Monday, December 15
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Tarewar Ƙaramin Ministan Tsaro Jihar Sokoto Shin Ko Kwalliya Ta Fara Biyan Kuɗin Sabulu Cikin Yaƙi Da Ƴaɲ Tá’aḍdą ?

Tarewar Ƙaramin Ministan Tsaro Jihar Sokoto Shin Ko Kwalliya Ta Fara Biyan Kuɗin Sabulu Cikin Yaƙi Da Ƴaɲ Tá’aḍdą ?

Duk Labarai
Tarewar Ƙaramin Ministan Tsaro Jihar Sokoto Shin Ko Kwalliya Ta Fara Biyan Kuɗin Sabulu Cikin Yaƙi Da Ƴaɲ Tá'aḍdą ? Biyo bayan tarewar ƙaramin ministan tsaro, Dakta Bello Muhammad Matawalle da manyan hafsoshin sojin Najeriya Jihar Sokoto domin fatattakar ƴąɲ bîɲḍiĝa da masu gârkűwa da mutane kamar yadda shugaban ƙasa Tinubu ya umarce su, wata majiya tace tuni kwalliya ta fara biyan kuɗin sabulu kan yâƙíɲda suke da ƴąɲ ta'ąddáɲ Wata majiya ta ce, ana can ana gwąfzáwa a tsakaniɲ ƴąɲ bîɲdiģa da sojojin inda kuma ƴâɲ bîɲdiĝa da dama suke tsréwa wasu kuma suke mụtųwa sanadiyyar lugúdéɲ wuta ta sama da ƙasa da dakarun sojòji suke musu bisa haɗin gwiwar rundunonin tsaro daga Jihohin Katsina, Sokoto, da Kaduna. Majiyoyi sun tabbatar da cewa duk da yadda wasu manya ba sa son a yáƙi ƴañ ta'...
Karin farashin man fetur zai nunkawa ‘yan Najeriya wahalar da suke ciki>>Kungiyar Yarbawa ta Afenifere ta gayawa Tinubu

Karin farashin man fetur zai nunkawa ‘yan Najeriya wahalar da suke ciki>>Kungiyar Yarbawa ta Afenifere ta gayawa Tinubu

Duk Labarai
Kungiyar kishin Yarbawa ta Afenifere ta koka kan karin farashin man fetur da kamfanin mai na kasa,NNPCL yayi. Kamfanin NNPCL ya kara farashin man fetur din daga Naira 617 zuwa Naira 897 akan kowace lita. Kakakin Afenifere Mr Jare Ajayi yace ta yaya kamfanin na NNPCL da bai dade da cewar ya samu riba ba amma a yanzu zai ce wai ana binsa bashi. Kungiyar tace tana baiwa shugaban kasar shawarar da ya yiwa NNPCL magana a maida man farashinsa na baya idan kuwa ba haka ba,wahalar da za'a shiga zata shafe duk wani ci gaban da aka samu a karkashin gwamnatinsa.
Dan kwallon Najeriya, Ademola Lookman ya shiga jerin wanda zasu iya lashe kyautar Ballon D’ Or

Dan kwallon Najeriya, Ademola Lookman ya shiga jerin wanda zasu iya lashe kyautar Ballon D’ Or

Duk Labarai
Dan kwallon Najeriya, Ademola Lookman ya shiga jerin 'yan wasan da zasu iya lashe kyautar Ballon D' Or ta shekarar 2014. Lookman ya shiga jerin manyan 'yan kwallon Duniya irin su Bellingham, Kylian Mbappe da Vinicius Jr wanda ke gaba-gaba wajan lashe kyautar. Dan wasan yayi kokari sosai a gasar Serie A inda ya ciwa kungiyarsa ta Atalanta kwallaye 3 a wasan da suka buga da Bayer Leverkusen a gasar Europa. Hakanan a gasar AFCON,ya ciwa Najeriya kwallaye 3. A baya dai an yi rade-radin zai koma kungiyoyin Arsenal da PSG saidai a karshe be bar kungiyar tasa ba.
‘Matatar mu tana iya samar da man fetur fiye da abin da ake bukata a Najeriya’

