Monday, July 6
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Sati 3 kenan tun bayan da shugaba Tinubu ya tafi kasar waje, ‘yan Najeriya sun fara tambayar lafiya kuwa?

Sati 3 kenan tun bayan da shugaba Tinubu ya tafi kasar waje, ‘yan Najeriya sun fara tambayar lafiya kuwa?

Duk Labarai
Tun ranar 28 ga watan Disamba na shekarar 2025 ne shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bar Najeriya zuwa Turai. Shugaban ya kuma halarci taron kasashen Duniya dake gudana a kasar UAE. Yanzu sati 3 kenan shugaba Tinubu baya Najeriya. 'Yan Najeriya da yawa a kafafen sada zumunta sun fara tambayar shin ina shugaban kasar ya shigane? Wasu na tambayar Allah sa dai Lafiya. Rahotanni sun bayyyana cewa, Kwanakin shugaba Tinubu 961 akan Mulki saidai a cikin wadannan kwanakin ya shafe wanaki 240 a kasashen waje. Watau a duk cikin kwanaki 4 da yayi yana mulki, kwana daya yayi shi ne a kasashen waje. https://twitter.com/i/status/2012445361525166455 https://twitter.com/i/status/2012480257945681962 https://twitter.com/i/status/2012450978323165459
Kalli Bidiyon: Abinda Wannan mahaifin yawa ‘ya’yansa da ya dauki hankula sosai

Kalli Bidiyon: Abinda Wannan mahaifin yawa ‘ya’yansa da ya dauki hankula sosai

Duk Labarai
Wannan mahaifin ya sayawa 'ya'yansa Wardrobe ta saka kaya da suka dade suna tambayarsa ya siya musu. Ya nuna yanda kayan yaran nasa ke zube a kasa inda yace sun dade suna rokonsa ya sai musu inda zasu rika saka kayansu. Yace ya dade yana son ya sai musu sai aka yi sa'a wani abokinsa yana son sayarwa ya kirashi yace ya saya. An ga yaran nata murna bayan da suka dawo daga makaranta suka tarar da mahaifinsu ya saya musu Wardrobe din. https://twitter.com/i/status/2012415996615700912
Kalli Bidiyon: Gwamnan jihar Kebbi tare da soja me guntulen Hannu da ya jawo cece-kuce sosai

Kalli Bidiyon: Gwamnan jihar Kebbi tare da soja me guntulen Hannu da ya jawo cece-kuce sosai

Duk Labarai
A ranar Tunawa da 'yan mazan jiya, Gwamnan jihar Kebbi, Nasiru Idris ya hadu da wani soja da ya rasa hannunsa a wajan aiki. An gabatar da sojan a wajan gwamnan, inda gwamnan yace a yiwa sojan hannun Roba, inda yace a masa me kyau, har yana tambaya duka nawa yake? https://twitter.com/i/status/2012100209048977895 Saidai wannan lamari ya jawo cece-kuce inda masu sharhi suka zargi gwamnan da rashin nuna tausai ga sojan musamman ganin cewa ya rasa hannun nasa ne wajan yiwa kasa Hidima. Masu Sharhin na ganin cewa ba maganar kudi kawai bace, ya kamata gwamnan ya nuna alhini da halin da sojan ke ciki.