Saturday, April 11
Shadow
Samun Soyayyar Rahama Sadau, Ya Fi Samun Naira Milyan Dari, Ra’ayin Hon Ibrahim Ajeebo

Samun Soyayyar Rahama Sadau, Ya Fi Samun Naira Milyan Dari, Ra’ayin Hon Ibrahim Ajeebo

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Samun Soyayyar Rahama Sadau, Ya Fi Samun Naira Milyan Dari, Ra'ayin Hon Ibrahim Ajeebo Me za ku ce?
Ji labarin yanda wata ta mutu ta dawo a jihar Kano

Ji labarin yanda wata ta mutu ta dawo a jihar Kano

Duk Labarai
BABBAR MAGANA: Tun Cikin Azumi Aka Yi Zaton Ța Mùtu Sai Gashi Ta Dawò Gida, Ashe Ba Ita Ta Mùťù Bà. Billahillazi yanzu a daren nan aka kawo min wani labari a cikin garin Kura dake Kano Wallahi Tallahi wai wata yarinya ce Allah Ya yi mata rasuwa tun a cikin azumi sai yau aka ganta kawai ta dawo gida luma Wallahi ita ce. Ni ma ina zaune ina cin abinci aka zo ana fada min ban yadda ban gama cin abincin ba na tashi na je domin na gani da idona. Wallahi ina zuwa har unguwar tasu kawai na ga kofar gidan su yarinyar cike da mutane na ta shiga ana ganinta. Ni ma na ganta Wallahi abun dai akwai mamaki sosai. Abu kamar a fim mutum ya mutu amma ya dawo. Adreshin unguwar da yarinyar take Alkalawa ne a cikin garin Kura dake Kano. Amma dai abun akwai mamaki sosai Wallahi. Ikon Allah. ...
Bùďùŕwà Ta Ķàšhè Kànťa Ta Hanyar Fàdawà Ŕijìya Saboda Śàurayinta Yà Çe Bà Ya Sòntà

Bùďùŕwà Ta Ķàšhè Kànťa Ta Hanyar Fàdawà Ŕijìya Saboda Śàurayinta Yà Çe Bà Ya Sòntà

Duk Labarai
Bùďùŕwà Ta Ķàšhè Kànťa Ta Hanyar Fàdawà Ŕijìya Saboda Śàurayinta Yà Çe Bà Ya Sòntà. Maijidda Ilu, ta rasa ranta sakamakon fàďàwa wani tsohon rijiya da ta yi. Hakan ya faru ne a Unguwan Kan Bariki dake Garin Kumo karamar hukumar Akko jihar Gombe. Sabanin fahimta ya shiga tsakanin ta da saurayin ta mai suna Umar, ya ce baya sonta, wanda daga jin haka, sai ta fùśàta, ta fada rijìýa inda hakan ya yi sanadiyar ŕasà ranta. Tuni dai jami'an tsaron 'yan sanda suka tusa keyar matashi Umar domin amsa tambaboyi da bincike.
Wanda suke bani kyauta a baya sune yanzu suke rokona in basu kudi saboda matsin tattalin arziki>>Inji Peter Obi

Wanda suke bani kyauta a baya sune yanzu suke rokona in basu kudi saboda matsin tattalin arziki>>Inji Peter Obi

Duk Labarai
Dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour Party, Peter Obi ya bayyana cewa, wadanda ke bashi kyauta a shekarun da suka gabata a yanzu sune ke neman ya tallafa musu. Peter Obi ya bayyana hakane a wajan taron Jam'iyyar Labour party din da ya wakana a Abuja. Yace zasu shiga zabe me zuwa a shirye kuma zasu tsayar da mutane na gari a matsayin 'yan takara. Peter Obi ya kara da cewa, matsin tattalin arziki yayi tsanani ta yada wanda a baya suke gayyatarsa yana cin abinci tare dasu amma yanzu sune ke neman ya taimaka musu.
Kada wanda muka sake jin ya biya masu Gàrkùwà da mutane kudin fansa>>Me baiwa shugaban kasa shawara kan Tsaro, Nuhu Ribadu ya gargadi ‘yan Najeriya

