Monday, April 13
Shadow
Dakatarwar da nawa Fubara taimakonsa na yi, dan da ban dakatar dashi ba da Tuni majalisar jihar Rivers ta tsigeshi>>Shugaba Tinubu

Dakatarwar da nawa Fubara taimakonsa na yi, dan da ban dakatar dashi ba da Tuni majalisar jihar Rivers ta tsigeshi>>Shugaba Tinubu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, dakatarwar da yawa Gwamnan jihar Rivers, Simi Fubara ce ta hana majalisar jihar tsigeshi a matsayin gwamna. Ya bayyana haka ta bakin lauyan Gwamnati, kuma Ministan Shari'a, Lateef Fagbemi inda yace da basu dakatar da Gwamna Fubara ba da tuni an tsigeshi. Yace kuma da an tsigeshi da shikenan yayi batan bakatantan. Yace amma dakatarwar ta Fubara wata dabara ce ta hana tsigeshi. Shugaba Tinubu dai ya dakatar da Gwamna Fubara har na tsawon watanni 6.
A cikin Azumin Watan Ramadana, An kama dan shekaru 35, Abdullaziz Mohammed da yiwa karamar yarinya me shekaru 5 fyade a jihar Adamawa

A cikin Azumin Watan Ramadana, An kama dan shekaru 35, Abdullaziz Mohammed da yiwa karamar yarinya me shekaru 5 fyade a jihar Adamawa

Duk Labarai
'Yansanda a jihar Adamawa sun kama dan shekaru 35 Abdullaziz Mohammed da zargin yiwa karamar yarinya me shekaru 5 fyade a jihar. Kakakin 'yansandan jihar, CSP Suleiman Nguroje ne ya bayyana haka inda yace lamarin ya farune a karamar hukumar Mubi dake jihar. Yace mahaifin yarinyar me ya kai musu kara ranar March 17, 2025 inda yace Abdulaziz ya ja diyarsa zuwa cikin wani dakin da ake Nika a Kasuwar Barkono dake Mubi ya mata fyade. Tuni dai aka tafi da yarinyar zuwa Asibiti. Yayin da shi kuma wanda ake zargi ya amsa laifinsa. Kwamishinan 'yansandan jihar yayi Allah wadai da lamarin inda ya aika da wanda ake zargi zuwa sashen binciken manyan laifuka na jihar.
Dakatarwar da Shugaba Tinubu yawa Gwamnan jihar Rivers, Simi Fubara na Tangal-Tangal yana ta neman ‘yan Majalisa su amince masa domin idan basu amince ba dole ya janye dakatarwar

Dakatarwar da Shugaba Tinubu yawa Gwamnan jihar Rivers, Simi Fubara na Tangal-Tangal yana ta neman ‘yan Majalisa su amince masa domin idan basu amince ba dole ya janye dakatarwar

Duk Labarai
Rahotanni sun bayana cewa, dakatarwar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya wa gwamnan jihar Rivers Simi Fubara na Tangal-Tangal. Dalili kuwa sai an samu biyu bisa uku na 'yan majalisar dattijai dana majalisar wakilai duka sun amince masa kamin wannan dakatarwa ta tabbata. A yanzu haka rahotanni, kamar yanda jaridar TheCable ta ruwaito na cewa, wakilan shugaban kasar sai kai kawo suke a tsakanin 'yan majalisar dan ganin sun samo kansu sun amince da dakatar da Gwamnan jihar Rivers din. Saidai matsalar itace mafi yawanci 'yan majalisar basa Najeriya, da yawansu sun je aikin Umrah inda wasu ke wasu kasashen. Hakanan wata matsala itace banda 'yan majalisar dake jam'iyyun Adawa, har wadanda ke jam'iyyar APC an samu suna nuna rashin amincewa da wannan dakatarwar da akawa Gwamnan ji...
Bamu san da zaben kiranye da akewa Sanata Natasha Akpoti ba>>Inji INEC

