Wednesday, April 29
Shadow
Sumar da yaran da muka kama suka yi a kotu duk karyace kawai dan su ja hankalin mutanene>>Inji Shugaban ‘yansandan Najeriya

Sumar da yaran da muka kama suka yi a kotu duk karyace kawai dan su ja hankalin mutanene>>Inji Shugaban ‘yansandan Najeriya

Duk Labarai
Shugaban 'yansandan Najeriya, IGP Kayode Egbetokun ya bayyana cewa, sumar da matasa 6 suka yi a kotu karyace kawai dan su jawo hankalin mutanene. Saidai yace duk da haka an baiwa matasan taimakon gaggawa wanda hakan ke nuna kokarin 'yansanda wajan ganin sun baiwa wanda suke tsare dasu kulawa. Yace kuma maganar shekarun yaran idan dai mutum ya kai shekarar aikata laifi karancin shekarunsa basa hana a hukuntashi kuma haka dokar take koda a kasar Ingila ne. Yace wasu daga cikin laifukan da ake zargin yaran da aikatawa sun hada da lalata dukiyar 'yan kasa da kuma barazana ga tsaron kasa. Ya kara da kira ga mutane da kada su nuna goyon bayan wani bangare kuma hukumar 'yansanda zata tabbatar ta bayyana duk abinda ke faruwa ba tare da boye komai ba. Sanan ya bayar da tabbacin cewa ...
Hotuna: Matar aure ta càkàwà mijinta wuka ya mùtù bayan da gardama ta barke tsakaninsu

Hotuna: Matar aure ta càkàwà mijinta wuka ya mùtù bayan da gardama ta barke tsakaninsu

Duk Labarai
Wata matar aure me suna Comfort Olajumoke Olalere Tinubu ta kashe mijinta ta hanyar caka masa wuka ya mutu bayan da gaddama ta barke a tsakaninsu. Lamarin ya farune a Gbeyi dake yankin Adegbayi a Ibadan jihar Oyo da misalin karfe 10 na daren Laraba, 30 ga watan October 2024. Shekaru 3 kenan da aurensu kuma suna da yara 2. TheNation ta ruwaito cewa matar me shekaru 33 ta kulle mijinta, Olusegun a dakinsu bayan da suka yi fada wanda daga baya abin ya kazance da ya kai ga har ta caka masa wuka ya mutu. Zuwa yanzu dai 'yansanda na bincike akan lamarin.
Kalli Bidiyo: Yanda matar aure ta jewa mijinta tsìràrà bayan sun yi fada dan dai kawai ta shawo kansa

Kalli Bidiyo: Yanda matar aure ta jewa mijinta tsìràrà bayan sun yi fada dan dai kawai ta shawo kansa

Duk Labarai
{"remix_data":[],"source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Wata matar aure ta dauki hankula a kafafen sada zumunta bayan da ta jewa mijinta tsirara, Tumbur bayan sun yi fada dan ta shawo kansa. An ga Bidiyon yanda matar ke daukar kanta da kuma abinda mijin yayi bayan ya ganta. https://twitter.com/Postsubman/status/1852590947869024357?t=xNDKNAB5f75CCZ_eyuBSxQ&s=19 Saidai matsalar da yarbanci suke magana.
Babu kananan yara a cikin wadanda muka kai kotu, duk manyan mutanene wasunsu ma suna da aure>>Gwamnatin Tarayya

Babu kananan yara a cikin wadanda muka kai kotu, duk manyan mutanene wasunsu ma suna da aure>>Gwamnatin Tarayya

