Wannan Bidiyon na Tauraruwar fina-finan Hausa, Maryam Booth ya dauki hankula a kafafen sada zumunta.
Da yawa sun rika bayyana ra'ayoyinsu akai inda wasu ke cewa anya ba Ciko ta yi ba?
https://www.tiktok.com/@b.villah/video/7580442333619965204?_t=ZS-91zaBSXF58b&_r=1
Attajirin Najeriya, Alhaji Aliko Dangote ya bayyana cewa akwai ban haushi sosai yanda wasu mas kudi ke kashe Miliyoyin kudade wajan sayen motocin Alfarma da jiragen sama.
Yace wani lokacin idan yayi tafiya da jirginsa, babu ma wajan da zai ajiyeshi saboda duk filin jirgin an cikeshi da jiragen mutane.
Yace maimakon wannan barnar kudin, kamata yayi ace masu kudin sun bude kamfanoni ne ta yanda Dukiyarsu zata habaka kuma su samarwa matasa ayyukan yi.
https://www.tiktok.com/@soartvs/video/7580508561025846536?_t=ZS-91zVMhrvcLw&_r=1
Tauraron Tiktok, Gfresh Al-amin kenan a wannan Bidiyon inda ya sumbaci Amaryarsa, Maryam da aka daura musu aure jiya.
A jiya ne dai aka daura auren a garin Gombe kamar yanda Hutudole ya kawo muku.
Abokinsa Aminu J. Town da sauransu ne suka shige gaba-gaba wajan wannan bikin.
https://www.tiktok.com/@ib.exclusive/video/7580650872405871892?_t=ZS-91zUDDsqdCj&_r=1
Da gidan Marigayi Sheikh Dahiru Usman Bauchi, Me suna Naziru ya bayyana cewa mahaifinsu bai rasu ba.
Yace malam ya koma wata rayuwa ce ta daban.
https://www.tiktok.com/@nazirutahir/video/7580423434748906772?_t=ZS-91zTNuhB4cr&_r=1
Wasu iyaye na zargin wani malami da yiwa 'ya'yansu 9 Luwadi a Abuja.
Lamarin kamar yanda gidan Rediyo da TV na Brekete Family suka ruwaito ya farune a Abuja inda iyayen har sun kai korafi wajan 'yansanda kuma har an kama wanda ake zargi.
Saidai sun ce daga baya sun samu Rahoton cewa an sakeshi.
Mutumin an ce har jan Sallah yana yi a unguwarsu sannan kuma yaran sun ce idan yayi Luwadi dasu yakan musu barazanar Mutuwa idan suka gayawa wani.
https://www.tiktok.com/@sahabi_jaafar_yellow/video/7580518215625788693?_t=ZS-91zOVlLTp8D&_r=1
Sanata Natasha Akpoti ta ce dama irin damar da take son samu kenan wadda bata samu a bayaba ta tonawa sanata Godswill Akpabio asiri kan yanda ya nemi yin lalata da ita.
Ta bayyana hakane bayan da sanata Godswill Akpabio ya maka ta a kotu yana neman ta biyashi diyyar Naira Biliyan 200 saboda zargin ta bata masa suna da zargin karya data masa na cewa ya so yin lalata da ita.
Sanata Natasha Akpoti tace lallai ta samu sammacen kotu akan karar da Sanata Godswill Akpabio ya shigar akanta.
Tace yanzu ne ta samu damar tona masa Asiri.
A tace a baya abinda yasa bata tona masa asiri ba, a dokar majalisa sai ta gabatar da korafinta a gaban kwamitin bincike kamin taje kotu amma ba'a bata wannan damar ba amma yanzu ta ji dadi tunda da kansa ya kai magana kotu.
Tsohon Ministan shari'a a zamanin Mulkin tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari, Abubakar Malami ya bayyana cewa baya cikin masu daukar nauyin taaddaci a Najeriya.
Ya bayyana hakane a matsayin martani kan wani rahoto da ya zargeshi da wasu manyan Arewa da alaka da wasu da ake zargin masu daukar nauyin ta'addanci ne.
Malami yace a tarihinsa ba'a taba zarginsa ba ko aka kamashi ko aka masa shari'a akan daukar nauyin ta'addanci ba.
Yace ko tsohon Janar din da ya bayar da labarin ba yace yana zarginsu bane, yace an gano suna da alaka ne da mutanen da ake bincike.
Yace dan haka bashi da hannu a lamarin daukar nauyin ta'addanci a Najeriya.
Bidiyon Shoprite na Abuja dake Apo a dauki hankua baya da aka ga babu komai a cikinsa.
Wata da ta je Shoprite dinne ta fito ta bayyana hakan inda tace idan zasu kulle gara su kulle kawai amma wannan irin abin bai kamata ba.
https://twitter.com/abujastreets/status/1997053577882489155?t=noUX5sfsywnG3uFOk9qaKw&s=19
Shoprite dai sun kulle shagunansu a sassa daban-daban na Najeriya.
Kakakin majalisar Dattijai, Sanata Godswill Akpabio ya maka sanata Natasha Akpoti a kotu inda yace yana neman ta biyashi diyyar Naira Biliyan 200 saboda bata masa suna.
Akpabio yace Natasha ta mai karyar cewa ya nemi yin lalata da ita wanda hakan ya bata masa suna sosai an rika masa dariya da wulakanci.
Yace dan haka yana neman kotu ta tursasa Sanata Natasha Akpoti ta janye wannan zargi da take masa sannan ta goge duk wani abu me alaka da wannan zargi data wallafa a kafafen sada zumunta sannan kuma ta fito ta bashi hakuri.
Sahara Reporters ta ruwaito cewa, wani tsohon janar, General, Ali-Keffi ya bayyana cewa a zamanin tsohon shugaban kasa, Janar Muhammadu Buhari an nadashi ya jagoranci binciken masu daukar nauyin 'yan ta'adda a Najeriya.
Yace binciken su ya kamo mutane 20 da ake zargi.
Yace cikin mutane 20 din da ake zargi akwai wadanda ke da alaka da Tsohon shugaban sojoji, Janar Tukur Yusuf Buratai da Tsohon babban lauyan Gwamnati, Abubakar Malami da Tsohon Gwamnan babban bankin Najeriya, CBN, Godwin Emefiele da tsohon shugaban sojoji, Janar Farouk Yahya.
Yace amma kwatsam sai aka kamashi.
Yace ana tsareshi na wani lokaci sannan aka masa ritayar dole.
Yace har yau bai san laifin da ya aikata ba aka masa wancan wulakanci.
Yace sannan ya samu Labarin an saki mutane 20 din da suka kama in...