Thursday, March 26
Shadow
Kalli Bidiyon: Wani ya je Saudiyya inda ya yiwa Tauraruwar Tiktok, Babiana Addu’ar Allah ya bata nasara akan Sadiya Haruna

Kalli Bidiyon: Wani ya je Saudiyya inda ya yiwa Tauraruwar Tiktok, Babiana Addu’ar Allah ya bata nasara akan Sadiya Haruna

Duk Labarai
Wannan Bidiyon wani bawan Allah ne masoyin Tauraruwar Tiktok, Babiana inda ya mata addu'a a dakin Ka'aba Allah ya bata nasara akan Sadiya Haruna. https://www.tiktok.com/@amanar.gov.abbakabiryusu/video/7618880019942755604?_r=1&_t=ZS-94ojsC0fvjE&sp_source=7537614245375297080 A baya dai, Itama Sadiya Haruna ta je dakin ka'ba inda tace ta kai karan Babiana gaban Allah ya bi mata hakkinta.
Kalli Bidiyon: Bayan da Sheikh Dr. Ahmad Gumi yace aje Idi kuma aje Sallar Juma’a, tsohon Bidiyon Dr. Idris Dutsen Tanshi ya bayyana inda shi kuma yace idan mutum yayi Idi ba lallai sai yayi Juma’a ko Azahar ba

Kalli Bidiyon: Bayan da Sheikh Dr. Ahmad Gumi yace aje Idi kuma aje Sallar Juma’a, tsohon Bidiyon Dr. Idris Dutsen Tanshi ya bayyana inda shi kuma yace idan mutum yayi Idi ba lallai sai yayi Juma’a ko Azahar ba

Duk Labarai
Cece-kuce ya barke a kafafen sada zumunta bayan da Malamin Addinin Islama, Sheikh Dr. Ahmad Gumi yace aje Idi kuma aje Sallar Juma'a. Malam yace idan ya zamana mutum daya zai je to ya je Juma'a ya bar Idi. https://www.tiktok.com/@izzalatul.bidia/video/7618693269660175636?_r=1&_t=ZS-94oRqB9nibp&sp_source=7537614245375297080 Saidai bayan bayyanar wannan jawabi nasa, An rika yada tsohon Bidiyon Marigayi, Dr. Idris Dutsen Tanshi inda ya bayar da fatawar cewa idan mutum yayi Idi, ba lallai yayi Juma'a ko Azahar ba. https://www.tiktok.com/@e.snig.ltd_tiga_01/video/7618735768973905173?_r=1&_t=ZS-94oSL7l8TdQ&sp_source=7537614245375297080
Kalli Bidiyon: Ganin Me baiwa shugaba Tinubu shawara a kan harkar tsaro, Malam Nuhu Ribadu da Minista Hannatu Musa Musawa akan keken Doki suna Annashuwa a kasar Ingila ya dauki hankula

Kalli Bidiyon: Ganin Me baiwa shugaba Tinubu shawara a kan harkar tsaro, Malam Nuhu Ribadu da Minista Hannatu Musa Musawa akan keken Doki suna Annashuwa a kasar Ingila ya dauki hankula

Duk Labarai
An hangi me baiwa shugaban kasa shawara akan harkar tsaro, Malam Nuhu Ribadu tare da minista, Hannatu Musa Musawa akan keken Doki a kasar Ingila suna annashuwa. Suna cikin tawagar shugaban kasa, Bola Ahmad da ta je kasar Ingila inda yake ziyarar aiki. Wasu dai sun ce hakan bai dace ba lura da yanda Najeriya ke fama da matsalar tsaro. https://www.tiktok.com/@arewacontinental/video/7618748690005511444?_r=1&_t=ZS-94oQdn8BA0H&sp_source=7537614245375297080
Kalli Bidiyon: Abinda Sarkin Ingila ya gayawa shugaba Tinubu da ya dauki hankula sosai

Kalli Bidiyon: Abinda Sarkin Ingila ya gayawa shugaba Tinubu da ya dauki hankula sosai

Duk Labarai
Sarkin Ingila, King Charles ya gayawa shugaba Tinubu, Naija No dey carry last. Lamarin ya dauki hankula sosai inda akai ta tafi. Wannan turancin 'yan Najeriya ne dake nufin ba'a barin Najeriya a baya. Sarki Charles ya bayyana hakane a karshen jawabin da yayi a wajan taron cin abinci na girmamawa da aka shiryawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a Ingila. https://twitter.com/i/status/2034390502196285860 Shugaba Tinubu dai na ziyarar aiki a Ingila irin ta ta farko da wani shugaban Najeriya yayi a cikin shekaru 37 da suka gabata. Ana sa ran wannan ziyarar aiki zata jawo hankalin Ingila ta zuba jari a Najeriya.
Kalli Bidiyon: Dan Najeriya da ya je Kasar Jamhuriyar Nijar yace Nijar din zai bi yayi Sallah Gobe, ba zai cika Azumi 30 ba

Kalli Bidiyon: Dan Najeriya da ya je Kasar Jamhuriyar Nijar yace Nijar din zai bi yayi Sallah Gobe, ba zai cika Azumi 30 ba

Duk Labarai
Dan Najeriya, Faruk da ya je Nijar yace a kasar ta Nijar an ga watan Shawwal na sallah dan haka gobe za'a yi sallah. Yace shima gobe zai ajiye Azuminsa yayi Sallah ba zai cika Azumi 30 ba kamar yanda za'a yi a Najeriya ba. https://www.tiktok.com/@faruq_abuja_back_up/video/7618709603345288468?_r=1&_t=ZS-94nsQ1H1uz3&sp_source=7537614245375297080
An kama sojan Najeriya da fashi da makami

An kama sojan Najeriya da fashi da makami

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Abia na cewa an kama sojan Najeriya me suna Lance Corporal Chukwu Ebuka da zargin fashi da makami. Sojan yawa wani mutum da ba'a tantance kowanene ba fashin Naira Miliyan 4.9 Sojan yace yana aiki ne da bataliyar 14 Brigade dake Ohafia a jihar Abia. A Bidiyon sojan da ya watsu a kafafen sada zumunta an ji wani babban soja na masa tambayoyi. Sojan dai ya amsa duka laifukan da ake zarginsa da aikatawa a Bidiyon. https://twitter.com/i/status/2034319639384138193
Kalli Bidiyon: Duk wanda baya gamsar da matarsa, akwai yiyuwar zata bi maza>>Inji Alkarmawi

Kalli Bidiyon: Duk wanda baya gamsar da matarsa, akwai yiyuwar zata bi maza>>Inji Alkarmawi

Duk Labarai
Malam Alkarmawi na Kano ya bayyana cewa, yana da muhimmanci magidanci ya rika gamsar da matarsa. Yace idan ya zamana magidanci baya iya gamsar da matarsa, a irin hakane a ke samun matan aure na bibiyar maza. https://www.tiktok.com/@binkabeer35/video/7618292854976269589?_r=1&_t=ZS-94nIA3BWkEL&sp_source=7537614245375297080 Yace suma mata masu kin yiwa mazansu biyayya, su ji tsoron Allah.