Bamu san da zaben kiranye da akewa Sanata Natasha Akpoti ba>>Inji INEC

Duk Labarai
Hukumar zabe me zaman kanta, INEC wadda itace ke da alhakin gudanar da zaben yin kiranye na duk wani zababben dan siyasa tace bata san da maganar zaben kiranye da akewa Sanata Natasha Akpoti ba. A jiyane dai Bidiyo da hotuna suka bayyana inda aka ga mutane da yawa a mazabar sanata Natasha Akpoti suna gudanar da abinda aka kira da zaben kiranye dan ta dawo gida ta daina wakiltarsu a majalisar Dattijai. An gudanar da zaben yanke kauna ga Sanata Natasha Akpoti a karamar hukumar Okehi dake jihar. Wani me suna Nura Abdullahi da aka yi hira dashi game da lamarin yace suna zabenne dan Sanata Natasha Akpoti bata wakiltarsu da kyau sannan kuma ta kasa magance matsalolin talauci, Ilimi da gyaran abubuwan more rayuwa. Saidai an gano cewa an yaudari mutanene da cewa za'a basu tallafine amm...
An kai karin jami’an tsaro dubu 10 Jihar Rivers bayan dakatar da Gwamna Fubara

An kai karin jami’an tsaro dubu 10 Jihar Rivers bayan dakatar da Gwamna Fubara

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Rivers na cewa,karin jami'an tsaron Civil Defense dubu 10 ne aka kai jihar Rivers dan su samar da tsaro bayan dakatar da Gwamna Fubara. Rahotannin sun ce an kai jami'an tsaronne dan su hadu da sojoji da sauran jami'an tsaron dake jihar dan su samar da tsaro ga bututun man fetur dake jihar. Kakakin hukumar ta Civil Defense, Afolabi Babawale ya tannatar da hakan, yayi kira da a daina fasa bututun man inda yace jami'ansu dubu 10 ne aka kai jihar ta Rivers dan su hana hakan. Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu dai ya dakatar da Gwamna Fubara bayan da aka fasa bututun man fetur a jihar har sau 3.
Doka bata baka damar tsige zababben Gwamna ba>>El-Rufai ya gayawa Tinubu

Doka bata baka damar tsige zababben Gwamna ba>>El-Rufai ya gayawa Tinubu

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Tsohon Gwamna jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyanawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu cewa, doka bata bashi ikon tsige zababben gwamna ba. El-Rufai ya bayyana hakane jawabin da ya wallafa a shafinsa na X. Yace tabbas shugaban kasa na da cikakken iko amma ikonsa bai hada da tsige zababben gwamna ba. Ya bayyana cewa, dakatar da gwamnan jihar Rivers da Tinubu yayi ba daidai bane inda yayi kiran a mayar da Simi Fubara kan mukaminsa. Yace tabbas dalilin da shugab...
Kalli Bidiyo: El-Rufai yana yawan taimakon mutane amma daga baya sai su ci amanarsa>>Inji Gwamnan Kaduna, Malam Uba sani

Kalli Bidiyo: El-Rufai yana yawan taimakon mutane amma daga baya sai su ci amanarsa>>Inji Gwamnan Kaduna, Malam Uba sani

Duk Labarai
Gwamnan Kaduna, Malam Uba Sani ya bayyana cewa, Tsohon Gwamnan jihar, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai na da yawan taimako amma matsalar da ake samu shine mafi yawan lokuta mutane na yaudararsa ne ko suna cin amanarsa. Ya bayyana hakane a wani bidiyo da ya watsu sosai a kafafen sada zumunta. Yace Tunda yake da El-Rufai bai taba ganin yana kokarin siyasa kansa gida ba ko iyalansa, a ko da yaushe yana kokarin taimakon mutanene. Yace dan haka suna tare dashi kuma zasu bashi kariya da goyon baya. Kalli Bidiyon anan Da alama dai wannan tsohon Bidiyone dan kuwa tuni dangantaka ta yi tsami tsakanin Malam Nasiru Ahmad El-Rufai da Gwamna Uba Sani inda El-Rufai ya fada a gidan talabijin na Arise TV cewa Uba Sani ba abokinsa bane, sun bata.
Kalli Bidiyo DA ƊUMI-ƊUMI: An Samu Fashewar Tankar Man Fetur A Yammacin Wannan Rana Ta Laraba A Dai-dai Kasan Gadar Karu Abuja Kan Hanyar Zuwa Keffi A Kalla Sama Da Motoci 20 Ne Suka Ķone

