Sunday, February 22
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Bani da tabbacin tsaron rayuwata, za’a iya kamani a tsare ba da son raina ba>>Sanata Natasha Akpoti ta koka

Bani da tabbacin tsaron rayuwata, za’a iya kamani a tsare ba da son raina ba>>Sanata Natasha Akpoti ta koka

Duk Labarai
Sanata Natasha Akpoti ta koka da cewa, tana cikin fargabar tsaro. Sanata Natasha ta bayyana bakane a majalisar dinkin Duniya inda aka yi zama na mata 'yan majalisa a Birnin New York City na kasar Amurka. Bayan data gabatar da korafi kan dakatar da ita da aka yi daga ayyukan majalisar Najeriya, Sanata Natasha Akpoti tace tana fargaba kan tsaron kanta. Tace za'a iya kamata a tsare ba bisa son ranta ba a birnin New York City na kasar Amurka inda tace kuma tana zargin Gwamnatin Najeriya da hannu game da hakan.
Da Duminsa: Kwanaki 2 kacal bayan komawar El-Rufai SDP, Rikicin cikin gida ya kunno kai a Jam’iyyar

Da Duminsa: Kwanaki 2 kacal bayan komawar El-Rufai SDP, Rikicin cikin gida ya kunno kai a Jam’iyyar

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa kwanaki biyu kacal da komawar tsohon gwamnan jihar Kaduna Malam Nasiru Ahmad El-Rufai Jam'iyyar SDP, rikcin cikin gida ya kunno kai a cikin Jam'iyyar. Rahoton yace Sakataren Jam'iyyar, Olu Agunloye ne ya nemi daukin shugaban 'yansandan Najeriya, IGP Kayode Egbetokun inda yace ana shirin tsigeshi da karfin tsiya daga kan kujerarsa. Rahoton yace wasu 'yan Jam'iyyar dake goyon bayan tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad da ya koma Jam'iyyar ne ke neman tsige Olu Agunloye daga mukaminsa. Sakataren ya kuma bayyana cewa, wanine yayi amfani da takardar karya yake masa barazanar saukeshi daga kujerar sa. Dama dai tuni rade-radi ya fara yaduwa inda ake zargin cewa, Jam'iyya me mulki, APC ko Gwamnatin Tinubu ta dasa munafukai a cikin Jam'iyyar.
Kalli Bidiyo, Kwana daya da komawar El-Rufai Jam’iyyar SDP, an ga su sanata Akpabio da Barau na ganawa da shuwagabannin Jam’iyyar inda hakan yasa wasu ke ganin Gwamnatin Tinubu ta dasa munafukai a cikin Jam’iyyar

Kalli Bidiyo, Kwana daya da komawar El-Rufai Jam’iyyar SDP, an ga su sanata Akpabio da Barau na ganawa da shuwagabannin Jam’iyyar inda hakan yasa wasu ke ganin Gwamnatin Tinubu ta dasa munafukai a cikin Jam’iyyar

Duk Labarai
Kwana daya bayan da tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bar Jam'iyyar APC zuwa SDP, wani Bidiyo ya bayyana inda aka hango Sanata Godswill Akpabio da Sanata Barau Jibril suna ganawa da shuwagabannin Jam'iyyar. Saidai hutudole bai iya tantance bidiyon sabone ko tsoho ne ba. https://www.tiktok.com/@shehugabam/video/7430650225653533958?_t=ZM-8ubaHaXQi5V&_r=1 Saidai ko da bidiyon tsoho ne hakan na alamta cewa akwai yiyuwar wata kullalliyar Alaka tsakanin Jam'iyyar APC da SDP. Dama dai tuni wasu ke dari-darin akwai yiyuwar an saka munafukai cikin Jam'iyyar SDP daga bangaren gwamnati dan su lalata tafiyar 'yan Adawa.
Sanata Natasha Akpoti ta dauko dala ba Gammo inda ta kai karar Sanata Godswill Akpabio majalisar Dinkin Duniya acan ma ta masa tonon silili da terere

Sanata Natasha Akpoti ta dauko dala ba Gammo inda ta kai karar Sanata Godswill Akpabio majalisar Dinkin Duniya acan ma ta masa tonon silili da terere

Duk Labarai
Sanata Natasha Akpoti da majalisar dattijai ta dakatar saboda zargin karya dokar majalisar ga dukkan alamu bata hakura ba. A wani taron mata 'yan majalisa na Duniya da aka yi a majalisar Dinkin Duniya dake birnin New York na kasar Amurka, Sanata Natasha Akpoti a can ma ta taso da maganar dakatar da ita. Tace an mata rashin adalci da take hakkinta, inda tace akwai yiyuwar ma a tsareta a birnin New York. Ta bayyana cewa, tana fargabar tana cikin matsalar tsaro.
Ku sake Tunani, Musulunci bai farlanta kulle makarantu ba a lokacin azumin watan Ramadana>>Ministar Ilimi, Suwaiba Ahmad ta jawo hankalin Gwamnonin Arewa

Ku sake Tunani, Musulunci bai farlanta kulle makarantu ba a lokacin azumin watan Ramadana>>Ministar Ilimi, Suwaiba Ahmad ta jawo hankalin Gwamnonin Arewa

