Friday, December 5
Shadow
Ban taba ganin Mutum Irin Shehu ba, Gaba daya gidajensa baya sa Haya, Kyauta yake ba mutane su zauna>>Inji Matar Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Ban taba ganin Mutum Irin Shehu ba, Gaba daya gidajensa baya sa Haya, Kyauta yake ba mutane su zauna>>Inji Matar Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Duk Labarai
Matar Marigayi Sheikh Dahiru Usman Bauchi, A'isha ta bayyana cewa, bata taba ganin mutum irinsa ba. Tace gidajensa baya badasu hay, Kyauta yake baiwa mutane su zauna. Ta bayyana hakane a wata hira da aka yi da ita inda take bayyana halaye na gari na Sheikh Dahiru Usman Bauchi. https://www.tiktok.com/@gtahausa/video/7578241269458128159?_t=ZS-91uf16fd7lw&_r=1
An zakulo Tsohon Bidiyon karamin Ministan, Bello Matawalle inda yake cewa ba duka Fulanine Tshàgyèràn Dhàjì ba

An zakulo Tsohon Bidiyon karamin Ministan, Bello Matawalle inda yake cewa ba duka Fulanine Tshàgyèràn Dhàjì ba

Duk Labarai
An zakulo Wani tsohon Bidiyon karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle inda yake cewa ba duka Fulanine 'yan Bindiga ba. Bidiyon dai an daukeshi ne tun lokacin yana gwamnan jihar Zamfara inda aka ji yana cewa 'yan sa kai suna matsawa Fulani. Yace har sai da ta kai ga ya Haramta ayyukan 'yan sa kai a jiharsa. https://twitter.com/instablog9ja/status/1995746969810059281?t=Nyi9H6GXWC76IMtPSAQhnA&s=19
Shekaru na basu kai ba, Na yi kankanta sosai ace an bani Mukamin Jakada>>Inji Sanata Shehu Sani

Shekaru na basu kai ba, Na yi kankanta sosai ace an bani Mukamin Jakada>>Inji Sanata Shehu Sani

Duk Labarai
Sanata Shehu Sani daga jihar Kaduna ya bayyana cewa shekarun sa ba su kai ba, yayi kankanta sosai ace an nadashi jadakan Najeriya zuwa wata kasa. Ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi inda aka tambayeshi game da rahotan dake cewa shugaba Tinubu ya bayar da sunansa cikin wanda zai baiwa mukamin Jakadanci. Sanata Shehu Sani yace har yanzu yana da ayyukan da zai wa Al'ummarsa a Kaduna Tukuna. https://twitter.com/Imranmuhdz/status/1996140553721778596?t=530oT-R8RwGP4W8f5Eq1eg&s=19
Kalli Bidiyon: An kama Mahaifinta saboda ya sayi sabon layi, Ashe layin Tshàgyèràn Dhàjì sun taba Amfani dashi shine

Kalli Bidiyon: An kama Mahaifinta saboda ya sayi sabon layi, Ashe layin Tshàgyèràn Dhàjì sun taba Amfani dashi shine

Duk Labarai
Wannan matashiyar ta koka da cewa an kama mahaifinta saboda ya sayi sabon layi yana amfani dashi. Tace layin ashe tsageran daji sun taba amfani dashi. Tace sun yi kokarin ganin mahaifinta amma abi ya ci tura. Ta bayyana cewa su taimaka su saki mahaifinta dan bashi da isashshiyar Lafiya. https://twitter.com/Mazi_Chinonso1/status/1996113550356488590?t=3uhHuUcSafhmjI7uHvMJSA&s=19
Kalli Bidiyon: Yanzu ke Rashida Mai Sa’a da kika kawo Makullin Kulle Zarmalulun mazajen aure, Ya kike so wadanda basu da aure irina su yi>>Inji Wannan matashiyar

Kalli Bidiyon: Yanzu ke Rashida Mai Sa’a da kika kawo Makullin Kulle Zarmalulun mazajen aure, Ya kike so wadanda basu da aure irina su yi>>Inji Wannan matashiyar

Duk Labarai
Wata mata ta kalubalanci Rashida Mai Sa'a bayan da ta kawo wani makulli da tace na matan aurene da mazansu ke bin mata. Rashida dai tace idan aka kulle makullin yana hana zarmalulun namiji tashi har sai an bude maullin. Saidai wannan matashiyar ta koka da cewa rashida Mai Sa'a bata kyauta musu ba dan kuwa ya take son irin su da basu da aure su yi kenan? https://www.tiktok.com/@rabiharuna888/video/7579335476805455111?_t=ZS-91uVHJ94MaX&_r=1
Ban cewa Sheikh Dahiru Bauchi dan Whùtà ba sannan ban ce mai Kàfìrì ba>>Inji Baffa Hotoro, kwana daya bayan da aka makashi Kotu