Kalli Bidiyo DA ƊUMI-ƊUMI: An Samu Fashewar Tankar Man Fetur A Yammacin Wannan Rana Ta Laraba A Dai-dai Kasan Gadar Karu Abuja Kan Hanyar Zuwa Keffi A Kalla Sama Da Motoci 20 Ne Suka Ķone

Duk Labarai
An Samu Fashewar Tankar Man Fetur A Yammacin Wannan Rana Ta Laraba A Dai-dai Kasan Gadar Karu Abuja Kan Hanyar Zuwa Keffi A Kalla Sama Da Motoci 20 Ne Suka Ķone. Idan Kana Da Mutanen Dake Bin Hanyar Karu, Nyanya Maraba A Abuja, Ko Zama Wadannan Yankuna, To Ku Kira Su Ku Ji Don Sanin Ko Suna Cikin Koshin Lafiya, Saboda Tankar Mai Ta Fashe A Hanyar Abuja Zuwa Nyanya, Inda Ta Yi Sanadiyar Mùțùwar Mutane Da Dama A Daidai Lokacin Shan Ruwa A Yau Laraba Jama'a a taimaka a yada (sharing) domin sako ya isa ga jama'a. Daga Yãhäyæ Yàküßù Àlhãssāñ. Kalli Bidiyon anan Kalli Karin Bidiyo Kalli karin Bidiyo anan
Ku Daina Takalarmu, Tinubu zai iya tsige kowane gwamna, na jihar Rivers ne tsautsai ya fada kanshi ya zama na farko>>Tinubu ya gargadi Gwamnoni

Ku Daina Takalarmu, Tinubu zai iya tsige kowane gwamna, na jihar Rivers ne tsautsai ya fada kanshi ya zama na farko>>Tinubu ya gargadi Gwamnoni

Duk Labarai
Babban lauyan Gwamnati, Lateef Fagbemi ya kare matakin da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dauka na dakatar da gwamnan jihar Rivers. Inda yace shugaban kasar na da karfin ikon dakatar da kowanw Gwamna. Fagbemi ya gargadi gwamnonin cewa duk gwamnan dake neman zama barazana ga Gwamnatin Tinubu na iya fuskantar dakatarwa. Yace a yau gwamnan jihar Rivers ne a gobe zai iya zama kowane Gwamna. Ya gargadi cewa babu wanda zasu bari ya mayar da Dimokradiyya abin wasansa.
Bidiyo Da Duminsa: Mutanen mazabar Sanata Natasha Akpoti sun fara zaben dan yi mata kiranye ta sauka daga wakilcinsu da take a majalisar Dattijai

Bidiyo Da Duminsa: Mutanen mazabar Sanata Natasha Akpoti sun fara zaben dan yi mata kiranye ta sauka daga wakilcinsu da take a majalisar Dattijai

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, mutanen mazabar Sanata Natasha Akpoti daga jihar Kogi sun fara yin zabe dan yi mata kiranye ta dawo daga wakiltarsu da take a majalisar Dattijai. Bidiyo ya nuna yanda tuni aka fara kada kuri'a dan yiwa Sanata Natasha Akpoti kiranye. Sanata Natasha Akpoti dai ta zargi kakakin majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio da nemanta da lalata zargin da ya karyata. Dalilin haka aka dakatar da ita daga ayyukan majalisar na tsawon watanni 6. kalli Bidiyon zaben anan