Saturday, December 13
Shadow

‘Yan Bindiga sun kashe ‘yansanda 5 da sojoji 2 a Jihar Zamfara

Kwamishinan ‘yansandan jihar Zamfara, Muhammad Shehu Dalinja ya tabbatar da mutuwar ‘yansanda 5 da sojoji 2 wanda ‘yan Bindiga suka kashe a karamar hukumar Tsafe dake jihar.

Ya bayyana cewa ‘yan Bindigar sun yiwa jami’an tsaron kwantan baunane inda suka bude musu wuta a kan hanyar Gusau zuwa Funtua ranar Alhamis.

Ya bayyana cewa, ‘yan Bindigar sun tafi kaiwa kamfanin gini na Setraco Company Hari ne inda jami’an tsaron suka samu bayanan sirri suka tafi dan taresu.

Yace yanda aka yi suka kashe musu jami’ai kenan.

Karanta Wannan  Kalli Hoton Matashiyar da ta Kàshè kanta saboda bata ci maki me yawa ba a jarabawar JAMB

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *