Tuesday, June 30
Shadow
Sojojin Najeriya sun kashe ƙasurgumin ɗan bindiga, Buharin Yadi a Kaduna

Sojojin Najeriya sun kashe ƙasurgumin ɗan bindiga, Buharin Yadi a Kaduna

Kaduna, Katsina
Sojojin Najeriya sun sun ce sun kashe wani ƙasurgumin ɗan bindiga da ya addabi wasu yankunan arewa maso yammacin ƙasar mai suna Kachalla Buhari Alhaji Halidu da aka fi sani da Buharin Yadi da wasu yaransa fiye da 30.. Cikin wata sanarwa kwamishin harkokin tsaron cikin gida, Samuel Aruwan, ya fitar ya ce lamarin ya faru ne sakamakon wani gagarumin farmaki da dakarun rundunar 'Sector 6 Operation Whirl Punch' suka kai a kan iyakar Kaduna da Katsina Ya ƙara da cewa Manjo Janar MLD Saraso ya jagoranci farmaki kan Yadi da mayaƙansa bayan samun rahotannin sirri da sojojin suka samu daga jihar Katsina. Sanarwar ta ce sojojin sun yi ba-ta-kashi da 'yan bindigar a kusa da dajin Idasu, inda suka kashe ‘yan bindiga aƙalla 36 ciki har da Kacahalla Buharin Yadi. Ƙasurgumin ɗan bindigar ya yi...
Goron Sallah: Gwamnan Sokoto ya bai wa ma’aikatan jihar naira 30,000

Goron Sallah: Gwamnan Sokoto ya bai wa ma’aikatan jihar naira 30,000

Sokoto
Gwamnan jihar Sokoto Ahmed Aliyu Sokoto, ya amince da bai wa ma'aikatan jihar naira 30,000 a matsayin goron sallah. Cikin wata sanarwa da kwamishinan muhalli na jihar, Nura Shehu ya aike wa BBC, ta gwamnan jihar ya amince da bai wa duka ma'aikatan jihar da ƙananan hukumomi da masu fansho goron sallar. Sanarwar ta ƙara da cewa su ma ma'aikatan wucin gadi masu karbar alawus-alawus za su amfana da goron sallar. ''Rukuni na farko ya haɗa da ma'aikatan Jiha, da na ƙananan hukumomi za su karɓi naira 30,000 a matsayin goron Sallah'', in ji sanarwar. Sanarwar ta kuma ce ''rukuni na biyu da ya ƙunshi masu karɓar fansho da masu karɓar alawus-alawus a ƙananan hukumomi da kuma masu karɓar alawus-alawus a hukumar kula da kiwon lafiya a matakin farko waɗanda za su karɓi naira 20, 000 a matsa...
Da Duminsa: ‘Yansanda sun haramta hawan Sallah a Kano

Da Duminsa: ‘Yansanda sun haramta hawan Sallah a Kano

Kano
Rundunar 'yan sandan Najeriya a jihar Kano ta haramta gudanar da bukukuwan hawan sallah da aka saba yi na al'ada a faɗin jihar. Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar 'yan sandan, Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, ta ce hakan na cikin shawarwarin tsaro da rundunar ta bai wa mazauna jihar gabanin bukukuwan babbar sallah da za a soma ranar Lahadi. Sanarwar ta ce rundunar za ta baza jami'anta a sassan jihar domin tabbatar da bin doka da oda a jihar, kafin sallah da lokacin bukukuwan bayan sallar. ''Haka kuma an haramta duka nau'ikan hawan sallah a lokacin bukukuwan babbar sallah da ke tafe'', in ji sanarwar. 'Yan sandan sun ce sun ɗauki matakin ne sakamakon rahotonnin tsaro da suka samu da kuma tuntuɓar masu ruwa da tsaki a harkar tsaro, domin tabbatar da zaman lafiyar al'ummar ji...

