Friday, January 23
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Kalli Bidiyon: Shima Tauraron fina-finan Hausa, Musa Mai Sana’a ya samu gagarumar kyauta daga mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima

Kalli Bidiyon: Shima Tauraron fina-finan Hausa, Musa Mai Sana’a ya samu gagarumar kyauta daga mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima

Duk Labarai
Tauraron fina-finan Hausa, Musa Mai Sana'a ya bayyana cewa mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya masa kyauta ta hannun Ali Nuhu. Ya bayyana hakane a wani Bidiyo da ya fito yakewa Ali Nuhu da mataimakin shugaban kasar godiya. Saidai be bayyana irin kyautar da aka masa ba https://www.tiktok.com/@maisanaakanotv/video/7596653199013022988?_t=ZS-93BDfn9OYTI&_r=1 A baya dai Musa Mai Sana'a ya fito yace ya kashe Miliyoyin Naira wajan yiwa Gwamnatin Tinubu hidima amma ba'a bashi komai ba. Hakanan Kashim Shettima yawa Adam A. Zango babbar kyauta ta mota.
Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle zai aurar da ‘ya’yansa 9

Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle zai aurar da ‘ya’yansa 9

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle zai aurar da 'ya'yansa maza da mata su 9. Katin gayyatar auren ya watsu sosai a kafafen sada zumunta inda aka ga cewa za'a yishi ne ranar 6 ga watan Fabrairu a babban masallacin Juma'a dake Abuja. Sunayen 'ya'yan nasa sune kamar haka, Ibrahim, Suraj, Safiya, Maryam, Aisha, Fahad, Muh’d, Nana Firdausi, and Farida. Kakakin jam'iyyar APC na jihar Zamfara, Yusuf Idris, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Kalli Bidiyon: Ku sakani a addu’a na karbi Addinin Musulunci >>Inji Wannan matar

Kalli Bidiyon: Ku sakani a addu’a na karbi Addinin Musulunci >>Inji Wannan matar

Duk Labarai
Wannan baiwar Allahn ta bayyana cewa ta karbi Addinin Musulunci inda ta nemi a sakata a addu'a. An ganta da litattafan Addinin Musulunci a Bidiyon data saki Kalli Bidiyon anan https://www.tiktok.com/@rejoiceallahnan0/video/7596051470563216657?_t=ZS-939pXUKkuDw&_r=1 https://www.tiktok.com/@rejoiceallahnan0/video/7596051470563216657?_t=ZS-939pXUKkuDw&_r=1
Kalli Bidiyon ‘yan kwallon Najeriya Super Eagles na maganar cewa ba’a biyasu hakokinsu ba kamin wasan da suka buga da Morocco

Kalli Bidiyon ‘yan kwallon Najeriya Super Eagles na maganar cewa ba’a biyasu hakokinsu ba kamin wasan da suka buga da Morocco

Duk Labarai
Wani sabon Bidiyon 'yan kwallon Najeriya, Super Eagles ya bayyana inda aka ji suna tattauna cewa ba'a biyasu hakkokinsu ba. An dauki Bidiyon ne kamin wasansu da Morocco wanda Moroccon ta fitar dasu a wasan Penalty. Lamarin dai ya jawo cece-kuce sosai inda ake dorawa hukumar NFF alhakin hakan. https://twitter.com/i/status/2012467439267717398