday, April 6
Shadow
Gidajen man fetur da ‘yan kasuwar man sun tafka Asara bayan da kamfanin mai na kasa, NNPCL ya rage farashin man fetur din inda a yanzu yake sayar dashi da Arha fiye da na Dangote

Gidajen man fetur da ‘yan kasuwar man sun tafka Asara bayan da kamfanin mai na kasa, NNPCL ya rage farashin man fetur din inda a yanzu yake sayar dashi da Arha fiye da na Dangote

Duk Labarai
' Yan kasuwar man fetur sun koka da sarar da suka tafka bayan da kamfanin mai na kasa NNPCL ya rage farashin man da yake sayarwa. A Legas, NNPCL na sayar da litar man fetur din aka farashin Naira 880 kan kowace lita yayin da a Abuja kuma NNPCL din na sayar da man fetur din akan farashin 935 akan kowace lita. Hakan na zuwane sati daya bayan da Dangote ya rage farashin man fetur din nasa. A Legas, Farashin man fetur din na NNPCL yafi na Dangote Arha da Naira 10. Saidai kamfanin na NNPCL ya baiwa 'yan kasuwar damar su sayar da tsohon man da suke dashi kamin fara amfani da sabon farashin.
Bakar fata dan kasar Ghana na cikin na gaba-gaba da ake tunanin zasu gaji Fafaroma

Bakar fata dan kasar Ghana na cikin na gaba-gaba da ake tunanin zasu gaji Fafaroma

Duk Labarai
Idan dai ana duba bunƙasar cocin Katolika ne wajen zaɓen fafaroma na gaba, da tabbas babu wani zaɓi illa daga Afirka. Afirka ce ke da mabiya Katolika da suka fi ƙaruwa cikin sauri a duniya, inda suka ƙaru da kashi 3.31 cikin 100 a shekara biyu tsakanin 2022 da 2023. Alƙaluma na baya-bayan nan daga Fadar Vatican kashi 20 na mabiya Katolika ne ke zaune a Afirka. A gefe guda kuma, nahiyar Turai ta fuskanci ƙaruwa mafi ƙanƙanta a wannan lokaci. Daga shekarar 1910 zuwa 2010, an samu raguwar mabiya ɗariƙar da sama da kashi 63, a cewar alƙaluman binicke na cibiyar Pew Research. Nahiyar ta Turai da ake yi wa kallon cibiyar Kiristanci ta duniya, yanzu ta zama ɗaya daga cikin mafiya nisa da addini gaba ɗaya. Duk da cewa har yanzu Katolika na da ƙarfi a nahiyar Latin Amurka, Ibanjilika na...
Yawan kayan da kamfanoni ke sayarwa a Najeriya sun ragu saboda mutane basu da kudin saye

Yawan kayan da kamfanoni ke sayarwa a Najeriya sun ragu saboda mutane basu da kudin saye

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa yawan kayan da kamfanoni ke sayarwa a Najeriya sun ragu saboda mutane basu da kudin saye. Kungiyar masu kamfanoni da masana'antu a Najeriya, MAN ne suka bayyana hakan. Rahoton yace an samu karuwar kayan da ba'a sayarba zuwa kaso 87.5 wanda darajar kayan sun kai Naira Tiriliyan 2.14 a shekarar 2014. Hakan ya nuna cewa yawan kayan da masana'antun basu siyarba ya karu idan aka kwatanta daga shekarar 2013 zuwa 2014. Kayan da suka fi fama da wannn matsala sun hada dana abinci, da lemukan kwalba, da taba da kayan sawa da takalma da sauransu.
Ba sai Buhari ya goyi bayan dan takara ba kamin yayi nasara a 2027>>Babachir David Lawal

Ba sai Buhari ya goyi bayan dan takara ba kamin yayi nasara a 2027>>Babachir David Lawal

Duk Labarai
Tsohon sakataren Gwamnatin Tarayya, Babachir David Lawal ya bayyana cewa ba sai tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya goyi bayan dan takara ba kamij dan takar yayi nasara akan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ba a shekarar 2027. Ya bayyana hakane a hirar da jaridar Punchng ta yi dashi inda yace suna zuwa gurin Buhari ne a matsayinsa na babba dan sanar dashi abinda zasu yi ya saka musu Albarka. Yace amma basa bukatar tsohon shugaban kasar ma ya shiga tafiyarsu dan suna da hankali da wayau sun san yanda zasu gudanar da al'amuransu. Babachir yace Gwamnatin Tinubu bata son talakawa ne shiyasa take kokarin ganin ta sakasu a wahalar da zata kai su ga halaka. Yace su kuma abinda suka fito dan karewa kenan talakawa da masu rauni.
Kokarin rage yawan kudaden dake hannun Al’ummar Najeriya da CBN ke yi ya ci Tura maimakon ma kudin dake hannun mutanen su ragu, karuwa suke

