Thursday, April 23
Shadow

Author: Bashir Ahmed

‘Yan Arewa bayin Allah ruwa Kwata suke sha, sai da Peter Obi ya tausaya ya je ya gina musu fanfon burtsatse sannan suke samun ruwan sha me kyau>>Inji Wannan masoyiyar Peter Obin

‘Yan Arewa bayin Allah ruwa Kwata suke sha, sai da Peter Obi ya tausaya ya je ya gina musu fanfon burtsatse sannan suke samun ruwan sha me kyau>>Inji Wannan masoyiyar Peter Obin

Duk Labarai
Wata masoyiyar Peter Obi ta dauki hankula bayan data bayyana cewa kamin shigar Peter Obi Arewa, Mutanen Arewa, Ruwan Kwata suke sha. Tace zuwan Peter Obi ne har ya ginawa 'yan Arewa fanfon Burtsatse. Tace abin ban tausai, bata taba tunanin akwai mutane irinta masu shan ruwan kwata ba. https://twitter.com/i/status/2044554314715111524
Nafiu Bala ya fara bin dattawan Arewa dan su sulhuntashi dasu Atiku

Nafiu Bala ya fara bin dattawan Arewa dan su sulhuntashi dasu Atiku

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Nafiu Bala Gombe ya fara bin dattawan Arewa akan su sulhuntashi dasu Atiku. Hakannna zuwane bayan da Su Atikun suka ce sun koreshi daga jam'iyyar ADC sannan rahotanni suka bayyana cewa, masu daukar nauyinsa sun yi watsi dashi. Rahoton yace saidai su Atikun sun ce ai shi yanzu ba dan ADC bane kuma basu tare da makaryaci wanda baya cika Alkawari. https://twitter.com/i/status/2044662504195014749
Da Duminsa:Ranar Zabe ko sakamakon zabe ba zan batawa kaina Lokaci in dubaba saboda nasan nine zan yi nasara, A lokacin kana da wasu tsirarin Gwamnoni tare da kai na yi nasara akanka ballantana yanzu da baka da Gwamna ko daya tare dakai>>Tinubu ya gayawa Atiku

Da Duminsa:Ranar Zabe ko sakamakon zabe ba zan batawa kaina Lokaci in dubaba saboda nasan nine zan yi nasara, A lokacin kana da wasu tsirarin Gwamnoni tare da kai na yi nasara akanka ballantana yanzu da baka da Gwamna ko daya tare dakai>>Tinubu ya gayawa Atiku

Duk Labarai
Fadar shugaban kasa tawa Tsohon Ministan shugaban kasa, Atiku Abubakar zazzafan martani game da kalamansa na cewa shine zai yi nasara a zaben 2027. A martanin da me baiwa shugaban kasa shawara kan harkar sadarwa, Daniel Bwala ya baiwa Tinubu, Yace a zaben 2023 ma lokacin Atiku nada wasu tsirarin Gwamnoni a bayansa an yi nasara akansa. Ballantana yanzu da bashi da gwamna ko guda daya. Yace dan haka yasan Shugaba Tinubu ba zai ma bata lokacinsa ya duba sakamakon zabe ba ranar zabe dan yasan shine zai yi nasara. https://twitter.com/i/status/2044540151842415010
Allah me Iko:Kalli Bidiyon yanda dandazon kudan zuma ya mamaye wasu sassa na kasar Israyla

Allah me Iko:Kalli Bidiyon yanda dandazon kudan zuma ya mamaye wasu sassa na kasar Israyla

Duk Labarai
Rahotanni daga kasar Yahudawan Israyla na cewa wasu dandazon kudan zuma sun bayyana inda aka ga sun mamaye wasu sassa na kasar. Bidiyon faruwar lamarin ya mamayr kafafen sadarwa inda mutane ke ta muhawara akai. Wasu dai sun rika danganta abin da cewa, kamun Allah ne, wasu kuma suka ce sakayya ce. https://twitter.com/i/status/2044431481162875143
Da Duminsa: Ministan Tsaro, Christopher Musa ya fadi sunan masu daukar nauyin Tshàgyèràn Dhàjì

Da Duminsa: Ministan Tsaro, Christopher Musa ya fadi sunan masu daukar nauyin Tshàgyèràn Dhàjì

Duk Labarai
Ministan Tsaro, Christopher Musa ya bayyana cewa yana zargin 'yan siyasa na bangaren adawane ke daukar nauyin matsalar tsaro a kasarnan. Ya bayyana cewa suna yin hakanne kawai dan su nuna cewa Gwamnati ta gaza. Ya bayyana hakane a hirar da aka yi dashi a gidan talabijin na Arise TV. Yace idan aka lura duk idan zabe ya karato sai kaga matsalar tsaro tana ta'azzara. Yace ba sai mutum yabi ta wannan hanyar ba sannan zai samu mulki.
Da Duminsa: Shugaba Tinubu yayi magana akan Shigar da Dino Melaye yayi zuwa wajan babban taron jam’iyyar ADC

