Wednesday, April 29
Shadow

Yanzu-Yanzu: Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf yace cikin yaran da gwamnatin Tinubu ta kai kotu jiya akwai ‘yan Kano kuma zai dawo dasu gida

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya bayyana cewa an jawo hankalinsa game da kananan yaran da gwamnatin tarayya ta gurfanar a gaban babbar kotun tarayya dake Abuja bisa zargin yunkurin kifar da gwamnatin Tinubu ta hanyar zanga-zanga.

Gwamnan a sanarwar da ya fitar ta kafar X, ya bayyana cewa, ya baiwa kwakishinan Shari’a umarnin gaggauta yin abinda ya dace kan lamarin.

Ya karkare da cewa insha Allahu zai dawo dasu gida Kano.

Karanta Wannan  APC ta saka Naira Miliyan 20 a matsayin kudin fom din takarar Sanata sannan Naira Miliyan 10 a matsayin kufin Fom din takarar dan majalisar wakilai

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *