Friday, February 20
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Ku shirya zamu kara kudin wutar lantarki>>Gwamnatin Tarayya ta gayawa ‘yan Najeriya

Ku shirya zamu kara kudin wutar lantarki>>Gwamnatin Tarayya ta gayawa ‘yan Najeriya

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya tace tana shirye-shieryen kara kudin wutar lantarki nan da wasu watanni kadan masu zuwa. Me baiwa shugaban kasa shawara akan harkar makamashi, Olu Verheijen ne ya bayyana hakan a yayin ganawa da kafar Bloomberg a birnin Darussalam na kasar Tanzania. A shekarar data gabata dai, an kara kudin wutar nunki 3 ga wadanda suke kan tsarin Band A na wutar.
Kalli Bidiyo yanda ‘yan Bìndìgà da suka tuba suka koma zikiri da salatin Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam)

Kalli Bidiyo yanda ‘yan Bìndìgà da suka tuba suka koma zikiri da salatin Annabi(Sallallahu Alaihi Wasallam)

Duk Labarai
Shugaban 'yan Bindiga me suna Kachalla Bugaje ya bayyana a baya cewa, ya tuba daga yin garkuwa da mutane inda yace mutane guda 50 da yayi garkuwa dasu, ya sakesu ba tare da karbar kudin fansa ba. Bayan nan ne kuma aka ganshi yana jagorantar mayakansa suna zikiri da salatin Annabi. Bugaje ya bayyana nadama sosai bisa abinda ya aikata tare da jawo hankalin sauran shuwagabannin 'yan Bindiga da su ajiye makamansu su koma ga Allah. Ganin bidiyon har yanzu da makamai a hannunsu shi da yaransa yasa da yawa suke zargin cewa ba da gaske yake maganar ajiye makaman ya daina yaki ba. Kalli Bidiyon anan
Subhanallahi kalli Bidiyo: Duk da kkashe na farko da aka yi, an kara samun wasu sun yi bikin kona Qur’ani a kasar Ingila

Subhanallahi kalli Bidiyo: Duk da kkashe na farko da aka yi, an kara samun wasu sun yi bikin kona Qur’ani a kasar Ingila

Duk Labarai
Biyo bayan kashe Salwan Momika da ya kona Qur'ani a bainar jama'a, an sake samun wasu da yawa sun sake kona Qur'anin inda suka rika saka hotunan wannan lamari a shafukansu na sada zumunta. Wani me sunan DigitalVagrant a kafafen sada zumunta ya bayyana cewa, zai maye gurbin Salwan Momika inda ya fita fili ya kona Qur'ani a Manchester dake kasar Ingila. Tuni dai mahukunta a birnin suka kamashi saboda yunkurin kawo fitina. Akwai da yawa da ake samu suna cin zarafin addinin Musulunci ta hanyoyi daban-daban dan tsananin nuna kiyayya.
Bana munafurci a siyasa>>El-Rufai

Bana munafurci a siyasa>>El-Rufai

Duk Labarai
Tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, baya munafurci a siyasa. El-Rufai bayyana hakane a shafinsa na sada zumunta inda yake martani ga wani da yace ya karanta littafinsa na accident civil servant kuma ya fahimci cewa, El-Rufai bai iya munafurci ba. El-Rufai ya tabbatar da hakan inda yace bai iya wasan kwaikwayo irin na 'yan film ba.
Da Duminsa: Matatar Man fetur din Dangote ta rage farashin man

Da Duminsa: Matatar Man fetur din Dangote ta rage farashin man

Duk Labarai
A wani yanayi da zai iya kawo sauki ga matsin rayuwa musamman ga talakawan Najeriya, Matatar man Dangote ta rage farashin litar mai da ake dauka a Depot daga Naira 950 zuwa Naira 890 akan kowace lita. Matatar man ta ce ta rage kudinne saboda saukar farashin danyen man fetur a Kasuwar Duniya. Me magana da yawun matatar man fetur din, Anthony Chiejina ne ya bayyana haka inda yace kamar yanda a ranar 19 ga watan Janairu da ya gabata suka kara farashin litar man fetur din saboda tashin farashin danyen man fetur din hakanan a yanzu tunda farashi ya sauka shine suma suka rage farashin. Matatar tace wannan rage farashin zai kawo saukin hauhawar farashin kayan masarufi da saukin rayuwa a tsakanin 'yan Najeriya.
Kalli Yadda Gwamna Zulum Ke Rushe Gidajen Talakawan Jihar Bornon

