Jarabawar JAMB: Jihohin Anambra da Legas ne suka fi yawan masu satar Jarabawar ta 2025
Rahoton da Hukumar JAMB data fitar ya bayyana cewa, jihohin Anambra da Legas ne suka fi yawan dalibai da ake zargi da aikata satar jarrabawar UTME na shekarar 2025, inda aka kama mutane 80 ta hannun 'yan sanda.
Shugaban JAMB, Farfesa Ishaq Oloyede, ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da aka gudanar a hedkwatar hukumar da ke Abuja, ranar Juma’a.
Ya ce an gano sababbin hanyoyin satar amsa, ciki har da canjin fasalin fuska da yatsun hannu tsakanin ɗalibai da masu yi musu jarrabawa a madadinsu, tare da hadin gwiwar wasu cibiyoyin CBT.
Anambra ce ke kan gaba da mutum 14 da ake zargi, inda 13 daga ciki ke fuskantar tuhuma kan amfani da wasu wajen rubuta musu jarrabawa, sannan guda ɗaya na da matsalar daidaito hoton wani da bayanan yatsa.
A jihar Legas, an kama mutum tara bi...







