Thursday, December 18
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Haka Na Saba: Garzali Miko yayi martani kan ganinshi yana loma da abinci a wajan Bikin Rarara

Haka Na Saba: Garzali Miko yayi martani kan ganinshi yana loma da abinci a wajan Bikin Rarara

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa, Kuma Mawaki, Garzali Miko yayi martani kan ganinshi da aka yi yana Loma a wajan Bikin Rarara da A'ishatulhumaira. Hutudole ya kawo muku cewa, yanayin cin abincin da Garzali miko yayi da hannu yana loma a wajan ya jawo cece-kuce a wajan. Saidai a wani sabon bidiyon an ga Garzali Miko yana cewa, shi haka ya saba cin abinci da hannu. https://www.tiktok.com/@kb_international/video/7504359246134398213?_t=ZM-8wR2hDy6B8v&_r=1 Yace ko a gobe ya samu dama da hannu zai ci abinci.
Bamu yadda ba, A mayar dasu gida, wane irin aiki ne zasu yi wanda matasanmu ba zasu iya yi ba? NLC ta jihar Legas ta yi gargadi kan matasa 89 daga Arewa da aka kai Su yi aiki a matatar man Dangote dake Legas

Bamu yadda ba, A mayar dasu gida, wane irin aiki ne zasu yi wanda matasanmu ba zasu iya yi ba? NLC ta jihar Legas ta yi gargadi kan matasa 89 daga Arewa da aka kai Su yi aiki a matatar man Dangote dake Legas

Duk Labarai
Rikicin 'yan matasan Arewa 89 da aka kai Matatar man Dangote dake Legas su yi aiki har yanzu bai kare ba. Da farko dai hutudole ya kawo muku rahoton cewa, bayan kai matasan jihar Legas, an zargi cewa 'yan Bindiga ne inda har 'yansanda suka yi bincike kan lamarin suka gano cewa ba 'yan Bindiga bane aiki aka kaisu su yi a matatar man fetur din ta Dangote daga jihar Katsina. Saidai duk da wankesu, a yanzu kuma kungiyar kwadago ta jihar karkashin Wakilinta, Comrade Funmi Sessi sun ce basu yadda da kawo matasan 'yan Arewa ba. Yace wane irin aiki ne Wanda sai an dakko matasan Arewan zasu yi wanda matasan jihar Legas ba zasu iya yiba, yace kuma dokar Najeriya ta tanadi cewa, dole a baiwa mutanen da ke kusa da kamfanin Kaso 70 na ma'aikatan da za'a dauka in yaso sauran kaso 30 din ana iya...
Sha’aban Sharada ya sauya sheƙa zuwa APC

Sha’aban Sharada ya sauya sheƙa zuwa APC

Duk Labarai
YANZU-YANZU: Sha'aban Sharada ya sauya sheƙa zuwa APC Dan takarar gwamnan jihar Kano a jam'iyyar ADP a zaben 2023, Sha'aban Sharada ya sanar da ficewar sa daga jam'iyyar zuwa APC. A wani faifen bidiyo da ya karade shafukan sada zumunta, Sharada, tsohon dan majalisar wakilai mai wakiltar mazaɓar Kano Municipal, ya sanar da komawa APC din ne a wata liyafa da ya haɗa ga magoya bayan sa a gidan sa da ke Kano. Ya ce ya auna ya ga cewa "da sabon gini gwanda yaɓe", bayan ya maida al'amuran ss ga Allah kan Ya yi masa zaɓi na alheri. DAILY NIGERIAN HAUSA ta rawaito cewa a kwanakin bayan an hango Sharada tare da shugaban jam'iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje a Abuja, lamarin da tun a lokacin ake kallon kamar yunkurin komawa jam'iyyar ta sa ya ke yi. A lokacin da ya ke taka...
Mu a Akwa Ibom Tinubu za mu yi a 2027>>Akpabio

Mu a Akwa Ibom Tinubu za mu yi a 2027>>Akpabio

Duk Labarai
Mu a Akwa Ibom Tinubu za mu yi a 2027 - Akpabio Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya ce dukkan jam’iyyun siyasa a jihar Akwa Ibom sun hade wuri guda. Ya kara da cewa wannan hadin gwiwa zai mara wa Shugaba Bola Tinubu baya domin sake tsayawa takara, da Gwamna Umo Eno na jihar, da kuma shi kansa Akpabio. Akpabio ya bayyana hakan ne a ranar Juma’a yayin taron rabon tallafi ga al'ummar mazabarsa da kuma kaddamar da ayyuka a Ikot Ekpene, yankin Akwa Ibom na arewa maso yamma. “Yayin da nake magana da ku yanzu, babu wani abin da ake kira jam’iyya a jihar Akwa Ibom a shekarar 2027,” in ji shi. “Don kujerar majalisar dattawa ta yankin Ikot Ekpene, dukkan jam’iyyun siyasa sun hade don kada kuri’unsu ga Sanata Godswill Akpabio. "Kujerar gwamna a shekarar 2027, dukkan...
ALLAH SARKI: Bayan Sun Yi Garkuwa Da Wannan Kàŕamìn Yaroñ, Daga Bisani Sun Kaśhè Shì Tare Da Jefa Gàwàrsà A Ŕamìn Masài A Šokoto

ALLAH SARKI: Bayan Sun Yi Garkuwa Da Wannan Kàŕamìn Yaroñ, Daga Bisani Sun Kaśhè Shì Tare Da Jefa Gàwàrsà A Ŕamìn Masài A Šokoto

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} ALLAH SARKI: Bayan Sun Yi Garkuwa Da Wannan Kàŕamìn Yaroñ, Daga Bisani Sun Kaśhè Shì Tare Da Jefa Gàwàrsà A Ŕamìn Masài A Šokoto
Za a samar da ƙarin kayan aiki don daƙile ƴan ta da ƙayar-baya – Janar Chris Musa

