Tuesday, August 4
Shadow

Ance wai Sheikh Ibrahim Inyas yaje da wasu ‘yan Najeriya kabarin Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) sun masa sallama kuma ya amsa har ma ya kira sunayensu, a wace jarida aka samu wannan labarin>>Inji Sheikh Lawal Triumph

Babban malamin Addinin Islama Sheikh Lawal Triumph ya kalubalanci ‘yan Darika cewa, ina aka samu labarin cewa wai Sheikh Ibrahim Inyas ya dauki malamai daga Najeriya sun je ziyarar kabarin Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam).

Wai da suka masa sallama sai ya amsa musu kuma ya kira sunan kowanne daga cikinsu, wannan yasa Larabawa mamaki suka yi ta shiga darika.

Yace yana son yasan a wace Jarida aka samo wannan labari sannan Fatima(AS) da Aliyu(AS) duk sun kaiwa Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam) ziyara kuma sun masa sallama amma bai kira sunayensu ba sai wadannan shehunnan?

Saidai an samu wani ya baiwa malam Amsa. Inda yacw shi yasan jaridar da aka samo wannan labarin.

Karanta Wannan  Ko da dalibi ya ci jarabawar JAMB ba tabbacin zai samu admission a jami'a>>Inji Hukumar JAMB

Kalli Bidiyon sa a kasa:

@fatihisani

#CapCut #fyp #viral #foryou Ai a cikin Jarida daya ne Labarin Yazo kuma gashi kaamar yadda muka skaa Part 1

♬ original sound – Fth sani

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *