Thursday, December 18
Shadow
Kalli Bidiyon: Mu da muke jiran tashin Qiyama? Trump ya dade bai kawo khari Najeriya ba>>Inji Aminu J. Town

Kalli Bidiyon: Mu da muke jiran tashin Qiyama? Trump ya dade bai kawo khari Najeriya ba>>Inji Aminu J. Town

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, Aminu J. Town yace a gayawa Trump ya gaggauta kawo harin da yace cewa zai kawo Najeriya. Yace Najeriya da ake jiran tashin Qiyama, wane irin tashin hankali ne ba'a gani ba a kasarnan? Yace 'yan Gwagwan ne ma zasu samu kasuwarsu ta bude. https://www.tiktok.com/@aminujtown/video/7568773069439896839?_t=ZS-917OnFf5Oin&_r=1 https://vt.tiktok.com/ZSyU2UAWB
Hujjojin da kuka kawo na banza da wofi ne, A kul kuka kaiwa Najeriya Khari>>Kasar China ta gargadi Amurka

Hujjojin da kuka kawo na banza da wofi ne, A kul kuka kaiwa Najeriya Khari>>Kasar China ta gargadi Amurka

Duk Labarai
China ta maida wa Amurka martani kana barazanar da ta yi wa Nijeriya Gwamnatin kasar China ta fitar da gargadi mai karfi kan duk wani yunkuri na tsoma baki cikin harkokin cikin gida na Najeriya, bayan kalaman da shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi na barazanar kai hari da sojoji a Najeriya bisa zargin cin zarafin Kiristoci. Da take jawabi a wajen taron manema labarai a ranar Talata, Mao Ning, mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar China, ta bayyana cewa, Beijing “na goyon bayan gwamnatin Shugaba Bola Tinubu gaba ɗaya yayin da take jagorantar al’ummar Najeriya kan tafarkin ci gaba da ya dace da halin ƙasar.” “China, a matsayinta na abokiyar haɗin gwiwar Najeriya, tana adawa da duk wata ƙasa da ke amfani da addini ko kare haƙƙin ɗan adam a matsayin hujja don tsoma baki...
Kalli Bidiyon: Amurka idan bata jefor Nokiliya Najeriya ba bata tsoron Allah>>Inji Sarkin Waka

Kalli Bidiyon: Amurka idan bata jefor Nokiliya Najeriya ba bata tsoron Allah>>Inji Sarkin Waka

Duk Labarai
Tauraron mwakin Hausa, Naziru Ahmad Sarkin Waka ya bayyana cewa Amurka ta kawo duk harin da zata kawo Najeriya musulmin Najeriya da Allah ya dogara. Naziru na martanine ga barazanar shugaban kasar Amurka, Donald Trump ta kawo hari Najeriya kan 'yan ta'adda. Yace dama dadin me ya ragewa Talakan Najeriya dan haka shi dai baya jin tsoro. Kalli Bidiyonsa anan: Kalli Bidiyon anan https://twitter.com/sarkinwaka_/status/1985637998197698792?t=WTa8Z_t9n5FkHrf9ybij2A&s=19
Ba’a fahimci Kalaman shugaban kasar Amurka Trump bane, Shifa Ba ‘yan Najeriya yace zai kawowa Khari ba, ‘yan Tà’àddà yace zai Yhaqa>>Inji Kungiyar Kiristocin Najeriya, CAN

Ba’a fahimci Kalaman shugaban kasar Amurka Trump bane, Shifa Ba ‘yan Najeriya yace zai kawowa Khari ba, ‘yan Tà’àddà yace zai Yhaqa>>Inji Kungiyar Kiristocin Najeriya, CAN

Duk Labarai
Kungiyar Kiristocin Najeriya, CAN ta bayyana cewa, da yawa basu fahimci kalaman Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ba. Kungiyar reshen jihohin Arewa 19 da Abuja ta bakin shugabanta, Rev. John Joseph Hayab ne ta bayyana hakan. Yace Ba 'yan Najeriya Trump yace zai kawowa hari ba, cewa yayi zai kawowa 'yan ta'adda harine, yace to menene na tayar da hankali inda ba mutum yasa yana da alaka da 'yan ta'addan ba? Yace wannan lamari kamata yayi ya zama hanyar da zata sa mu gyara matsalar tsaron mu ba wai ta zama hanyar cece-kuce akan addini ba.
Kalli Bidiyo: Duk macen da ta je gidan Solo na Musbahu Anfara sai ya aikata Alfasha da ita, mata 2 muka sani wanda ya dirkawa Cikin shege, Inji Wasu ‘yan Solo suka zargi Musbahu bayan Hirar da Hadiza Gabon ta yi dashi yace yana soyayya da ‘yan Fim amma ba zai iya aurensu ba

Kalli Bidiyo: Duk macen da ta je gidan Solo na Musbahu Anfara sai ya aikata Alfasha da ita, mata 2 muka sani wanda ya dirkawa Cikin shege, Inji Wasu ‘yan Solo suka zargi Musbahu bayan Hirar da Hadiza Gabon ta yi dashi yace yana soyayya da ‘yan Fim amma ba zai iya aurensu ba

Duk Labarai
Wasu 'yan matan Solo sun fito sun zargi Tauraron fina-finan Hausa, Musbahu Anfara da aikata Alfasha. Sun ce duk macen da ta je gidan solonsa sai yayi Alfasha da ita. Sun kara da zargin cewa, mata 2 suka sani wadanda ya dirkawa cikin shege. https://www.tiktok.com/@adijatouahmed3/video/7568678490589891858?_t=ZS-917CLO1J60n&_r=1 Hakan ya biyo bayan hirar da Hadiza Gabon ta yi dashine inda ya bayyana cewa yana soyayya da 'yan Fim amma ba zai iya aurensu ba. Yace dalilinsa shine yana son matar da zai aura ta zama zata iya hakura dashi kadai.
Ya kamata ‘yan Najeriya umsu goyi bayan zuwan kasar Amurka dan ta mana maganin matsalar tsaro>>Inji Adamu Garba

Ya kamata ‘yan Najeriya umsu goyi bayan zuwan kasar Amurka dan ta mana maganin matsalar tsaro>>Inji Adamu Garba

Duk Labarai
Tsohon Dan takarar shugaban kasa a jam'iyyar APC, Adamu Garba ya bayyana cewa ya kamata 'yan Najeriya su yi na'am da zuwan Amurka Najeriya dan ta magance mana matsalar tsaro. Yace Amurkar zata yaki 'Yan ta'adda dake Khashe mutane da kuma 'yan siyasa masu sace kudaden da aka ware dan magance matsalar tsaro. Ya kara da cewa, idan mutum baya cikin daya daga cikin biyun nan to bashi da matsala da kasar Amurka. Hakan ya zowa mutane da mamaki musamman lura da cewa, Adamu Garba dan Arewa ne inda 'yan Arewa da dama suka nuna rashin amincewa da wannan mataki na kasar Amurka.