Tuesday, August 4
Shadow

Wasu kungiyoyi masu saka ido a harkokin siyasa daga jihar Gombe sun yi Allah wadai da kalaman Dan takarar Gwamna na jam’iyyar PDP, Farfesa Isa Ali Pantami inda sukace ya daina kalaman da zasu iya kawo rudani

Gamayyar Kungiyoyin dake saka ido akan harkokin siyasa a jihar Gombe me suna The Gombe State Coalition of Political Civil Societies and Association ta yi Allah wadai da kalaman dan takarar gwamnan jihar a karkashin jam’iyyar PDP, Farfesa Isa Ali Pantami.

Kungiyar tace kalaman da Dan takarar yayi a ziyarar da ya kai karamar hukumar Dukku abin damuwa ne kuma ya kamata ya kiyaye.

Kungiyar tace dukka ‘yan takarar ya kamata su kiyaye kalamansu da yanayin ma’amalarsu dan a samu siyasa me tsafta.

Kungiyar tace Jihar Gombe an santa da zaman lafiya da fahimtar juna suna kira ga ‘yan siyasar kada su kawo rudanin da zai canja hakan.

Karanta Wannan  Ɗalibai 379,997 za su sake zana UTME ta bana bayan da JAMB ta tabbatar da an samu tangarɗar na'ura

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *