Thursday, April 16
Shadow
Kalli Bidiyon: Gwamna Abba na fada kan bututun ruwa da ba’a gyara ba ya dauki hankula

Kalli Bidiyon: Gwamna Abba na fada kan bututun ruwa da ba’a gyara ba ya dauki hankula

Duk Labarai
An ga wani Bidiyon gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf na ta yawo a kafafen sada zumunta inda Gwamnan ke fada game da wani Bututun ruwan Fanfo da ya lalace. Bidiyon dai ya jawo cece-kuce inda akaita bayyana mabanbanta ra'ayoyi akai. https://www.tiktok.com/@sardauna_shoot.ng/video/7626153902773226760?_r=1&_t=ZS-95MVdZgatSC&sp_source=7537614245375297080
Kalli Bidiyon: Dalilin da yasa naki yin wakar siyasa shine ban son in Zhaghi Kwankwaso in yabi Abba>>Ali Jita

Kalli Bidiyon: Dalilin da yasa naki yin wakar siyasa shine ban son in Zhaghi Kwankwaso in yabi Abba>>Ali Jita

Duk Labarai
Tauraron mawakin Hausa, Ali Isa Jita ya bayyana cewa, dalilin da yasa baya son yin wakar siyasa shine bai son sai ya soki Dr. Rabiu Musa Kwankwaso sanna ya yabi Gwamna Abba Kabir Yusuf. Yace Ko makaho ya shigo Kano yanzu yasan Kokarin Abba yafi na sauran gwamnonin da suka gabata. https://www.tiktok.com/@speciall101/video/7626131048526662942?_r=1&_t=ZS-95MU5vWL6Qr&sp_source=7537614245375297080
Kai malam Shekaruna 46 ba 35 ba, kuma kai na dan Adawa ne na gaskiya ba, APC ce ta turoka ka mata Munafurci>>Nafiu Bala ya gayawa Kwankwaso

Kai malam Shekaruna 46 ba 35 ba, kuma kai na dan Adawa ne na gaskiya ba, APC ce ta turoka ka mata Munafurci>>Nafiu Bala ya gayawa Kwankwaso

Duk Labarai
Nafiu Bala Gombe wanda ya kawo tarnaki a jam'iyyar ADC ya mayarwa da Kwankwaso zazzafan Martani inda yace Kwankwason ba dan Adawa bane na gaskiya. Nafiu ya bayyana cewa, Kwankwaso APC ce ta turoshi ya mata munafurci a jam'iyyar ADC. Sannan yace Shi shekarun sa 46 ba 35 ba kamar yanda Kwankwason yake fada. Sannan yace ya kamata Kwankwason yayi bincike da kyau kamin yayi magana irin waccan. Sannan yace ko da kuwa shi yarone bai kamata Kwankwason ya rainashi ba. Ya kara da cewa, Su Kwankwaso sun tsufa, kamata yayi su koma gefe su bar matasa su mulki Najeriya, yace kamata yayi su zama masu bayar da shawara. Yace Kwankwason da sauran shuwagabannin da yawa suma a lokacinsu matasa suka fara shiga harkar siyasa. Yace a 2023 fa Dattawan Arewa sun je suka samu Kwankwaso akan ya ja...
A karshe dai: Ainahin dalilin da yasa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya koma jam’iyyar APC ya bayyana

A karshe dai: Ainahin dalilin da yasa Gwamna Abba Kabir Yusuf ya koma jam’iyyar APC ya bayyana

Duk Labarai
Rahotanni nata yawo a kafafen sada zumunta inda ake bayyana ainahin dalilin da yasa Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf ya koma jam'iyyar APC. Rahoton yace akwai rade-radin dake yawo cewa, Kwankwaso na shirin canja Abba a matsayin dan takarar gwamna na jam'iyyar NNPP. Dalili kenan da yasa Abban ya yi gaggawa ya koma jam'iyyar APC dan samun Tikitin takara. https://twitter.com/i/status/2041481567730622823
Kalli Bidiyon: Yanda sabon wajan tsayuwar Motoci na zamani da aka kashe Miliyoyin Naira wajan ginawa a Abuja ya lalace bayan ruwan sama

Kalli Bidiyon: Yanda sabon wajan tsayuwar Motoci na zamani da aka kashe Miliyoyin Naira wajan ginawa a Abuja ya lalace bayan ruwan sama

Duk Labarai
Wajan tsayuwar motocin haya na Kugbo dake Abuja da aka kashe Miliyoyin Naira aka gina ya lalace. Lamarin ya jawo cece-kuce inda da yawa ke cewa dama can ba da kayan aiki masu inganci aka yi aikin ba. https://twitter.com/i/status/2041542821111320647 https://twitter.com/i/status/2041541799856976308 https://twitter.com/i/status/2041539082598187009
Da Duminsa: Yayin da ake fama da Nafiu, Wani sabin tsagi ya bulla a jam’iyyar ADC inda suka ce suma sune shuwagabannin jam’iyyar

Da Duminsa: Yayin da ake fama da Nafiu, Wani sabin tsagi ya bulla a jam’iyyar ADC inda suka ce suma sune shuwagabannin jam’iyyar

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa yayin da ake fama da Nafiu Bala Gombe, wani tsagi na jam'iyyar ADC ya bayyana inda suke ikirarin cewa, sune shuwagabannin jam'iyyar na gaskiya. Tsagin wanda wani me suna Don Norman Obinna kejagoranta, sun bayyana hakane a ganawa da manema labarai da suka yi a Abuja ranar Talata. Sun ce tsohon shugaban jam'iyyar, Ralph Nwosu da ya mikawa su David Mark ragamar jam'iyyar, tun shekarar 2022 wa'adin mulkinsa ya kare, kuma dama akwai shari'a da ake yi dashi a kotu bama guda daya ba.
Da Duminsa: Kwankwaso ya fusata da abinda Nafiu Bala Gombe yakewa ADC ya bayyana matakin da zasu dauka akan Nafiu

Da Duminsa: Kwankwaso ya fusata da abinda Nafiu Bala Gombe yakewa ADC ya bayyana matakin da zasu dauka akan Nafiu

Duk Labarai
A yayin da Nafiu Bala Gombe yake baiwa su Atiku da Kwankwaso da Peter Obi ciwon kai a jam'iyyar APC, Kwankwaso yayi martani Kwankwaso yace yasa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu yana yin dukkan mai yiyuwa wajan ganin ya muzguna musu ya hanasu rawar gaban hantsi amma hakan ba zai sanyaya musu gwiwa ba. Kwankwaso yace hakan karfafa su zai yi kuma ba zasu bar jam'iyyar ADC ba