Duk Labarai
Karamar Ministar Ilimi, Suwaiba Ahmad ta jawo hankalin Gwamnonin Arewa da cewa, su sake tunani kan kulle makarantu da suka yi saboda zuwan Azumin watan Ramadana. Tace musulunci bai farlanta kulle makarantu ba a yayin azumin watan Ramadan. Ta bayyana hakane a yayin wata hira da aka yi da ita a gidan talabijin na ChannelsTV. Jihohin Kebbi, Bauchi, Katsina da Kano ne suka kulle Makarantu saboda zuwan Azumin watan Ramadana inda suka ce sun bayar da wannan hutu ne dan baiwa dalibai damar Azumtar watan da yin Ibada yanda ya kamata saidai hakan ya jawo cece-kuce. A ci gaba da jawabinta, Minista Suwaiba ta bayyana cewa, A zamanin Annabi Muhammad (Sallallahu Alaihi Wasallam) har yaki yaje a cikin watan Ramadana dan haka Azumi bai hana mutum gudanar da ayyukansa na yau da kullun. Ta...
Labari Me Dadi: Majalisar Tarayya tace hukumar sadarwa ta NCC ta gaggauta toshe duk wani shafin dake nuna bidiyo da hotuna na tsìraìcì watau Blù Fìm

Labari Me Dadi: Majalisar Tarayya tace hukumar sadarwa ta NCC ta gaggauta toshe duk wani shafin dake nuna bidiyo da hotuna na tsìraìcì watau Blù Fìm

Duk Labarai
Majalisar tarayya ta amince da kudirin dokar toshe duk wani shafin yanar gizo dake nuna Bidiyo da hotunan tsiraici wanda aka fi sani da Blù fìm. Majalisar tace hukumar sadarwa ta kasa,NCC ta baiwa duka kamfanonin dake samar da Internet a Najeriya umarnin toshe shafukan dake nuna batsa nan take. Dan majalisa daga jihar Katsina, Dalhatu Tafoki ne ya kai kudirin dokar majalisar wanda kuma sauran 'yan majalisar suka amince dashi.
El-Rufai baya mutunta watan Ramadan, Tunda watan ya kama, bashi da aiki sai zagi da sukar shugaban kasa, Bola Ahmad>>Inji Reno Omokri

El-Rufai baya mutunta watan Ramadan, Tunda watan ya kama, bashi da aiki sai zagi da sukar shugaban kasa, Bola Ahmad>>Inji Reno Omokri

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Tsohon hadimin shugaban kasa, Reno Omokri ya soki tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai bayan da ya bar APC ya koma Jam'iyyar SDP. A wani bayani da ya wallafa a shafinsa na X, Reno Omokri ya zargi El-Rufai da rashin girmama watan Ramadana me Alfarma. Ya bayyana cewa tun da aka kama watan Azumin Ramadana El-Rufai bai yi amfani da shafukansa na sada zumunta ba wajan fadakar da Musulmai kan watan ba, maimakon hakan sai zagi da sukar shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu. ...
Kasuwanci Miliyan 7.2 ne aka kulle suka rushe a karkashin mulkin Tinubu saboda matsin rayuwa

Kasuwanci Miliyan 7.2 ne aka kulle suka rushe a karkashin mulkin Tinubu saboda matsin rayuwa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, daga shekarar 2023 zuwa 2024 kasuwanci miliyan 7.2 aka kulle suka ruguje saboda rashin tabbas na tattalin arzikin Najeriya. Shugaban hukumar bincike akan tattalin arziki ta kasa, NESG me suna Dr. Segun Omisakin ne ya bayyana hakan. Ya kara da cewa, hakan ya jawowa Najeriya asarar Naira Tiriliyan 94. Ya bayyana hakane a yayin kaddamar da rahoto akan kamfanoni inda yace kaso 30 cikin 100 na kananan kasuwancin da ake dasu a Najeriya sun kulle. Yace Najeriya na da jimullar kananan kasuwanci miliyan 24 kuma a yanzu gida Miliyan 7.2 daga cikinsu sun kulle. Yace rashin tabbas na tattalin arziki da hauhawar farashin kayan masarufi da kashe kudi da yawa wajan gudanar da ayyukan su ne ya jawo hakan.
Mahaukaciyace kawai da bata da rabon arziki dana zaice yana son dirka mata cikin shege amma tace bata yadda ba>>Inji Mahaifin me kudin Duniya Elon Musk dake da ‘ya’ya 13 wanda kusan duk ba ta hanyar aure ya samesu ba

Mahaukaciyace kawai da bata da rabon arziki dana zaice yana son dirka mata cikin shege amma tace bata yadda ba>>Inji Mahaifin me kudin Duniya Elon Musk dake da ‘ya’ya 13 wanda kusan duk ba ta hanyar aure ya samesu ba

Duk Labarai
Mahaifin me kudin Duniya, Elon Musk watau Errol Musk ya kare dansa bayan da aka tambayi ra'ayinsa game da da na 13 da dansa ya haifa da wata shahararriyar me amfani da kafafen sadarwa me suna Ashley St. Clair. Mahaifin na Elon Musk yace ai mahaukaciya ce kawai ba zata amincewa dansa ya dirka mata cikin shege ba. Elon musk dai yana da jimullar 'ya'yaye 14 wanda ya haifa tare da mata 4. Shima dai mahaifin na Elon Musk, Errol 'ya'yansa 7 2 daga cikinsu ya haifesu ne tare da diyar matarsa, watau Agola.