
Wasu kungiyoyin fafutuka a jihar Sokoto sun yi zanga-zangar neman a sauke shugaban INEC, Farfesa, Joash Amupitan daga mukaminsa.
Kungiyoyin sun yi zanga-zangar ne a Ranar Laraba inda suka yi tattako zuwa ofishin INEC.
Shugaban zanga-zangar, Yusuf Abubakar ya bayyana cewa, suna neman shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sauke shugaban INEC ko kuma shugaban INEC din ya sauka da kansa.