Wata nawa ake haihuwa

Gwajin Ciki
Sanin sanda zaki haihu abune me dadi. Ga bayanin masana ilimin kimiyyar lafiya kan lokacin haihuwa. Yayin da mutane mafi yawanci an fi sabawa da kirgen watanni idan aka zo maganar haihuwa, masana ilimin kimiyyar lafiya na amfani da kwanaki da makonnine. A cewar masana kiwon lafiya, cikakken daukar ciki har zuwa a haifeshi, makonni 40 ne, wanda yayi daidai da watanni 10. Nasan da yawa zasu sha mamaki da jin wannan bayani, to bari kuji abinda masana kimiyyar lafiya suka ce. Yawancin mata suna sanin suna da ciki ne bayan basu ga jinin al'adarsu ba, wanda a wannan lokacin kuma mace ta riga ta kai sati 4 da daukar cikin. To a wannan lokacin kuma saura sati 36 mace ta haihu, wanda shine yayi daidai da watanni 9, yanzu kun gane dalilin koh? Sanin ranar da zaki haihu, yawanci lik...

Yawan fitsari ga mai ciki

Gwajin Ciki
Yawan fitsari ga mace me ciki ba matsala bane, alamace ta daukar ciki saidai idan yayi yawa, yakan iya zama cuta. Yawan fitsari na faruwa ne ga mace me ciki saboda yanda jikinta yake canjawa saboda shigar ciki da kuma shirin haihuwa. Yawan fitsari na daga cikin alamun farko na daukar ciki. Yawanci yawan fitsari na farawane a mako na 10 zuwa 13 bayan mace ta dauki ciki. Yawanci mata masu ciki kan yi fitsari sau 6 zuwa 10 a rana. Saidai idan ya wuce haka, yana iya zama na ciwo. Kalan fisarin mace me ciki yakan kara duhu, daga ruwan dorawa, watau Yellow zuwa me ruwan dorawa sosai ko kuma Dark Yellow. Idan mace me ciki ta ji fitsari, yana da kyau, kada ta rikeshi, ta je ta yi, saboda rike fitsari yana da illa ga mace me ciki da danta.
Hukumar dake shirya gasar Euro wato (UEFA), ta bayyana wasu sabbabin dokoki guda uku da za a fara amfani da su a gasar ta bana wadda zata gudana a ƙasar Germany

Hukumar dake shirya gasar Euro wato (UEFA), ta bayyana wasu sabbabin dokoki guda uku da za a fara amfani da su a gasar ta bana wadda zata gudana a ƙasar Germany

Kwallon Kafa
Hukumar dake shirya gasar Euro wato (UEFA), ta bayyana wasu sabbabin dokoki guda uku da za a fara amfani da su a gasar ta bana wadda zata gudana a ƙasar Germany. Alƙalin wasa zai bayyana hukuncin da ya yanke kuma zaiyi bayanin hakan ga magoya baya ta hanyar sadarwar kunne kai tsaye (Headphones) Za a dinga bayar da bayanai kai tsaye zuwa ga masu sharhin wasa (Commentators) akan hukuncin alƙalin wasa bayan dawowar sa cikin fili daga ganin VAR domin a yiwa masu bibiyar wasan bayanin abun da ya faru kai tsaye. A kowacce ƙwallo za a saka na'ura wadda zata dinga fayyace wa alƙalin wasa satar gida da kuma batun taɓa ƙwallo da hannu a yadi na 18. Fagen Wasanni

Addu’a ga mai ciki: Addu’ar saukin haihuwa

Addu'a, Gwajin Ciki
Wannan addu'a da zamu baku anan manyan malamai sunce sadidan ce, an gwada akan mata dake nakuda kuma an yi nasara: Saidai kamin mu baku wannan addu'a, ga bayani kamar haka: A binciken masana malamai na sunnah sun ce babu wata addu'a da aka ware wadda aka ce mace me ciki zata rika yi. Malamai sunce akwai dai hadisan karya da ake dangantawa da Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi Wasallam) akan addu'a ga mai ciki. Misali Akwai hadisin da aka ce, A lokacin da fatima(A.S) ta zo haihuwa, Ma'aikin Allah Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi Wasallam) yasa Umm Salamah da Zaynab bint Jahsh su zo su karanta mata Ayatul Kursiyyu, da kuma al-A‘raaf 7:54, Yoonus 10:3, da kuma falaki da Nasi, Saidai wannan hadisin karyane, domin karin bayani ana iya duba al-Kalim at-Tayyib (p. 161) na Ibn Taymiy...
Iyalan Sheikh Ibrahim Nyass, sun yi kira ga Muhammadu Sanusi II yayi koyi da sawun Kakan sa Muhammad Sanusi l da aka cire ya hakura

Iyalan Sheikh Ibrahim Nyass, sun yi kira ga Muhammadu Sanusi II yayi koyi da sawun Kakan sa Muhammad Sanusi l da aka cire ya hakura

Kano
Shugaban Darikar Tijjaniyya Mahi Nyass ya shawarci Lamido Sanusi da ya yi koyi da kakansa ta hanyar kin amincewa da kujerar sarautar Sarkin Kano. Sarki Sanusi shi ne jagoran kungiyar Tijjaniyya a Najeriya. An mayar da shi a matsayin Sarkin Kano a karshen watan da ya gabata bayan da Gwamnatin Jihar ta yi wa dokar masarautu gyara inda ta rusa masarautu hudu daga cikin biyar da ke Jihar tare da tube Aminu Ado Bayero a matsayin Sarkin Kano. Mista Ado Bayero dai yana kalubalantar tsige shi ne a gaban kotu, kuma yanzu haka yana zaune a karamar fadar Sarkin bisa kin amincewa da umarnin Gwamnatin Jihar. Sai dai kungiyar ta Islama a wata takarda mai dauke da kwanan watan 3 ga watan Yuni mai dauke da sa hannun babban shugabanta Mista Nyass ta bukaci Sanusi da ya ki amincewa da mayar da shi ...
‘Yan Bindiga: Bani Da Ikon Tafiyar da Harkokin Tsaro A Zamfara – Gwamna Lawal

‘Yan Bindiga: Bani Da Ikon Tafiyar da Harkokin Tsaro A Zamfara – Gwamna Lawal

Jihar Zamfara, Tsaro
Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara ya koka kan yadda ya kasa sarrafa gine-ginen tsaro a jihar. Lawal ya ce ba shi da iko a kan shugabannin hukumomin tsaro a jihar, yana mai jaddada cewa suna karbar umarni daga manyansu. Da yake jawabi yayin wani taron birnin tarayya na bikin ranar dimokuradiyyar Najeriya karo na 25 a Abuja ranar Laraba, gwamnan ya yi tir da ayyukan ‘yan bindiga a jihar. A cewar Lawal: “Da sunan, ni ne babban jami’in tsaro na jihata amma idan ana maganar umarni da iko, ba ni da iko a kan duk wani jami’in tsaro na soja, ko ‘yan sanda ko na Civil Defence. “Suna karbar umarninsu daga manyansu ba daga gwamnoni ba. Ba mu da wannan iko, ina fata muna da, da ya kasance wani labari na daban. " Ya ce matsalar tsaro ba ta gyaru a jihar ba sakamakon katsalandan da ya b...
An Daure Wani Mutum A Gidan Yari Sakamakon Samun Sa Da Laifin Karbar Batirin Jirgin Kasa Na Sata

An Daure Wani Mutum A Gidan Yari Sakamakon Samun Sa Da Laifin Karbar Batirin Jirgin Kasa Na Sata

Duk Labarai
A ranar Alhamis ne wata kotun majistare da ke garin Kafanchan a jihar Kaduna, ta yanke wa wani matashi mai suna Chibuzo Emmanuel, dan shekara 40 da haihuwa, hukuncin daurin shekaru uku a gidan yari, bisa samunsa da laifin karbar baturan jirgin kasa da silinda na sata. Hukumar NSCDC, ta gurfanar da Emmanuel tare da Adamu Danbaba mai shekaru 52 da laifin sata da kuma karbar dukiyar sata. Jami'i mai shigar da kara na NSCDC, Mista Marcus Audu, ya shaida wa kotun cewa hukumar kula da layin dogo ta Najeriya da ke yankin Arewa ta tsakiya, Kafanchan, ta shigar da kara a ofishin hukumar a ranar 13 ga watan Mayu. Audu ya bayyana cewa Danbaba ma’aikacin layin dogo ne ya saci batir din jirgin kasa guda biyu da silinda mai nauyin kilogiram 12 a ofishin sa ya sayar wa Emmanuel akan kudi N24,000...