Za a samar da ƙarin kayan aiki don daƙile ƴan ta da ƙayar-baya – Janar Chris Musa

Duk Labarai
Babban hafsan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya tabbatarwa ƴan Najeriya cewa sojoji na aiki tukuru domin shawo kan matsalolin tsaro da ke ƙaruwa a baya-bayan nan. Ya bayyana cewa shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin samar da ƙarin kayan aiki - musamman na sama domin ƙarfafa yaƙi da ƴan ta da ƙayar baya da ake yi. Janar Musa ya bayyana haka ne bayan wata ganawa da shugaban Najeriyar ya yi da manyan hafsoshin tsaron ƙasar a fadarsa da ke Abuja ranar Juma'a. Babban hafsan ya ƙara da cewa tuni aka sayo kayan yaƙin domin daƙile ayyukan masu iƙirarin jihadi, waɗanda suka zafafa kai hare-hare a ƴan watannin nan, musammman a yankin arewa maso gabashin ƙasar. "Shugaban ƙasa ya ba da umarnin abu na gaba da za a yi, da kuma haɗa-kai da sauran ƙasashe da muke makwabtaka da su ...
Masu ikirarin Jìhàdì sun kàshè  manoma da masunta 40 a jihar Borno

Masu ikirarin Jìhàdì sun kàshè manoma da masunta 40 a jihar Borno

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa ƙungiyar mayaƙan ÌŚWÀP ta kashe wasu manoma 23 da kuma masunta a wani hari da ta kai ƙauyen Malam Karanti kusa da Baga a karamar hukumar Kukawa na jihar Borno. Majiyoyi sun ce mayaƙan sun tara manoman da kuma masunta ne wuri ɗaya, inda suka kashe manoman wake 23. An hana mazauna garin ɗaukar gawawwakin ƴan uwansu da aka kashe, kamar yadda gidan talabijin na Channels a Najeriya ya ruwaito. "Mun yi ƙoƙarin zuwa don ɗaukar gawawwakin waɗanda aka kashe tare da jami'an tsaro, sai dai mayaƙan sun hana mu yin haka. Iyalai da dama na jiran gawawwakin ƴan uwansu," in ji wani ɗan garin. Ƙauyen Malam Karanti matattara ne na mayaƙan ISWAP, wuri kuma da fararen hula ke noma da kamun kifi duk da irin barazanar da suke fuskanta.
Hukumar tace fina-finai ta haramta bikin ‘ƙauyawa’ a jihar Kano

Hukumar tace fina-finai ta haramta bikin ‘ƙauyawa’ a jihar Kano

Duk Labarai
Hukumar tace fina-finai a jihar Kano ta sanar da haramta bukukuwan Kauyawa da ake yi a faɗin jihar, a wani mataki na ƙarfafa kyawawan ɗabi'u tsakanin al'umma da kuma bin doka. Shugaban hukumar, Abba El-Mustapha ne ya sanar da matakin yayin wani taron manema labarai a yau Asabar, inda ya ce an kuma dakatar da dukkan wuraren gudanar da bukukuwan wato 'event centers' har sai abin da hali ya yi. El-Mustapha ya ce wannan mataki da suka ɗauka wani ɓangare ne da hukumar ke yi na ƙarfafa ɗabi'u masu kyau tsakanin al'umma. "Wannan mataki da muka ɗauka yana cikin tsarin dokar hukumar mu wanda majalisar jiha ta yi wa garambawul da kuma gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanya wa hannu," in ji El-Mustapha. Ya ƙara da cewa dokokin sun bai wa hukumar tace finai-finai ta jihar Kano damar kula da kuma...
Laftanar Buba Hamza Kènan Da Aka Ķàšhè A Fagen Dàga A Jihar Borno Bayan Kwanaki Kadan Da Kara Masa Girma A Gidan Sojà

Laftanar Buba Hamza Kènan Da Aka Ķàšhè A Fagen Dàga A Jihar Borno Bayan Kwanaki Kadan Da Kara Masa Girma A Gidan Sojà

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Laftanar Buba Hamza Kènan Da Aka Ķàšhè A Fagen Dàga A Jihar Borno Bayan Kwanaki Kadan Da Kara Masa Girma A Gidan Sojà Allah Ya gafarta masa.
Gwamnatin Kano ta kama awaki da su ke cinye bishiyoyin da aka dasa a sabbin titunan da ake ginawa

Gwamnatin Kano ta kama awaki da su ke cinye bishiyoyin da aka dasa a sabbin titunan da ake ginawa

Duk Labarai
Gwamnatin Kano ta kama awaki da su ke cinye bishiyoyin da aka dasa a sabbin titunan da ake ginawa. Ma'aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi ta Jihar Kano ce ta kama wasu awaki da su ke cinye bishiyoyin da aka dasa don ƙawata sabbin titunan da ake yi a cikin birnin jihar. Kwamishinan ma'aikatar, Dr. Dahir M. Hashim ne ya baiyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a Kano, inda ya ce tuni aka kama wajin aka daure su a ofishin Ƴansanda na Zone 1. Ya zargi al'umma da sakin wani sakaka, inda ya ce gwamnati ba za ta lamunci hakan ba. "Mun samu rahotanni cewa wasu suna barin awaki suna yawo suna cin sababbin bishiyoyin da muka dasa. "Ina so jama'a su sani cewa wannan abu ne da ba za mu lamunta ba. A halin yanzu, mun kama wasu awaki suna cin bishiyoyin da aka dasa kuma mun ɗauresu a Zon...