Wannan wani ne da yace an kunna waqar Yabon Inyass a wani gidan giya dake kusa da su.
Ya walafa Bidiyon a shafinsa inda abin ya bashi mamaki.
https://www.tiktok.com/@abdullhd20/video/7592366405882891528?_t=ZS-92tav8zInqr&_r=1
Rahotanni sun bayyana cewa, Dangote ya janye zargin da yakewa shugaban Hukumar NMDPRA, Alhaji Farouk Ahmad a gaban Hukumar ICPC.
Dangoten ya janye zargin da yake wa Ahmad ne inda yace ya kashe dala Miliyan $7 wajan biyawa 'ya'yansa kudin makaranta a kasar Switzerland.
Wata Majiya tace Dangoten ya janye zarginne bayan da aka bukaci ya je da kansa ba aiken Lauya ba ya gabatar da hujjoji a gaban ICPC kan wannan zargin da yake.
Hakanan Wata Hujja da aka samu game da janye wannan korafi da Dangoten yayi shine EFCC ta fara bincike kan lamarin.
Saidai ICPC tace duk da wannan Janyewar da Dangote yayi ba zata yi watsi da binciken da takewa Ahmad ba, tace ta ma aika da bukatar bincike makarantar da ake zargin Ahmad din ya kai 'ya'yansa.
Ahmad dai tun tuni ya sauka daga kan mukaminsa ...
Tsohon shugaban kasa, Muhammadu Buhari ya nemi wadanda zai baiwa mukaman Siyasa masu gaskiya da kishin Najeriya irinsa amma ya kasa samu.
Hadiminsa, Malam Bashir Ahmad ne ya bayyana hakan a wata hira da Ali Jita yayi dashi.
Yace Buhari ya gaya musu cewa a tsawon lokacin da ya dauka yana kokarin neman Mulki, ya manta bai nemi mutane nagartattu ba da zai yi aiki dasu.
Yace sai bayan da ya ci zabe, ya je gida ya kwanta amma Bacci ya ki zuwa, yace sai ya tuna wata ma'aikata da ke da matsala, sai yayi tunanin wanene zai dakko me irin ra'ayinsa ya baiwa wannan ma'aikata amma sai ya kasa samun ko da mutum daya.
Yace a wannan lokacinne yasan cewa bai samarwa kansa abokan aiki ba.
https://www.tiktok.com/@realalijita/video/7592575748817440008?_t=ZS-92tY3O7k8DA&_r=1
Wasu 'yan Kudu na kowa bayan ganin shanu a Cibiyar Kasuwanci ta Duniya dake Abuja.
Sun bayyana cewa hakan abin kunyane ga Najeriya.
https://twitter.com/i/status/2008986691495981342
Tsohon Shugaban kasa, Olusegun Obasanjo ya bayyana cewa, a shekarar 1983, manyan sojoji sun sameshi suka ce zasu yiwa shugaban kasa a wancan lokacin, Shehu Shagari Juyin Mulki dan shi Obasanjon ya zama shugaban kasa.
Saidai Obasanjon yace musu baya so.
Yace dalilinsa shine su suka Kafa Dimokradiyya diyya a Najeriya dan haka ba zai zama cikin wanda zasu rusata ba.
Hakanan shima tsohon shugaban kasar Soji, Janar Ibrahim Badamasi ya tabbatar da wannan labari na Obasanjo.
Rahotanni sun bayyana cewa, Hukumar 'yansandan Farin kaya ta DSS na shirin sake kama tsohon Ministan shari'a, Abubakar Malami da zarar an bayar da belinsa.
Malami ne ya bayyana hakan ta bakin me magana da yawunsa, Muhammed Bello Doka.
Yace DSS na shirin yi masa wannan abu da ya kira take hakinsa ne bayan da kotu ta bayar da belinsa.
Malami yayi zargin cewa, DSS sun dana tarko akansa suna jiran a bayar da belinsa su sake chafkeshi.
Wata majiya daga Kano tace ainahin abinda ya kawo rashin jituwar Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf da shugaban Tafiyar Kwankwasiyya, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso shine.
Kwankwason ya so saka 'yan majalisar jihar Kano su tsige Abba.
Wannan banai na ta yawo ne a kafafen sada zumunta inda a wata majiyar kuma aka rika ruwaito cewa, Kwankwaso baya son Abba ya sake tsayawa takarar Gwamnan Kano ne a shekarar 2027 inda yake son kawo wani dan takara na daban.
https://twitter.com/i/status/2008888990062223473
https://twitter.com/i/status/2008973814240055306
Tsohon Mataimakin Peter Obi a zaben shugaban kasa na shekarar 2023, Yusuf Datti Baba Ahmad ya bayyana cewa, zai fito takarar shugaban kasa zaben shekarar 2027 a jam'iyyar Labour Party.
Ya bayyana cewa idan ya zama shugaban kasa, a watanni na farko zai tabbatar ya linka Albashin jami'an tsaro da sau 4.
https://twitter.com/i/status/2008929943150071954
Kotun tarayya dake da zama a Abuja ta amincewa hukumar EFCC ta ci gaba da rike kadarorin tsohon Ministan shari'a, Abubakar Malami.
Kotun tace EFCC ta rike kadarorin guda 57 na wucin gadi kamin a amince a kwacesu na dindindin.
Hakanan Kotun ta bayar da belin Malami da dansa da matarsa.
Hakanan a zaman kotun, Mai Shari'a, Justice Emeka Nwite ya Gargadi Lauyan Abubakar Malami cewa kada ya sake yace zai nemi wata Alfarma a wajansa.
Yace ba zai lamunce a bata masa suna ba kuma duk sanayyarsa da mutum idan aka zo wajan aiki zai nuna ba sani ba sabo.
Kungiyar 'yan kwallon Najeriya ta Super Eagles da masu horas dasu sun ce ba zasu je wasan da zasu buga da Algeria ba idan ba'a biyasu hakkokinsu ba.
Kungiyar ta bayyana cewa akwai alkawuran kudaden da aka musu idan suka yi nasara a wasanni da kasashen Tanzania, Tunisia, Uganda, da Mozambique amma ba a cika musu wadannan alkawuran ba.
Kungiyar tace ba zata ke garin Marrakech ba ranar Alhamis dan yin Atisayen wasan da zasu buga da kungiyar kasar Algeria ba idan ba'a biyasu ba.
Najeriya dai zata yi wasan Quarter finals da kasar Algeria.