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta bayyana cewa babu kananan yara a cikin wadanda ta gabatar a kotu da take zargi da cin amanar kasa ta hanyar kifar da gwamnatin shugaban kasa,Bola Ahmad. Lauyan Gwanatin, Rimazonte Ezekiel ne ya bayyana haka a ganawarsa da manema labarai. Ya kara da cewa, laifin su shine suna kiran sojoji su kwace mulki da daga tutar kasashen waje da kuma tayar da hankula. https://twitter.com/channelstv/status/1852450588178460769?t=9Ads0XRv52vEALHwdLs_Mg&s=19 Saidai da yawa sun kalubalanceshi da cewa maganar tasa ba gaskiya bane musamman tunda gashi mutane na gani yara ne suka gabatar. A baya dai hutudole ya kawo muku yanda kakakin 'yansandan Najeriya ya kare kama yaran inda yace doka tace ko da shekaru 7 za'a iya kaishi kotu. Ya kara da cewa kuma cikin yaran da...
Za’a gyara titunan zuwa dakin dafa abinci na shugaban kasa Tinubu, da wanda jiragen samansa ke bi da wanda ake bi dan kai masa ziyara akan Naira Biliyan 9.8

Za’a gyara titunan zuwa dakin dafa abinci na shugaban kasa Tinubu, da wanda jiragen samansa ke bi da wanda ake bi dan kai masa ziyara akan Naira Biliyan 9.8

Duk Labarai
A yayin da 'yan kasa ke fama da abincin da zasu ci da kyar, Gwamnatin tarayya ta bayar da gyaran titunan da jirgin saman shugaba kasa, Bola Ahmad Tinubu ke bi akan Naira Biliyan 9.8. Hakanan za'a gyara Titunan zuwa dakin dafa abinci na shugaban kasar da titunan da ake bi dan kai masa ziyara. Sakataren hukumar ci gaban babban birnin tarayya Abuja, Shehu Ahmad ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar. Yace an baiwa kamfanin Julius Berger Plc aikin kuma an basu nan da watanni 6 su kammalashi. Yace idan aka lura za'a ga cewa titunan tabbas suna bukatar gyara. Saida kungiyoyin kare hakkin bil'adama sun yi Allah wadai da wannan aiki inda sukace kamata yayi a bayar da wadannan kudade wajan inganta rayuwar talakawa.
Hotuna Gwanin ban Tausai na wata likita bayan masu Gàrkùwà da mutane sun sakota

Hotuna Gwanin ban Tausai na wata likita bayan masu Gàrkùwà da mutane sun sakota

Duk Labarai
Wata likita me suna Dr. Ganiyat Popoola da dan uwanta sun shafe watanni 10 a hannun masu garkuwa da mutane a Kaduna amma yanzu ta samu kubuta. Hotunansu da aka gani bayan sakosu daga hannun masu garkuwa da mutanen musamman idan aka yi la'akari da hotunansu na kamin a kamasu ya baiwa mutane mamaki da tausai sosai. Matar dai tana aiki ne a asibitin ido na National eye Center dake Kaduna kuma tun ranar 27 ga watan Disamba na shekarar 2023 aka yi garkuwa da ita da mijinta, Nurudeen Popoola, da kuma dan uwanta, Folaranmi Abdul-Mugniy. Bayan tattaunawa da wadanda suka yi garkuwa da su, sun sako mijin amma suka ci gaba da rike matar, da dan uwanta, Abdul-Mugniy. Ranar 30 ga watan October ne dai shugaban kungiyar likitoci ta Resident Doctors, Tope Osundara ya tabbatar da kubutar matar....
Bayan shan suka daga ciki da wajen Najeriya, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayar da umarnin a sake duba tuhumar cin amanar kasa da akewa kananan yara da aka kai Kotu

Bayan shan suka daga ciki da wajen Najeriya, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayar da umarnin a sake duba tuhumar cin amanar kasa da akewa kananan yara da aka kai Kotu