Kada wanda muka sake jin ya biya masu Gàrkùwà da mutane kudin fansa>>Me baiwa shugaban kasa shawara kan Tsaro, Nuhu Ribadu ya gargadi ‘yan Najeriya

Duk Labarai
Babban me baiwa shugaban kasa shawara kan tsaro, Malam Nuhu Ribadu ya gargadi 'yan Najeriya da cewa, kada wanda ya sake baiwa masu garkuwa da mutane kudin fansa. Ya bayyana hakane a Kaduna yayin da yake karbar wasu da aka yi garkuwa dasu amma jami'an tsaro suka kubutar dasu mutane 60. Nuhu Ribadu ya bayyana cewa, biyan masu garkuwa da mutanen kudin fansa yana kara karfafa musu gwiwa kuma hakanne zai sa su ci gaba da neman kudin fansar. Yace Gwamnati na iya bakin kokarinta na ganin ta bisu har maboyarsu ta yi maganinsu.
Rashin tsaro da kashe-kashe sun ragu da kashi 90% a Najeriya, in ji NSA, Ribadu

Rashin tsaro da kashe-kashe sun ragu da kashi 90% a Najeriya, in ji NSA, Ribadu

Duk Labarai
Mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Nuhu Ribadu ya bayyana cewa Najeriya ta samu raguwar rashin tsaro da kashe-kashe da kusan kashi 90 a gwamnatin shugaba Bola Tinubu. Ribadu ya bayyana haka ne a garin Jos na jihar Filato a lokacin da ya ke zantawa da manema labarai jim kadan bayan wata ganawa da kwamandan rundunar ‘Operation Safe Haven’ Manjo Janar Folusho Oyinlola a ofishinsa, biyo bayan harin da yan indiga suka kai kan al’ummar Bokkos wanda ya yi sanadin mutuwar mazauna garin da dama. A cewarsa, gwamnatin shugaba Tinubu ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a kasar nan. “A cikin shekaru 1-10 da suka wuce, an rage yawan da kusan kashi 90 cikin 100 a kasarmu. "Muna da kididdigar ta shekarar 2022 da 2023, inda aka nuna cewa wadanda s...
Da wuya ka ga kasar da ta ci gaba a karkashin tsarin mulkin Dimokradiyya>>Inji Shugaban kasar Burkina Faso, Captain Ibrahim Traoré

Da wuya ka ga kasar da ta ci gaba a karkashin tsarin mulkin Dimokradiyya>>Inji Shugaban kasar Burkina Faso, Captain Ibrahim Traoré

Duk Labarai
shuganan kasar Burkina Faso, Captain Ibrahim Traore ya bayyana cewa da wuya ka ga kasar da ta samu ci gaba a karkashin tsarin Dimokradiyya. Ya bayyana hakane a fadarsa yayin kaddamar da wani shiri. Yace yawanci sai kasa ta samu daidaito ne sai daga baya ta koma kan tsarin Dimokradiyya. Yace amma ci gaba ana samunsa ne ta hanyar juyin juya hali.
An kama soja, Private Sadiq Sani bisa zargin fashi da makami

An kama soja, Private Sadiq Sani bisa zargin fashi da makami

Duk Labarai
' Yan sanda a jihar Naija sun kama soja, Private Sadiq Sani bisa zargin aikata Fashi da makami. An kamashi kuma da zargin cin zaafin wani dan kasuwa me suna Abdulrahman Salihu. Rahoton yace, Soja Sadiq ya je shagon Abdulrahman Salihu da sallah inda ya sayi kaya, sai yace a bashi account Number ya tura kudi. Saidai bayan da ya karbi account number din dan kasuwar yayi zargin wani abu inda yace ba zai bashi kayan ba sai ya ga Alert. Daga nan ne sai sojan ya aika da alert din karya. Ko da dan kasuwar ya ga haka sai rikici ya barke tsakaninsu inda sojan ya fitar da wuka ya yanki dan kasuwar sannan ya tsere. An sanar da 'yansanda inda suka bi sojan har gidansa dake Limawa a garin Minna suka kamashi. An kaiwa hukumar soji rahoton abinda sojan ya aikata inda wani babba...