Saturday, November 8
Shadow

Tsadar Rayuwa: Yadda Gwamnan Kogi Ke Shan Garin Kwaki ba Suga da Ƙuli-ƙuli Cikin Dare

{“remix_data”:[],”remix_entry_point”:”challenges”,”source_tags”:[],”origin”:”unknown”,”total_draw_time”:0,”total_draw_actions”:0,”layers_used”:0,”brushes_used”:0,”photos_added”:0,”total_editor_actions”:{},”tools_used”:{},”is_sticker”:false,”edited_since_last_sticker_save”:false,”containsFTESticker”:false}

Gwamnan jihar Kogi Alhaji Ahmed Usman Ododo ya bayyana garin kwaki a matsayin abincin da ya riƙe shi a lokacin da ya ke makaranta, don haka ya bayyana cewa bai san lokacin da zai daina shan garin ba duk da cewa ya zama gwamna a yanzu.

Ododo ya bayyana haka ne cikin wani gajeren bidiyon da aka ɗaukeshi a lokacin da ya ke shan gari cikin dare, inda wanda ya dauki bidiyon ya yi barazanar yaɗawa amma gwamnan ya ce ko a jikinsa.

Gwamnan ya ce gari ya riga da ya bi jikinsa, don haka a duk lokacin da ya ke shan gari ya na tuna rayuwar da ya yi a makaranta ne a lokacin da ya ke karatu.

Karanta Wannan  Kalli Kayatattun hotunan Rahama Sadau

“Gari ya riga da ya bi jikina, kuma zan ci gaba da sha domin shi ya riƙeni a lokacin da na ke makaranta”. In ji gwamnan.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *