Ma'aikatar lafiya ta Lebanon ta ce Isra'ila ta kashe mutum aƙalla 100 a wasu hare-hare ta sama da ta kai ƙasar.
Hakan na kunshe ne cikin sabbin alkaluma da ma'aikatar ta fitar, inda ta ce an kuma jikkata mutum sama da 400.
Hezbollah ta harba gomman rokoki zuwa kudancin Isra'ila, a cewar ƙungiyar a wata sanarwa.
Ta ce ta far wa shingayen sojoji da kuma wuraren ajiye makamai ta hanyar amfani da makamai masu linzami,a wani matsayin martani ga hare-haren da Isra'ilar ta kai kudancin ƙasar.
A wata sanarwa ta daban, dakarun tsaron Isra'ila (IDF), sun ce an harba rokoki aƙalla 35 daga Lebanon kuma hakan ya shafi shingayensu.
An jikkata wani mutum mai shekara 50 a yankin Galilee, a cewar sojoji Isra'ila.
Sanarwar ta ƙara da cewa sojin saman ƙasar sun kakkaɓo rokoki da dama da Hezbollah ɗin ta harba yayin da wasu kuma suka yi lahani a wasu yankuna kusa da garin Ami'ad.
Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya bayyana cewa ya zuwa ranar Lahadin da ta gabata, gwamnatin jihar ta karɓi kusan naira biliyan huɗu da rabi daga cikin fiye da naira biliyan 13 da aka yi musu alƙawari a matsayin tallafi ga waɗanda ibtila'in ambaliya ya shafa a Maiduguri.
"...naira 4,441,494,902.81 ne suka shigo hannunmu daga cikin alƙawuran N13,195,500,000 da aka yi mana. Za mu ci gaba da sanar da jama'a duk lokacin da aka samu ƙarin shigowar kuɗi" In ji gwamna Zulum.
Farfesa Zulum ya bayyana hakan ne a lokacin da yake kafa kwamitin mutum 35 da zai kula da raba wannan tallafi ga waɗanda al'amarin ya shafa.
Wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar, Bukar Tijjani ya fitar, ya wallafa a shafin X na gwamna Zulum, gwamnan ya ce kwamitin zai ƙunshi wakilai daga hukumomi da ...
Wani tsoho dakw rawa a wajan Maulidi ya dauki hankula sosai bayan da aka ga bidiyonsa a shafukan sada zumunta.
Kalli Bidiyon a kasa:
https://twitter.com/bb_khamees/status/1837826273663414293?t=R_hZyH8aRHUgtZ0lNpgtmQ&s=19
Wasu dai na ganin hakan bai dace ba inda wasu ke cewa duk cikin shauki ne.
Ban Take Sunan Annabi Muhammad S.A.W A Jikin Kafet Dina Ba, Sunana Ne A Jiki, Amma Duk Wanda Yake Da Wata Gamsasshiyar Hujja Da Ta Fi Tawa, A Shirye Nake Da Na Karbi Gyara, Inji Sarki Muhammadu Sanusi II
Kasar Yahudawan Israela sun jefawa kasar Lebanon Rokoki 300 a wani sashi na ci gaba da yakin da suke da kungiyar Hezbollah.
Kasar ta Israela dai a cewarta ta gargadi fararen hula dasu tashi daga kusa da gidajen 'yan kungiyar Hezbollah kamin su kai hare-haren.
Kasar tace ta gano 'yan Kungiyar Hezbollah dake shirin kai mata hare-haren Rokoki shine ta dakile su.
Rahotanni sun bayyana cewa, hukumar Hisbah dake Kano ta Hafsat Baby wadda aka fi sani da hafsa Lawancy 'yar Tiktok wadda Bidiyon tsiraicinta ya bayyana.
A wani bidiyo dake ta yawo a kafafen sada zumunta, an ga Hafsat da wasu sauran mata a tsugune a ofishin Hisbah.
Tuni shugaban hukumar ta Hisbah ta Kano,Malam Aminu Ibrahim Daurawa ya tabbatar da kama Hafsat baby.
A wasu Rahotannin dai,Hafsat ta bayyana cewa, itace a bidiyon kuma ita ta dauki kanta bidiyon amma ta ajiye a wayarta, bata san wanene ya turawa Duniya ba.
Tace ba ta turawa kowa Bidiyon ba.
Ma'aikacin Asibiti a Zaria ta jihar Kaduna, Musa A Bello da ya ajiye aikinsa saboda tsammanin Hamster Kombat zasu bashi kudi da yawa yayi Allah ya isa.
Ya bayyana hakane a shafinsa na sada zumunta inda yace wanda ya bashi shawarar yin Hamster Kombat yace masa da haka Bitcoin ya fara.
Yace abin takaici ne abinda hamsters Kombat suka bashi wanda bai taka kara ya karyaba inda ya ajiye aikinsa na shekara da shekaru saboda tsammanin zaau bashi kudi masu yawa.
Ya kara da cewa yanzu ta ina zai fara, daga barazanar da ake masa a wajan aiki ko da dariyar da jama'a ke masa?
Yace rayuwarsa a yanzu ta shiga halin rashin tabbas amma yace in Allah ya yarda zai sake samun wani aikin.
https://twitter.com/pharm_musa/status/1837710459480199366?t=kxuLRfll1IXCLsPQWbEaug&s=19
Yace ba za...
SO GAMÒN JINI: Nayi Alƙawarín Aúren Hafsat 'Yar TikTok, Idan Har Ta Amíɲce, A Cewar Matashi Prince Bilal Basheer.
"Ni dan asalin jahar Zamfara ne, na kuma shirya tsaf tare da tsarkake niya, dòmiɲ mu rufawa juna asiri akan auran Hafsat, tare da biyan sadaki kamar yadda addinin musuluɲci ya tanada, inji matashin kamar yadda ya bayyana a shafinshi na Facebook.
Wace shawara zaku bashi?