Kokarin rage yawan kudaden dake hannun Al’ummar Najeriya da CBN ke yi ya ci Tura maimakon ma kudin dake hannun mutanen su ragu, karuwa suke

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa matakan da babban bankin Najeriya, CBN ya dauka dan rage yawan kudaden dake hannun 'yan Najeriya basu bayar da sakamakon da ake so ba. Babban bankin Najeriya ya dauko matakai masu tsauri sosai dan ganin an rage yawan kudaden dake hannun mutane a Najeriya amma hakan bata samu ba. Rahoton yace fiye da kaso 90 na tsabar kudin dake yawo a Najeriya na hannun mutanene basa cikin bankuna. Wanda hakan ke kara nuna cewa mutane sun fi yadda da yin ciniki da kudin zahiri fiye da amfani da banki ko fasahar kasuwanci ta zamani. Hakan na faruwa ne duk da kokarin gwamnati na karfafa gwiwar mutane wajan rage yawa amfani da tsabar kudi a yayin gudanar da kasuwanci. Masana tattalin arziki dai sun bayyana cewa idan kudi suka yi yawa a hannun mutane, kayan masarufi za...
Shugaba Tinubu zai gana da kwamandojin tsaro dan magance matsalar Kàshè-Kàshè

Shugaba Tinubu zai gana da kwamandojin tsaro dan magance matsalar Kàshè-Kàshè

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zai gana da kwamandojin tsaro da babban me bashi shawara kan harkar tsaro, Malam Nuhu Ribadu dan shawo kan matsalar yawaitar kashe-kashen da ake samu. Shugaba Tinubu ya dawo Najeriya a daren jiya bayan kwashe sama da sati biyu yana hutu a Turai. A yayin da yake wannan hutun an kashe mutane sama da 120 sannan an jikkata wasu yayin da aka raba wasu da muhallansu. Jihohin da suka fi fuskantar wannan matsala sune Benue, da Filato. Wata majiya ta bayar da tabbacin cewa, shugaban zai gana da masu ruwa da tsaki a bangaren tsaro dan kawo karshen matsalar.
Kar a saka min kayan kyale-kyale ko Alatu a kabarina>>Wasiyyar Fafaroma

Kar a saka min kayan kyale-kyale ko Alatu a kabarina>>Wasiyyar Fafaroma

Duk Labarai
Marigayi shugaban cocin katolika da ya mutu, watau Fafaroma Francis ya bar wasiyyar cewa, kada a saka masa kayan Alatu a kabarinsa. Tun a shekarar 2022 ne ya rubuta wannan wasiyyar inda yace kuma yana so a binneshine a Rome wanda rabon da a binne Fafaroma a wannan waje tun shekarar 1669. Fararoma Francis ya mutu yana da shekaru 88 inda ya sha yabo saboda soyayyar da yake nunawa Talakawa, 'yan Luwadi, 'yan Gudun Hijira, Falasdinawa da sauransu.
Da Duminsa: Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo Najeriya bayan kwashe kwanaki 19 a Turai yana hutawa

Da Duminsa: Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo Najeriya bayan kwashe kwanaki 19 a Turai yana hutawa

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dawo Najeriya a yau, Litinin bayan kwashe kwanaki 19 a Turai yana hutawa. Dama dazu da rana fadar shugaban kasar tace yau zai dawo Najeriya. Da farko dai an bayyana cewa sati biyu shugaban kasar zai yi amma daga baya sai gasho ya wuce hakan, wanda lamarin ya fara saka 'yan Najeriya cikin damuwa.
Ji yanda aka yi daurin auren dan ministan kudi ba tare da kowa ya sani ba saboda yace bai son Almubazzaranci musamman saboda halin da ‘yan Najeriya ke ciki

Ji yanda aka yi daurin auren dan ministan kudi ba tare da kowa ya sani ba saboda yace bai son Almubazzaranci musamman saboda halin da ‘yan Najeriya ke ciki

Duk Labarai
An daura auren dan ministan Kudi Wale Edun, me suna Mr. Tobi Edun a asirce ba tare da kowa ya sani ba. Daurin auren ya samu halartar manyan mutane ma'aikatan gwamnati na 'yan kasuwa amma ba'a yi Sharholiya ba. Ministan kudin ne ya bukaci kada a yi almubazzaranci wajan bikin dan nasa. Inda ake tsammanin ya dauki wannan mataki ne musamman saboda halin matsin da mafi yawan 'yan Najeriya ke ciki, kamar yadda wata majiya a kusa dashi ta gayawa jaridar Vanguard.