Thursday, January 15
Shadow

Sumar da yaran da muka kama suka yi a kotu duk karyace kawai dan su ja hankalin mutanene>>Inji Shugaban ‘yansandan Najeriya

Shugaban ‘yansandan Najeriya, IGP Kayode Egbetokun ya bayyana cewa, sumar da matasa 6 suka yi a kotu karyace kawai dan su jawo hankalin mutanene.

Saidai yace duk da haka an baiwa matasan taimakon gaggawa wanda hakan ke nuna kokarin ‘yansanda wajan ganin sun baiwa wanda suke tsare dasu kulawa.

Yace kuma maganar shekarun yaran idan dai mutum ya kai shekarar aikata laifi karancin shekarunsa basa hana a hukuntashi kuma haka dokar take koda a kasar Ingila ne.

Yace wasu daga cikin laifukan da ake zargin yaran da aikatawa sun hada da lalata dukiyar ‘yan kasa da kuma barazana ga tsaron kasa.

Ya kara da kira ga mutane da kada su nuna goyon bayan wani bangare kuma hukumar ‘yansanda zata tabbatar ta bayyana duk abinda ke faruwa ba tare da boye komai ba.

Karanta Wannan  An bayyana cewa tsohon Shugaban Jam'iyyar APC Abdullahi Umar Ganduje na ci gaba da samun sauƙi a bayan kwanciya jiɲÿa da ya yi a birnin London na ƙasar Birtaniya kamar yadda aka bayyana

Sanan ya bayar da tabbacin cewa hukumar ‘yansandan zata ci gaba da aiki bisa kwarewa da bin doka da oda.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *