Sunday, July 26
Shadow
Farashin kayan masarufi sun yi sauki a Najeriya

Farashin kayan masarufi sun yi sauki a Najeriya

Duk Labarai
An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga kashi 24.23 a watan Maris ɗin 2025 zuwa kashi 23.71 a watan Afrilun 2025. Hukumar Ƙididdiga ta Najeriya, NBS ta ce hauhawar farashin da aka samu a watan Afriliu ya nuna an samu ragin kaso 0.52 na hauhawar idan aka kwatanta da watan Maris. “Wannan na nuni da cewa hauhawar farashin Ta shekara-shekara Ta ragu a watan Afrilun 2025 idan aka kwatanta da watan Afrilun 2024." Dangane kuma da hauhawar farashin kayan abinci a watan Afrilun 2025 ta kasance kaso 21.26 kamar yadda ke faruwa a shekara-shekara.
KARON FARKO: Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump, ya ziyarci Babban Masallacin Sheikh Zayyad da ke Abu Dhabi, wanda ke ɗaya daga cikin manyan masallatai a duniya mai cike da fasahar gini ta zamani

KARON FARKO: Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump, ya ziyarci Babban Masallacin Sheikh Zayyad da ke Abu Dhabi, wanda ke ɗaya daga cikin manyan masallatai a duniya mai cike da fasahar gini ta zamani

Duk Labarai
KARON FARKO: Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump, ya ziyarci Babban Masallacin Sheikh Zayyad da ke Abu Dhabi, wanda ke ɗaya daga cikin manyan masallatai a duniya mai cike da fasahar gini ta zamani. Trump ya ziyarci masallacin ne a yayin ziyararsa zuwa babban birnin Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE). Ya samu rakiyar Sheikh Khaled bin Mohamed, Yarima Mai Jiran Gado na Abu Dhabi.
Hadiza Gabon Ta Gayyaci Ustaz Alqali Abubakar Salihu Zaria Cikin Shirin Gabon Room Talk Show

Hadiza Gabon Ta Gayyaci Ustaz Alqali Abubakar Salihu Zaria Cikin Shirin Gabon Room Talk Show

Duk Labarai
Hadiza Gabon Ta Gayyaci Ustaz Alqali Abubakar Salihu Zaria Cikin Shirin Gabon Room Talk Show. {"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Fitacciyar ‘yar fim kuma mai gabatar da shirin Gabon Room Talk Show, Hadiza Gabon, ta gayyaci sanannen Malamin addini, Ustaz Alqali Abubakar Salihu Zaria, domin tattaunawa da shi a shirin da ta ke gabatar wa. Shin ko kuna ganin zata iya ƙure shi kamar yadda ta saba ƙure mutane?
YANZU-YANZU: ‘Yan Majalisar Tarayya Biyu Daga Jihar Kano, Honarabul Kabir Rurum Da Abdullahi Sani Sun Sanar Da Ficewar Su Daga Jam’iyyar NNPP Zuwa APC A Hukumance

YANZU-YANZU: ‘Yan Majalisar Tarayya Biyu Daga Jihar Kano, Honarabul Kabir Rurum Da Abdullahi Sani Sun Sanar Da Ficewar Su Daga Jam’iyyar NNPP Zuwa APC A Hukumance

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} 'Yan Majalisar Tarayya Biyu Daga Jihar Kano, Honarabul Kabir Rurum Da Abdullahi Sani Sun Sanar Da Ficewar Su Daga Jam'iyyar NNPP Zuwa APC A Hukumance
Masu Ikirarin Jìhàdì sun shiga Uku, An fito da rundunar sojojin da basu taba yin rashin nasara ba an kaisu Arewa Maso gabas, sojojin kansu sai murna suke

Masu Ikirarin Jìhàdì sun shiga Uku, An fito da rundunar sojojin da basu taba yin rashin nasara ba an kaisu Arewa Maso gabas, sojojin kansu sai murna suke

Duk Labarai
Rahotanni da hutudole ke samu na cewa Rundunar sojojin Najeriya ta fito da daya daga cikin rundunar sojojin ta mafi karfi da bayar da sakamakon da ake so wajan yaki inda aka kaisu Arewa maso gabas. Sunan rundunar shine 134 Special Forces Battalion Wanda a baya sun yi yaki tare da rundunar sojoji da Najeriya ta dauoo haya daga kasar Afrika ta Kudu a shekarar 2013 suka yaki Boko haram,. Rundunar ta kuma taba yaki a Kangarwa dake jihar ta Borno a lokacin da aka yi fama da 'yan Bindiga wadanda ba B0k0 Hàràm ba kuma ta gama dasu. Sannan a shekarar 2019, sun kuma yaki B0k0 Hàràm inda kuma suka yi nasara. Hakanan a shekarar 2022 an kai rundunar jihar Kaduna inda ta yaki 'yan Bindiga a camma kuma ta yi nasara. Sojojin dake Arewa maso gabas rahotanni sun bayyana cewa sai murna suke d...
Ji yanda dan majalisa yawa abokan aikinsa tonon silili, yace yanzu kowane Sanata ana bashi Naira Biliyan 2 dan majalisar wakilai kuma Naira Biliyan 1 dan suwa mutanen mazabarsu aiki tun bayan da shugaba Tinubu ya cire tallafin man fetur

Ji yanda dan majalisa yawa abokan aikinsa tonon silili, yace yanzu kowane Sanata ana bashi Naira Biliyan 2 dan majalisar wakilai kuma Naira Biliyan 1 dan suwa mutanen mazabarsu aiki tun bayan da shugaba Tinubu ya cire tallafin man fetur

Duk Labarai
Wani dan majalisar tarayyar Najeriya yawa abokan aikinsa Tonon Silili inda yace babu dan majalisar dake samun kasa da Naira Biliyan 2 na yiwa mazabarsa aiki a majalisar dattijai. Yace hakanan a bangaren 'yan majalisar wakilai, babu wanda ke samun kasa da Naira Biliyan 1 shima dan yiwa 'yan mazabarsa aiki. Ya bayyana hakane a jihar Osun, kamar yanda jaridar Sahara reporters ta ruwaito. Saidai ba'a bayyana sunansa ba, yace 'yan majalisar sun samu karin kudinne bayan da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya cire tallafin man fetur. Hakanan yace suma Gwamnoni an kara musu kudaden da ake basu na yiwa jihohinsu aiki. Wannan dai ya zowa mutane da mamaki ganin yanda 'yan majalisar ke kukan suma suna cikin wani hali a yayin da 'yan Najeriya ke kokawa da tsadar rayuwa.