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayar da umarnin a sake duba tuhumar cin amanar kasa da akewa kananan yara da aka kai kotu na yunkurin kifar da gwamnatin sa ta hanyar zanga-zanga. Shugaban yace babban lauyan Gwamnati ya duba lamarin dan bayar da shawara kan abinda ya kamata a yiwa yaran. Yara kanana guda 32 ne dai aka gabatar a babbar kotun tarayya dake Abuja bisa zargin cin amanar kasa saboda sun yi zanga-zangar yunwa. Yaran dai an gansu cikin yunwa da rashin lafiya da firgici inda wasu daga cikinsu suka rika faduwa a farfajiyar kotun. Tuni dai aka garzaya da guda 5 asibiti. Hakanan an ga bidiyon yanda yaran ke rububin biskit da ruwa da aka basu dan su ci a cikin kotun. Lamarin ya jawo Allah wadai ga gwamnati a ciki da wajen Najeriya.
Hukumar ‘yansandan Najeriya tace indai mutum ya kai shekaru sama da 7 za’a iya kaishi kotu, kuma wadannan yara karamin cikinsu shine me shekaru 13

Hukumar ‘yansandan Najeriya tace indai mutum ya kai shekaru sama da 7 za’a iya kaishi kotu, kuma wadannan yara karamin cikinsu shine me shekaru 13

Duk Labarai
{"remix_data":[],"source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{"square_fit":1},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":true,"containsFTESticker":false} Kakakin hukumar 'yansandan Najeriya ya kare sukar da akewa gwamnati kan gurfanar da kananan yara a kotu bisa zargin kifar da gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta hanyar zanga-zanga. A wata hira da gidan Talabijin na Channels TV suka yi dashi, Olumuyiwa Adejobi ya bayyana cewa, basu kai kananan yara kotu ba. Yace doka tace idan dai yaro ya wuce shekaru 7 za'a iya gurfanar dashi a kotu. Yace kuma duka cikin yaran mafi karancin shekaru sune wanda ke da shekaru 13. https://twitter.com/K...
Kalli Bidiyon yanda kananan yaran da Gwamnatin Tinubu ta kama saboda sun yi zanga-zangar yunwa ta barsu da yunwa suke rububin biskit a cikin kotu

Kalli Bidiyon yanda kananan yaran da Gwamnatin Tinubu ta kama saboda sun yi zanga-zangar yunwa ta barsu da yunwa suke rububin biskit a cikin kotu

Duk Labarai
{"remix_data":[],"source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Kananan yara 32 ne dai gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta gabatar a gaban babbar kotun tarayya dake Abuja bisa zargin yunkurin kifar da gwamnatinsa ta hanyar yi masa zanga-zanga. Yaran dai an gansu cikin dauda da yunwa da rashin lafiya wanda hakan ya jawowa gwamnatin Tinubun Allah wadai. A wasu bidiyon an ga yaran suna kuka. https://twitter.com/jharmo/status/1852282458693157335?t=-Tx5rXM6o8t-J60gkbtMzA&s=19 Inda a wasu kuma aka gansu suna warwar biskit saboda tsananin yunwa.
T-Pain dai ko yara basu tsira daga ukubar gwamnatinsa ba>>Atiku ya soki Tinubu kan Azabtar da kananan yara saboda sun masa zàngà-zàngà

T-Pain dai ko yara basu tsira daga ukubar gwamnatinsa ba>>Atiku ya soki Tinubu kan Azabtar da kananan yara saboda sun masa zàngà-zàngà

Duk Labarai
{"remix_data":[],"source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar shugaban kasa a jami'iyyar PDP a shekarar 2023, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana Allah wadai da takaici kan yanda gwamnatin shugaban kasa,Bola Ahmad Tinubu ta gurfanar da kananan yara wanda ke fama da yunwa da rashin lafiya a kotu bisa zargin cewa sun yi yunkurin kifar da gwamnatin tarayya ta hanyar yin Zanga-zanga. Hutudole ya ruwaito muku cewa 5 daga cikin yaran dai sun fadi a farfajiyar kotun inda aka garzaya dasu Asibiti. Atiku a sanarwar da ya fitar da yammac...