Kalli Yadda Gwamna Zulum Ke Rushe Gidajen Talakawan Jihar Bornon

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Abunda Gwamna Zulum yake yi wa talakawan jihar sa na rushe gidajen su sam bai dace ba koda kuwa local dillalai ne suka cuce su na saida musu filayen da bana su ba. Na tabbata akwai wadanda da yawa ba su da masaniyar yadda abun yake kuma hakan zai iya zama silar talaucewar mutane da yawa. Ya kamata Gwamnatin jihar ta kama dukkannin dillalan da suka cuci al'umma domin su biya wa 'yanda suka saidawa wurin hakkokinsu, haka zalika Gwamna Zulum shima ya ragewa wa 'yanda hakan ya shafa ...
APC ta kori ministan Buhari, Aregbesola

APC ta kori ministan Buhari, Aregbesola

Duk Labarai
Jam'iyyar APC ta kori tsohon gwamnan jihar Osun kuma tsohon ministan cikin gida Rauf Aregbesola, a kan zarginsa da yin abubuwan da suka saba wa jam'iyyar. Reshen jam'iyyar na jihar ta Osun shi ne ya tabbatar da korar a wata wasika da ya fitar. Aregbesola, wanda ya kasance ministan cikin gida a lokacin gwamnatin da ta gabata, ya jagoranci wani bangare na jam'iyyar ta APC a jihar, bangaren da aka yi wa lakabi da “The Osun Progressives,” wanda kuma daga baya aka sake masa lakabi da ''Omoluabi Caucus''. Korar tsohon gwamnan ta biyo bayan taron da bangaren da yake jagoranta ne wato Omoluabi Caucus, ya gudanar kuma karkashin jagorancin, Aregbesola. A lokacin taron bangaren ya sanar da aniyarsa ta ficewa daga APC,inda ya bayar da hujjar raguwar tasirin jam'iyyar a jihar.
Shugaban Amurka, Donald Trump ya haramta bukukuwan ranar ‘yan Luwadi da Madigo da na tunawa da kkisan da kawa Yahudawa

Shugaban Amurka, Donald Trump ya haramta bukukuwan ranar ‘yan Luwadi da Madigo da na tunawa da kkisan da kawa Yahudawa

Duk Labarai
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya yi sabuwar doka data hana hukumar sojoji ta kasar shiga bukukuwan watan ranar 'yan Luwadi da Madigo da ranar Tunawa da kisan da akawa Yahudawa watau Holocaust. Sauran bukukuwan da aka dakatar sun hada dana watan tunawa da tarihin Bakaken fata, dana ranar tunawa da kisan Martin Luther king, da watan tarihin mata da sauransu. Hukumar tsaro ta kasar Pentagon ta bayyana cewa, ta dauki matakan ne dan bin umarnin shugaban kasar na dakatar a tsare-tsaren daidaito na jinsi.
Kalli bidiyon Soja yana kuka da bankwana na karshe kamin a kkasheshi a fagen yaki

Kalli bidiyon Soja yana kuka da bankwana na karshe kamin a kkasheshi a fagen yaki

Duk Labarai
{"remix_data":[],"remix_entry_point":"challenges","source_tags":[],"origin":"unknown","total_draw_time":0,"total_draw_actions":0,"layers_used":0,"brushes_used":0,"photos_added":0,"total_editor_actions":{},"tools_used":{},"is_sticker":false,"edited_since_last_sticker_save":false,"containsFTESticker":false} Bidiyon wani sojan kasar Congo ya dauki hankula a kafafen sada zumunta inda aka ganshi yana kuka yana neman a taimakawa iyalansa a basu hakkinshi bayan ya mutu. Kalli Bidiyon anan https://www.youtube.com/watch?v=ACuySd7lNTM?si=XjLZLSDaPegjizRY Da alama sojan yana fagen daga ne dan har harbin bindiga da aka masa sai da ya nuna.