Ban cewa Sheikh Dahiru Bauchi dan Whùtà ba sannan ban ce mai Kàfìrì ba>>Inji Baffa Hotoro, kwana daya bayan da aka makashi Kotu

Duk Labarai
A jiya ne dai hutudole ya kawo muku Rahoton cewa, wani masoyin marigayi Sheikh Dahiru Usman Bauchi ya maka Baffa Hotoro a kotu saboda kalaman da yayi kan malamin. Mutumin dai a baya ya baiwa Baffa Hotoro kwanaki ya janye kalamansa akan malam sannan ya bayar da hakuri ko kuma ya kaishi kotu. Saidai Baffa Hotoro bai janye kalaman nasa ba sannan bai bayar da hakurin ba, dalilin hakane yasa mutumin ya maka Baffa Hotoro a kotu. Saidai kwana daya bayan faruwar hakan, an ga wani Bidiyo na Baffa Hotoro yana cewa shi bai ce Dahiru Bauchi dan Wuta bane sannan bai kirashi da Kafuri ba. Yace kawai dai ya bayyanashi a matsayin jahili wanda ya karantar da a bi Inyasi maimakon Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam). https://www.tiktok.com/@masoyinsheikhbaffahotoro/video/7579408940627250443?_t...
Kalli Bidiyon Da Duminsa: Ashe har yanzu magana na nan,Maiwushirya ya jadawa ‘YarGuda Lefe

Kalli Bidiyon Da Duminsa: Ashe har yanzu magana na nan,Maiwushirya ya jadawa ‘YarGuda Lefe

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, Idris Maiwushirya ya hadawa mutuniyarsa, 'YarGuda Lefe. Ya bayyana hakane a shafinsa na sada zumunta inda aka ga Akwatunan Lefen da kayan da ya siya yana nunawa. Saidai ba'a sani ba ko da gaskene ko kuwa Barkwancin da suka saba yine dan a baya an yi yukurin daura musu aure amma abin bai yiyu ba. https://www.tiktok.com/@maiwushiryabackup/video/7579552059435879701?_t=ZS-91uSx7k8To0&_r=1
Kalli Bidiyon yanda sojan Najeriya yayi bayanin Abashi da Alawus da suke dauka dalla-dalla

Kalli Bidiyon yanda sojan Najeriya yayi bayanin Abashi da Alawus da suke dauka dalla-dalla

Duk Labarai
Wani sojan Najeriya yayi bayanin Albasinda akw biyansu dalla-dalla tun daga fara aiki har ka gama. Saidai yayi maganane akan kurtu inda yace yayi wannan bayanine musamman ga wadanda ke son shiga aikin na soja. Yace albashin farko idan aka daukeka aiki Naira 104,000 ne. Daga nan ne idan ka shekara 5 aka kara maka matsayi, zaka samu karin Albashin zuwa Naira 112,000. Yace idan mutum yayi shekaru 10 za'a kara masa albashi zuwa Naira 115,000. Yace idan ka shekara 15 za'a kara maka albashi zuwa Naira 125,000. Yace idan ka shekara 20, za'a kara maka albashi zuwa Naira 150,000. Yace amma akwai alawus na Naira dubu 20 duk wata da ake biyansu. https://twitter.com/Teeniiola/status/1996090687670903014?t=hFwHR8pD9yrEWgZptQAyTw&s=19
Wani ya koka da cewa a lokacin Christopher Musa na shugaban sojojin Najeriya, sau 3 ana Jèfà Bàmà-Bàmàì akan Musulmai wanda basu ji ba basu gani ba da sunan kuskure

Wani ya koka da cewa a lokacin Christopher Musa na shugaban sojojin Najeriya, sau 3 ana Jèfà Bàmà-Bàmàì akan Musulmai wanda basu ji ba basu gani ba da sunan kuskure

Duk Labarai
Wani bawan Allah ya koka dacewa a lokacin Janar Christopher Musa na shugaban sojojin Najeriya, sau 3 ana jefawa musulman da basu ji ba basu gani ba bama-bamai da sunan Kuskure. Ya ce an jefawa masu Maulidi Bam a Tudun Biri ranar 3 ga watan Disamba 2023 inda mutane 126 suka rasa rayukansu. Hakanan yace akwai wani kauye a Sokoto da shima aka jefawa bama-bamai mutane 10 suka rasa rayukansi. Sannan yace ranar 13 ga Janairun 2025 ma an jefawa mutane bama-bamai a Zurmi jihar Zamfara inda mutane 16 suka rasa rayukansu. Yace saidai tun bayan sauke Janar Christopher Musa ba'a sake samun irin wannan matsalar ba. Yace nadashi Minista rashin girmama Musulmai ne kuma ya sa musulmai da yawa sun kadu, inda yayi fatan Sanatoci Musulmai ba zasu amince dashi ba a matsayin sabon ministan tsa...