Da Duminsa: Shugaba Tinubu yayi magana akan Shigar da Dino Melaye yayi zuwa wajan babban taron jam’iyyar ADC

Duk Labarai
Fadar shugaban kasa ta yi magana akan shigar da Dino Melaye yayi ya je wajan babban taron jam'iyyar ADC. Shugar ta Dino Melaye ta dauki hankula sosai a kafafen sada zumunta inda ake ta muhawara akai. Me magana da yawun shugaban kasa, Bayo Onanuga ya bayyana cewa, Dino Melaye shine daya daga cikin mashirmatan shuwagabannin jam'iyyar ADC. Yace Allah ya mana tsari daku. https://twitter.com/i/status/2044525281021419721
Da Duminsa: Gwamnatin tarayya ta bayyana jihohi 33 da kananan hukumomi 226 dake fuskantar yiyuwar Ambaliyar ruwa a Najeriya

Da Duminsa: Gwamnatin tarayya ta bayyana jihohi 33 da kananan hukumomi 226 dake fuskantar yiyuwar Ambaliyar ruwa a Najeriya

Duk Labarai
Gwamnatin tarayya ta bayyana jihohi 33 da kananan hukumomi 226 da ke fuskantar barazanar Ambaliyar ruwa a damunar bana. Ministan ruwa da tsafta, Joseph Utsev ne ya bayyana hakan a yayin ganawa da manema labarai a Abuja. Ya bayyana cewa, Jihohin da Ambaliyar ruwan zata faru sun hada da Abia, Adamawa, Anambra, Bauchi, Bayelsa, Benue, Borno, Cross River, Delta, Ebonyi, Edo, Enugu, Gombe, Imo, Jigawa, Kaduna, Kano, Kebbi, Kogi, Kwara, Lagos, Nasarawa, Niger, Ogun, Ondo, Osun, Oyo, Plateau, Rivers, Sokoto, Taraba, Yobe, Zamfara, da babban birnin tarayya, Abuja. Ya bayyana cewa wasu garuruwan akwai hatsari me yawa wasu kuma kadan na faruwar ambaliyar ruwan.
Da Duminsa: Kasar Amurka tace shugaba Tinubu ya gaggauta cire karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle daga mukaminsa saboda bata yadda dashi ba

Da Duminsa: Kasar Amurka tace shugaba Tinubu ya gaggauta cire karamin Ministan tsaro, Bello Matawalle daga mukaminsa saboda bata yadda dashi ba

Duk Labarai
Kasar Amurka ta bayyana cewa bata yadda da karamin ministan tsaro na Najeriya ba, Bello Matawalle. 'Yar majalisar jihar Florida, Kimberly Daniels ce ta bayyana hakan inda tace suna kira ga shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ko dai ya cire Bello Matawalle ko kuma ya canja masa ma'aikata. Hakan na zuwane yayin da matsalar tsaro ke ci gaba da ta'azzara a musamman Arewacin Najeriya. A baya dai akwai zarge-zargen da ake tawa karamin Ministan tsaron wanda ya sha musantawa
Nafiu Bala Gombe ya samu matsala da masu daukar nauyinsa

Nafiu Bala Gombe ya samu matsala da masu daukar nauyinsa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa, Nafiu Bala Gombe da ya fito yace shine shugaban jam'iyyar ADC na riko ya kawo tarnaki a jam'iyyar ya samu matsala da masu daukar nauyinsa. Rahoton yace dama rabin kudin aiki aka bashi idan ya kammala za'a bashi sauran amma yanzu ya nemi a bashi sauran amma sun kiya Saboda sun ce ya kasa hana a yi babban taron jam'iyyar na ADC. Hakanan dakin Otal Din da suke biya masa a Transcorp Hilton sun daina biya Rahoton yace sun babe sosai.
Kalli Bidiyon: An tambayi Atiku Abubakar shin zai iya janyewa Peter Obi idan ya ga cewa ya fishi jama’a?

Kalli Bidiyon: An tambayi Atiku Abubakar shin zai iya janyewa Peter Obi idan ya ga cewa ya fishi jama’a?

Duk Labarai
A wata hira da aka yi da tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar, an tambayeshi shin zai iya janyewa Peter Obi takara idan ya lura Peter Obin yafi shi jama'a? Atiku yace zai iya mana. Yace ita takarar siyasa ana samuntane ta hanyar zaben fidda gwani ko kuma ta hanyar samar da dan takara na bai daya. Yace a kowane mataki idan Peter Obi ya zamana shine yayi nasara zai goyi bayansa. https://twitter.com/i/status/2044467777180672111