
Babban Hadimin ministan Abuja ta bangaren sadarwa, Lere Olayinka ya soki mutanen, Arewa inda yace yanayin tsarin rayuwarsu ta auren mata barkatai da haihuwar ‘ya’yan da basu iya kulawa dasu ne ke kara rura wutar matsalar tsaron
Yace ta yaya me gadi dake daukar Albashin dubu 60 zai auri mata 4 ya haifi ‘ya’ya 17 ace ba za’a samu matsala ba?
Yace gasunan a Abuja kullun suna ganinsu da robar bara idan ya gansu yakan yi tunanin shin nan gaba wane irin mutane wadannan yaran zasu zama?
Yace wasu zasu zargi Gwamnati amma maganar gaskiya wannan ba laifin Gwamnati bane.