Wednesday, May 6
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kalli Bidiyon Yanda Hàrsàsàì suka fado daga cikin wata Mota data je wucewa ta kofar jami’ar ABU Zaria

Kalli Bidiyon Yanda Hàrsàsàì suka fado daga cikin wata Mota data je wucewa ta kofar jami’ar ABU Zaria

Duk Labarai
Rahotanni daga garin Zaria, Jihar Kaduna na cewa, Harsasai sun fado daga cikin wata mota da ta je wucewa ta kofar jami'ar ABU dake garin. Saidai kamin a ankara motar ta tsere. An ga yanda mutane suka rika tattara harsasan dake zube a kan titi bayan tserewar motar. https://twitter.com/DejiAdesogan/status/1993595283163296074?t=VnHyYZBpBXKh1XXSyu2KOQ&s=19
Ni fa nafi damuwa da Tshàgyèràn Dhàjì fiye da mutanen da suke Dàukà>>Inji Sheikh Dr. Ahmad Gumi

Ni fa nafi damuwa da Tshàgyèràn Dhàjì fiye da mutanen da suke Dàukà>>Inji Sheikh Dr. Ahmad Gumi

Duk Labarai
Malamin addinin Islama, Sheikh Dr. Ahmad Gumi ya bayyana cewa, yafi damuwa da Tshàgyèràn Dhàjì fiye da mutanen da suke yin Garkuwa da su. Malam ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a Channels TV inda yace kamar a Asibiti ne idan aka kawo mutum na zubar da jini, ana fara tsayar da jinin ne farko kamin a fara gyaran ciwo ko dinki. Malam yace misali Mahaukaci ne a kasuwa ya cakawa mutane da yawa wuka, kamata yayi a fara kwace wukar dake hannunsa kamin a fara kula wadanda ya cakawa wukar. Yace bawai bai damu da wadanda lamarin 'yan Bindigar ke shafa ba, abinda yake magana akai shine a fara dakatar da zubar da jinin tukunna.
Kalli Bidiyon: Gwamnati ta kàsà kàrbàr daliban Kebbi daga hannun mu ta Qarfi, sai dai Sulhu aka yi muka badasu>>Inji Tshàgyèràn Dhàjì

Kalli Bidiyon: Gwamnati ta kàsà kàrbàr daliban Kebbi daga hannun mu ta Qarfi, sai dai Sulhu aka yi muka badasu>>Inji Tshàgyèràn Dhàjì

Duk Labarai
'Yan Bìndìgà da suka yi garkuwa da daliban makarantar MAGA dake jihar Kebbi sun bugi Qirji cewa Gwamnati ta kasa karbar dalibai ta Qarfi sai Sulhu aka yi suka bayar da daliban. A Bidiyon da suka saki, an jisu suna tambayar daliban shin Jiragen sama nawa suka ji sun wuce ta saman su suka ce basu san iyaka ba. Sannan sun tambayi daliban cewa, ko an tabasu ko an ci zarafinsu? Suka ce a'a. https://twitter.com/AM_Saleeeem/status/1993429655479566738?t=ADbi262pk3LD7RWtFJBNUQ&s=19
Kalli Bidiyon: Naga matata dana saki Maryam maza sun baibayeta wai zasu aureta, amma ni nasan Ummaruntane kawa zai sha Dùkà su watse su barta>>Inji Gfresh

Kalli Bidiyon: Naga matata dana saki Maryam maza sun baibayeta wai zasu aureta, amma ni nasan Ummaruntane kawa zai sha Dùkà su watse su barta>>Inji Gfresh

Duk Labarai
Tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin ya bayyana cewa, yaga masa sun baibaye Matarsa daya saka watau Maryam. Yace suna mata Qaryar wai zasu aureta. Yace amma shi yasan Ummaruntane kawai za sha duka su watse su barta. Dana nan dan kallon Bidiyon Gfresh dai ya saki matarsa, Maryam ne bayan da fada ya kaure tsakaninsu kan zuwansa gidan tsohuwar matarsa, Safiya Haruna.
Fatana shine a Samu Wani Minista ya aureni, Shi kuma Gfresh Baqin ciki ya hàllàqàshì>>Inji Tsohuwar Matar Gfresh, Maryam

Fatana shine a Samu Wani Minista ya aureni, Shi kuma Gfresh Baqin ciki ya hàllàqàshì>>Inji Tsohuwar Matar Gfresh, Maryam

Duk Labarai
Tsohuwar matar Tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin wadda ya saka kwanannan, watau Maryam ta yi fatan a samu wani Minista ya aureta shi kuma Gfresh Al-amin Baqin ciki ya Hallaqashi. Ta wallafa hakanne a shafinta na Tiktok. Wani ne ya mata comment din hakan inda saboda jin dadi da amincewa da comment din ta hadashi da hotonta ta dora a shafinta. Kalli Bidiyon anan https://hutudole.com/fatana-shine-a-samu-wani-minista-ya-aureni-shi-kuma-gfresh-baqin-ciki-ya-hallaqashiinji-tsohuwar-matar-gfresh-maryam/
Ji yanda ta kaya tsakanin Tsohon Minista, Sheikh Isa Ali Pantami da wani daya zargeshi da Shyekye Kirista a ATBU

Ji yanda ta kaya tsakanin Tsohon Minista, Sheikh Isa Ali Pantami da wani daya zargeshi da Shyekye Kirista a ATBU

Duk Labarai
Wani ya zargi Tsohon Minista, Malamin Addinin Islama, Sheikh Farfesa Isa Ali Pantami da sawa a Shyekye wani kirista a jami'ar ATBU. Saidai malam ya mayar masa da martanin cewa wannan zancen karyane dan bai taba kashewa ba kuma bai taba sawa a kashe wani ba. Mutumin ya kawo Rahoton jaridar Punchng da hotunan dalibin da ake zargin malam akai. Saidai malam yace idan mutumin yana jin yana da hujja akan wannan zargi nasa, ya kai kotu ko kuma ya bayar da cikakkun bayanansa dan shi malam ya kaishi kotu a yi shari'a, malam yace kaga a haka ma idan zargin da ake masa da gaskene, shi mutumin ya taimaki iyalan mamacin kenan sai a hukuntashi. Saidai wasu sun rika baiwa malam Shawarar ya maka jaridar ta Punchng a kotu da wanda ya masa wannan zargi. Amma wasu sun baiwa malam shawarar cew...
Kai Duniya: Ji yanda Wani Marar Imani ya tsallaka Maqabara ya Qàqùlò Qàbàrìn Jariri a Potiskum, Jihar Yobe

Kai Duniya: Ji yanda Wani Marar Imani ya tsallaka Maqabara ya Qàqùlò Qàbàrìn Jariri a Potiskum, Jihar Yobe

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Yobe na cewa, wani mutum ya tsallaka katangar maqabartar Potiskum ya tone Qabarin wani jariri sannan ya tsere da gawar. Kakakin 'yansandan jihar,  SP Dungus Abdulkarim ya tabbatar da faruwar lamarin. Ya koka da yawaitar tone-tonen Qaburbura a jihar. Inda yace ko a farkon watannan sai da suka samu Rahoton irin hakan a Karamar hukumar Jakusko inda har yanzu suna neman wanda ake zargin. Kwamishinan 'yansandan jihar CP Emmanuel Ado ya yi Allah wadai da lamarin inda ya baiwa duk DPO dake fadin jihar umarnin su saka ido a maqabartun jihar dan hana irin haka faruwa.
Mun yi Namijin kokari wajan kubutar da Daliban jihar Kebbi, Ina jinjinawa jami’an tsaron mu>>Inji Ministan Tsaro, Bello Matawalle

Mun yi Namijin kokari wajan kubutar da Daliban jihar Kebbi, Ina jinjinawa jami’an tsaron mu>>Inji Ministan Tsaro, Bello Matawalle

Duk Labarai
Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle ya bayyana cewa, sun yi kokari sai wajan nasarar kubutar da daliban makarantar MAGA na jihar Kebbi. Ya bayyana cewa, yana jinjinawa jami'an tsaro kan namijin kokarin da suka yi wajan wannan nasara da aka samu. Yace sun gudanar da aikinne bisa umarnin shugaban kasa Bola Tinubu. https://twitter.com/Bellomatawalle1/status/1993395151671062682?t=RKtiwXLCCSe1UVMXvVpSCg&s=19
Kalli Bidiyon Yanda Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle ya gana da daliban makarantar Jihar Kebbi da aka kubutar

Kalli Bidiyon Yanda Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle ya gana da daliban makarantar Jihar Kebbi da aka kubutar

Duk Labarai
Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle ya gana da daliban makarantar MAGA su 24 banyan an kubutar dasu. An ga ministan a jikin motar daliban inda yake tambayarsu ko an tabasu? An ji daliban na cewa ba'a taba su ba. Amma dai 'yan Bindigar sun rika musu barazanar cewa zasu Yqnka su. https://twitter.com/Minikothe3rd/status/1993365275186450443?t=HVbzCRkR84_9uYoYDN5sAA&s=19