Sunday, March 23
Shadow

YANZU-YANZU: Shugaban Ƙasa Bola Tinubu Ya Amince Da Naɗin Dakta Asiya Balaraba Ganduje A Matsayin Darakta A Hukumar Raya Arewa Maso Yamma

DAGA Bashir Abdullahi El-bash

A wani mataki na duba cancanta da ƙwazon aiki, shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu ya amince da naɗin Dakta Asiya Abdullahi Umar Ganduje a matsayin daraktar sashen kula da al’umma da raya yankunan karkara a sabuwar hukumar raya yankin Arewa maso Yamma.

Naɗin Dakta Asiya Ganduje a wannan matsayi ajiye ƙwarya ne a gurbinta duba da cewa mace ce jaruma mai juriya da himmar aiki. Ta daɗe tana ɗawainiya da hidimtawa al’umma ta fannoni daban-daban na rayuwa daga aljihunta. Ta ba da gagrumar gudunmawa wajen raya ilimi na addini da na zamani a birane da karkara. Ta taimaki ɗumbin jama’a da tallafin karatu, aikin yi, sana’o’in dogaro da kai da harkokin kula da kiwon lafiya da ayyukan jinƙai.

Karanta Wannan  Tonon Silili: Dama can Sanata Akpabio da Natasha Akpoti sun san juna kamin ta zama sanata>>Inji Daya daga cikin sanatocin

Dakta Asiya Ganduje ba a iya nan ta tsaya ba, mace ce mai kaifin ƙwaƙwalwa da basira. Ko da lokacin da mahaifinta yake matsayin gwamnan Jihar Kano ta yi amfani da ƙwarewarta ta fannoni daban-daban ta tallafa masa wajen samun nasarar lashe zaɓe. Ta ja mutane da dama a jiki ta taimake su wanda hakan ya ƙarawa mahaifinta da gwamnatinsa farin jini.

Ba ta wannan matsayi na darakta a hukumar raya yankin Arewa maso Yamma a yanzu, gagarumin cigaba ne ga Arewa da ma Najeriya gaba ɗaya. Domin kuwa ayyukan da aka kafa hukumar domin su tuni dama can ita ta yi nisa wajen gudanar da ire-irensu wanda wannan matsayi zai ƙara mata himma ne da cigaba da faɗaɗa alkhairanta su game ko’ina.

Karanta Wannan  Bankin China ya bai wa Najeriya rancen kuɗin gina titin jirgi kasa daga Kano zuwa Kaduna

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *