Friday, January 23
Shadow
Kalli Bidiyon: Gwamnan jihar Kebbi tare da soja me guntulen Hannu da ya jawo cece-kuce sosai

Kalli Bidiyon: Gwamnan jihar Kebbi tare da soja me guntulen Hannu da ya jawo cece-kuce sosai

Duk Labarai
A ranar Tunawa da 'yan mazan jiya, Gwamnan jihar Kebbi, Nasiru Idris ya hadu da wani soja da ya rasa hannunsa a wajan aiki. An gabatar da sojan a wajan gwamnan, inda gwamnan yace a yiwa sojan hannun Roba, inda yace a masa me kyau, har yana tambaya duka nawa yake? https://twitter.com/i/status/2012100209048977895 Saidai wannan lamari ya jawo cece-kuce inda masu sharhi suka zargi gwamnan da rashin nuna tausai ga sojan musamman ganin cewa ya rasa hannun nasa ne wajan yiwa kasa Hidima. Masu Sharhin na ganin cewa ba maganar kudi kawai bace, ya kamata gwamnan ya nuna alhini da halin da sojan ke ciki.
Kalli Hotuna:Dan gidan Ministan Ayyuka, Osborn Umahi ya fito takarar kujerar shugaban karamar hukuma

Kalli Hotuna:Dan gidan Ministan Ayyuka, Osborn Umahi ya fito takarar kujerar shugaban karamar hukuma

Duk Labarai
Dan gidan Ministan ayyuka, Osborn Umahi ya fito takarar neman kujerar shugaban karamar hukumar. Ya fito ne neman takarar kujerar Karamar hukumar Ohaozara ta jihar Ebonyi. Magoya bayansa ne suka rakashi Ofishin APC inda ya sayi fom din takarar akan Naira Miliyan 30. Dama dai a baya yawa mahaifinsa shugaban yakin neman zabe sannan kuma gwamnan jihar Ebonyi na yanzu, Francis Nwifuru ya bayyana shi a matsayin dan takararsa
Wanda suka tsayawa Malami aka bayar da belinsa na son su janye

Wanda suka tsayawa Malami aka bayar da belinsa na son su janye

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, wadanda suka tsayawa Tsohon Ministan shari'a, Abubakar Malami aka bayar da belinsa na son janyewa. Hakan yasa lauyoyin Malamin suka je a yau, Juma'a sika samu babban Alkalin kotun tarayya suka nemi ya taimaka a saki Malami daga gidan yarin Kuje. Saidai Sahara Reporters data ruwaito lamarin tace, An yi bayanin ne a sirri ba'a san ba'a bari kowa yasan abinda aka tattauna ba.
Ashe shugaba Tinubu ya halarci Daurin auren dan Atiku da ya koma APC

Ashe shugaba Tinubu ya halarci Daurin auren dan Atiku da ya koma APC

Duk Labarai
Bayan da dan Atiku Abubakar, me suna Abba Atiku Abubakar ya koma jam'iyyar APC. Lamarin ya dauki hankula sosai. Inda har sai da Atikun ya fito yace ra'ayin dansa ne ya koka jam'iyyar APC kuma ba zai tursasa masa ra'ayin siyasa ba. Saidai Rahotanni sun bayyana cewa, a baya, Shugaba Tinubu kamin ya zama shugaban kasa, ya halarci daurin auren dan Atikun da aka yi a Dubai.
Har Yanzu Beli Kyautane: Duk dansandan da yace ku bashi kudin beli ku kawo mana korafi>>Inji Hukumar ‘Yansanda

Har Yanzu Beli Kyautane: Duk dansandan da yace ku bashi kudin beli ku kawo mana korafi>>Inji Hukumar ‘Yansanda

Duk Labarai
Hukumar 'yansandan Najeriya reshen Abuja sun bayyana cewa, Har yanzu Beli Kyautane. Hukumar tace duk dansandan daya Bukaci sai an bashi kudi kamin a bayar da beli a kai musu karansa. Hakan ya fito ne daga bakin me magana da yawun hukumar,SP Josephine Adeh. Ta bayyana hakane yayin da ake ta korafi akan wasu 'yansanda da suka ki bayar da beli suka ce sai an biya kudi.
Kasar Amurka ta ware kudi har N587 billion ($413.046m) dan magance matsalar tsaro a Najeriya

Kasar Amurka ta ware kudi har N587 billion ($413.046m) dan magance matsalar tsaro a Najeriya

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Kasar Amurka ta ware kudi har Naira N587 billion ($413.046m) dan magance matsalar tsaro a Najeriya da sauran wasu kasashen Afrika. Hakan na kunshene a cikin kasafin kudin shekarar 2026. Hakan na zuwane bayan da Amurkar ta kai hari a jihar Sokoto. Hakanan kuma a baya, kasar Amurka ta kawowa sojojin Najeriya tallafin kayan aiki.