
Abale ya mayarwa da Aminu J. Town Martani kan sukar da ya masa saboda karbar shinkafar tallafi ta Nuhu Abdullahi da Naira dubu 50.
Aminu J. Town ya bayyana a cikin Bidiyonsa cewa Abale yafi karfin shinkafar kuma karbar da ya je yi zai zubar masa da kima a idon Duniya.
Saidai Abale cikin fushi hadda zagi ya cewa, Aminu J. Town ya kiyayeshi idan ba haka ba zasu hada kafar wando daya.
Yace yaransa ne aka hana shiga wajan karbar shinkafar shiyasa ya je dan a kyalesu.
Abale yace yana da kyamis wanda da kudinsa ya budeshi babu bashi hakanan kuma shima ya raba shinkafar.