Friday, December 5
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kalli Bidiyo: Da cuwa-cuwa aka hada jama’ar da suka taru a wajan jana’izar Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Kalli Bidiyo: Da cuwa-cuwa aka hada jama’ar da suka taru a wajan jana’izar Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Duk Labarai
Wannan malamin yayi zargin cewa, da cuwa-cuwa aka tara jama'ar da suka taru a wajan jana'izar Sheikh Dahiru Usman Bauchi. Ya bayyana cewa kuma da wuya a samu mutane adalai 40 a cikin mutanen da suka taru a waja jana'izar malamin. Yayi zargin cewa duk 'yan Bindigar dake Arewa maso yamma 'yan darika ne inda yace an ga hotuna shehunan darika a jikin bindigun 'yan Bindigar. https://www.tiktok.com/@zaidou1taza/video/7578672250929433867?_t=ZS-91r33VPcVO4&_r=1
Dalibai Kiristoci na Jami’o’in Federal University Kashere, Gombe da BUK Kano sun koka da cewa akwai masallatai da yawa a wadannan jami’o’in amma an hanasu gina coci ko guda daya

Dalibai Kiristoci na Jami’o’in Federal University Kashere, Gombe da BUK Kano sun koka da cewa akwai masallatai da yawa a wadannan jami’o’in amma an hanasu gina coci ko guda daya

Duk Labarai
Daliban jami'o'in Federal University Kashere, Gombe dana jami'ar BUK, Kano Kiristoci sun koka da cewa, akwai masallatai da yawa a wadannan jami'o'in amma an hanasu gina coci ko guda daya. Daya daga cikin daliban na Kashere ne ya fito yake zanga-zanga shi kadai inda yace suna bukatar Coci a jami'ar. https://twitter.com/Zeru010/status/1995207329504235744?t=PK6iWd492V___RWeKguilw&s=19 Wani kirista ta bayyana cewa abin haushin shine jihar Gombe da yawan musulmai da kirista daidai suke watau 50/50 amma irin wannan abin na faruwa. https://twitter.com/Zeru010/status/1995375684320207249?t=b2LtmuYCGtr1EUeOSloutg&s=19 Wannan zanga-zanga da dalibin yayi tasa shima wani dalibin jami'ar BUK Kano ya bayyana cewa suna hakan take, akwai masallatai a BUK amma su ba'a basu damar...
Facebook da Instagram sun kulle shafin mawakin Najeriya, Edris Abdulkarim saboda yiwa Trump waka

Facebook da Instagram sun kulle shafin mawakin Najeriya, Edris Abdulkarim saboda yiwa Trump waka

Duk Labarai
Shafukan sada zumunta na Facebook da Instagram sun kulle shafin mawakin Najeriya, Edris Abdulkarim saboda wakar da yawa shugaban kasar Amurka, Donald Trump. Idris yayi wakar ne akan harin da aka ce Trump din zai kawo Najeriya. Sannan ya bayyana irin matsalolin tsaron da Najeriya ke fama dasu. Ya kuma bayyana irin satar kudin da 'yan siyasa ke yi da rashawa da cin hanci yayin da Talakawa ke fama da matsalar tsaro da Talauci. Saidai bincike ya nuna cewa tuni an kulle shafinsa saboda wannan wakar.
Kalli Bidiyon: An ga Bilal Villa a daji dauke da Bìndyghà, lamarin ya jawo cece-kuce inda ya bayyana cewa sabuwar waka ce

Kalli Bidiyon: An ga Bilal Villa a daji dauke da Bìndyghà, lamarin ya jawo cece-kuce inda ya bayyana cewa sabuwar waka ce

Duk Labarai
Bidiyon Tauraron matashin mawakin Arewa, Bilal Villa a daji sanye da kayan sojoji ya bayyana a kafafen sada zumunta inda kuma aka ganshi dauke da Bindiga. Lamarin ya jawo cece-kuce sosai inda wasu ke cewa ko da barkwanci ne hakan bai kamata ba musamman yanda ake cikin halin matsalar tsaro. https://twitter.com/iam_muazzam1/status/1995226619695469001?t=AU2y5OgiB5JSw2RIUr92zQ&s=19 Babu dai tabbacin ingancin Bidiyon ko na gaske ne ko kuwa AI ne. Saida a wani lamarin me kama da wannan, An kuma ga Bilal Villa a wani Bidiyo a daji sanye da kayan sojoji shima yana cewa suna daukar waka ne. A karshen Bidiyon yace shi ba da Bindiga bane. https://www.tiktok.com/@bilalvillah675/video/7578480300410342677?_t=ZS-91qvLVI9Sam&_r=1 https://www.tiktok.com/@daddy_collection/...
Da Duminsa: Abin ya zo, Kasar Amurka ta turo jirgin Leken Asiri Najeriya

Da Duminsa: Abin ya zo, Kasar Amurka ta turo jirgin Leken Asiri Najeriya

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Kasar Amurka ta aiko da jirgin saman Lekan Asiri zuwa Najeriya. Jirgin kamar yanda me saka ido akan ayyukan masu ikirarin Jìhàdì a yankunan Sahel, Brant Philip ya bayyana, yace ya yi leken Asirin ne a Jihar Borno, Akan Kungiyar ÌSWÀP. Jirgin ya taso ne daga matsugunin kasar Amurkar dake kasar Ghana. Sahara Reporters ta ruwaito Brant Philip yana cewa Gwamnatin Najeriya ta amincewa kasar Amurkar ta kai hari kan 'yan kungiyar. Sannan yace Amurkar zata yi amfani da jihar Naija a matsayin matsuguninta yayin wannan aiki. Saidai hadimin tsohon shugaban kasa, Malam Bashir Ahmad ya soki Brant Philip inda yace bai kamata ya fitar da wannan bayani ba dan bayanine na sirri kuma kamar yana ankarar da 'yan Kungiyar ÌŚWÀP dinne su shiryawa harin.
Kalli Bidiyon:Ina nan kan bakana ina son in auri matar tsohon shugaban kasa, A’isha Buhari kuma insha Allahu zata amince, masu min bakin ciki inga yanda zaku yi >>Inji Umar Khalid

Kalli Bidiyon:Ina nan kan bakana ina son in auri matar tsohon shugaban kasa, A’isha Buhari kuma insha Allahu zata amince, masu min bakin ciki inga yanda zaku yi >>Inji Umar Khalid

Duk Labarai
Matashi Umar Khalid da ya fito ya bayyana soyayyarsa ga matar tsohon shugaban kasa, Hajiya A'isha Buhari ya jaddada soyayyar tasa. Yace yana son ya auri A'isha Buhari da gaske kuma in Allah ya yadda zata amince inda yace sai ya ga yanda 'yan Bakin ciki zasu yi. https://www.tiktok.com/@umarpitykhalid0/video/7578512484462644498?_t=ZS-91prORQwqob&_r=1