‘Matatar mu tana iya samar da man fetur fiye da abin da ake bukata a Najeriya’

Duk Labarai
Shugaban gamayyar kamfanonin Dangote wanda ke da matatar mai ta Dangote Refinery ya ce matatar ta shiya tsaf domin fara sayar da tataccen man fétur da disel har ma da kanazir ga gidajen man kasar. Alhaji Aliko Dangote ya shaidawa BBC matatar tana iya samar da fiye da man da ake bukata a kasar. ''Inda mu ke ciki yanzu mun soma yin mai, muna jiran su zo su soma karba saboda abinda aka yi a sabon tsari shi ne za su ba mu man fetur da za mu sarafa wanda za mu basu'', in ji shi. Ya kara da cewa kamfanin mai na kasa NNPCL ne ke da alhakin saka farashin litar man da matatar tasa za ta fitar: ''Wajan saka kudin mai ba a hannunmu yakeba, a hanun NNPC yake ,kawai abinda zan iya tabbatar cewa a yanzu muna da man fetur da Kananzir da disel, duk wadannan wadanda za mu iya ba wa Najeriya fiy...
Ji yanda wani me Adaidaita Sahu ya kashe mahaifiyarsa ya kuma yanke wasu sassan jikin dansa dan yin tsafi

Ji yanda wani me Adaidaita Sahu ya kashe mahaifiyarsa ya kuma yanke wasu sassan jikin dansa dan yin tsafi

Duk Labarai
Wani me adaidaita Sahi/Keke Napep ya kashe mahaifiyarsa sannan kuma ya yanke wasu sassan jikin dansa dan yin tsafi. Mahaifiyar tasa ta ga ya yanki wasu sassan jikin dansa dan yin tsafi inda ta kaiwa dan nasa dauki anan ne a kokarin hanashi aikata wannan laifi ya kashe mahaifiyar tasa. Ya tsere amma alhaki sai ya fada cikin wari rami yayin da yake gudu. Sunan mutumin Amadi Alozie kuma lamarin ya farune a jihar Obingwa, karamar Obingwa a wani yanki da ake kira da Umudosi,kamar yanda jaridar Vanguard ta ruwaito. Tuni dai aka garzaya da dan nasa zuwa asibiti.
Kamfanin mai na kasa,NNPCL ya dakata da sayarwa da ‘yan kasuwa da man fetur

Kamfanin mai na kasa,NNPCL ya dakata da sayarwa da ‘yan kasuwa da man fetur

Duk Labarai
Kamfanin man fetur na kasa,NNPCL ya dakatar da sayarwa da 'yan kasuwar man fetur karkashin kungiyar IPMAN da mai. Hakan na zuwane bayan da kamfanin man ya kara farashin man fetur din a gidajen man su zuwa akalla Farashin Naira 855 har zuwa sama. Wakilin kungiyar na IPMAN, Hammed Fashola ya bayyana rashin jin dadi kan lamarin inda yace aun biya kudin sayen man fetur din amma gwamnati ta dakatar da komai. Ya bayyana cewa basu dan dalilin yin hakan ba dan kuwa zuwa yanzu NNPCL bata gaya musu me ya kawo dakatar da sayar musu da man fetur din ba.
Gwamnatin tarayya ta saka dokar ta baci a Onne saboda shigo da miyagun makamai Najeriya

Gwamnatin tarayya ta saka dokar ta baci a Onne saboda shigo da miyagun makamai Najeriya

Duk Labarai
Hukumomi a Najeriya sun saka dokar ta baci akan tashar ruwa dake onne jihar Rivers. Hakan ya biyo bayan jiragen ruwa da akai ta kamawa suna dauke da miyagun makamai ne da ake shirin shigowa dasu Najeriya. Lamarin yayi kamari ta yanda an baza jami'an tsaro a tashar jirgin ruwan wanda kuma duk kayan da aka kawo sai an bincikasu yanda ya kamata. Shugaban hukumar Kwastam, Bashir Adeniyi, ne ya bayyana haka yayin ganawa da manema labarai inda yace hakan na barazana ga tsaron Najeriya.