Monday, January 19
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Majalisar Dattijai zata yi dokar saka ido da kula da ayyukan bankunan yanar gizo irin su Opay, Moniepoint da sauransu

Majalisar Dattijai zata yi dokar saka ido da kula da ayyukan bankunan yanar gizo irin su Opay, Moniepoint da sauransu

Duk Labarai
Majalisar Dattijai na shirin yin sabuwar doka dan kula da ayyukan bankunan yanar gizo irin su Opay, Moniepoint da sauransu. Dayake magana akan muhimmancin wannan doka, Sanata Adams Oshiomhole ya bayyana cewa, an taba sace masa kudi a asusun bankinsa kuma inda aka tura kudaden Opay ne da Moniepoint. Yace kuma basu da rassa a zahiri da mutum zai ce ya shigar da korafi. dan haka akwai bukatar a yi dokar da zata saka ido a ayyukan da suke. https://twitter.com/AsakyGRN/status/1996645682640265295?t=qvwu4FHmYIHsrWjka2UMqQ&s=19 Ita kuma a nata bangaren, Sanata Natasha Akpoti ta bayyana cewa wai idan aka yi wannan doka zata taimakawa matasan Najeriya dake samun kudi ta yanar gizo su rika samu daidai da takwarorinsu na kasashen waje. https://twitter.com/ChuksEricE/status/19...
Shugaba Tinubu ya aika da sunan Dambazau da karin wasu mutane da zai baiwa Mukamin jakadanci zuwa majalisa

Shugaba Tinubu ya aika da sunan Dambazau da karin wasu mutane da zai baiwa Mukamin jakadanci zuwa majalisa

Duk Labarai
Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya tura ƙarin sunan mutum 4 ɗoriya a kan waɗanda aka fitar a baya zuwa ga majalisar dattawa domin a tantance su a matsayin jakadun ƙasar da za a tura ƙasashen waje. Mutum huɗu da Tinubu ya tura su ne: Ibok-Ete Ekwe Ibas, tsohon shugaban riƙon-ƙwarya na jihar Rivers da tsohon ministan harkokin cikin gida Abdulrahman Dambazau. Sauran kuma su ne Sanata Ita Enang da tsohon gwamnan jihar Imo Chioma Ohakim. Yanzu dai jimilla shugaban ya tura sunan mutum 65 ke nan da yake buƙatar majalisar ta tantance, inda ake sa ran da zarar an tantance su, zai sanar da ƙasashen da za a tura su.
Kalli Bidiyon ‘yan Arewa daban-daban da suka je cirani jihohin Inyamurai da yarbawa aka kamasu aka ce Tshàgyèràn Dhàjì ne

Kalli Bidiyon ‘yan Arewa daban-daban da suka je cirani jihohin Inyamurai da yarbawa aka kamasu aka ce Tshàgyèràn Dhàjì ne

Duk Labarai
A 'yan kwanakinan kamen 'yan Arewa Hausawa da fulani na karuwa a jihohin Yarbaw da Inyamurai. Ana kama wadanda yawanci 'yan ciranine ana makala musu sunan garkuwa da mutane. Saidai da yawan 'yan kudun dake shahi akan wadanda ake kamawan na bayyana cewa ya kamata a tsananta bincike dan wadanda ake kamawa din basa kama da masu garkuwa da mutane. Lamarin dai ya jawo zazzafar muhawara a kafafen sadarwa. https://twitter.com/Gen_Buhar/status/1996249984149196897?t=4SM6pyVkOcIeSZZfRnaKTg&s=19 https://twitter.com/MFaarees_/status/1996271281671385142?t=ocMhMwwzvF9p541Rj0VJFQ&s=19 https://twitter.com/DrOzitababy/status/1996259267578327213?t=rY8c5tzGEQyd3XIwn_SJJQ&s=19
Peter Obi yayi Allah wadai da rabon motocin yakin neman zaben Tinubu na 2027 yayin da Talakawa ke cikin matsi

Peter Obi yayi Allah wadai da rabon motocin yakin neman zaben Tinubu na 2027 yayin da Talakawa ke cikin matsi

Duk Labarai
Ba Daidai Ba Ne Raba Motocin Kamfen Yayin Da Talakawa Ke Fama Da Yunwa, Obi Ya Soki Gwamnatin Tinubu Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam'iyyar LP a 2023, Peter Obi, ya soki raba motocin alfarma ga wakilan ƙungiyar Renewed Hope Ambassadors domin shirye-shiryen zaɓen 2027, lamarin da ya danganta ga gwamnatin Tinubu. A sanarwar da ya fitar, Obi ya ce wannan aiki tsananin rashin tausayi ne da cin amana, musamman a lokacin da ƴan ƙasa ke fama da yunwa, rashin aikin yi da matsalolin tsaro. Ya jaddada cewa maimakon kashe kuɗaɗen jama’a kan motocin kamfen, gwamnati ta mayar da hankali kan samar da abinci, kiwon lafiya, ayyukan yi da inganta tsaro.
Kalli Bidiyon: Malamin Addinin Islama Inyamuri ya bayyana cewa ba za iya Qìrgà sau nawa ‘yan Qabilarsa Inyamurai suka Jèfèshì da duwatsu ba saboda yana jawo hankalinsu zuwa a Musulunci

Kalli Bidiyon: Malamin Addinin Islama Inyamuri ya bayyana cewa ba za iya Qìrgà sau nawa ‘yan Qabilarsa Inyamurai suka Jèfèshì da duwatsu ba saboda yana jawo hankalinsu zuwa a Musulunci

Duk Labarai
Malamin Addinin Islama Inyamuri me suna Sheikh mohammed Chukwuemeka ya bayyana cewa ba zai iya Qirga sau nawa aka jefeshi ba dan yana jawo hankalin Inyamurai 'yan wansa su Musulunta. Yace amma hakan bata sa ya daina wa'azin ba kuma ba zai daina ba Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a BBC. https://twitter.com/7signxx/status/1996439541524451640?t=CB1zsBwOcHDGIi_VG21Gig&s=19
Da Duminsa: Kalli Yanda Janar Christopher Musa ya sha rantsuwar fara aiki a matsayin ministan tsaro

Da Duminsa: Kalli Yanda Janar Christopher Musa ya sha rantsuwar fara aiki a matsayin ministan tsaro

Duk Labarai
Janar Christopher Musa ya sha rantsuwar fara aiki a matsayin ministan tsaro. Me magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ne ya bayyana hakan. https://twitter.com/aonanuga1956/status/1996593270890107074?t=EeK9ZKw9jPgcNnNUi0HoVQ&s=19 Hakan na zuwane kwana daya bayan da majalisar dattijai ta amince dashi a matsayin Ministan tsaron bayan shugaba Tinubu ya aike mata da sunansa.
Kalli Bidiyon yanda wasu gungun Giwaye suka bayyana a Jihar Borno suna cinye amfanin gona

Kalli Bidiyon yanda wasu gungun Giwaye suka bayyana a Jihar Borno suna cinye amfanin gona

Duk Labarai
Giwaye sun bayyana a garin Kala Balge na jihar Borno inda suke cinye amfanin gona da yiwa dabbobin kiwo Barazana. Mawallafin harkar tsaro, Zagazola Makama ne ya bayyana hakan inda yace gwamnati ya kamata ta dauki mataki dan kawar wa mutane wannan barzanar. https://twitter.com/ZagazOlaMakama/status/1996574628915864020?t=pqzcAbzefL8m2QrlFXegWA&s=19