A ranar Litinin an sayo dalar Amurka akan Naira 1,725.
Hakan na nuna cewa Nairar ta samu daraja idan aka kwatanta da farashin da aka sayi dalar a ranar Juma'a data gabata watau Naira 1,735.
Wannan farashi na kasuwar bayan fage ce.
Amma a farashin Gwamnati, Naira faduwa ta yi inda aka sayi dala akan Naira 1,676.
Babbar kotun tarayya dake Abuja ta soke karar da aka shigar akan mutane 119 kan zargin cib amanar kasa da shiga zanga-zanga.
Mai Shari'a Obiora Egwuatu ne ya soke tuhumar bayan da lauyan gwamnati MD Abubakar ya bukaci hakan.
A zaman kotun na yau Talata lauyan gwamnatin ya ce babban lauya na kasa ne zai ci gaba da kula da lamarin.
Kungiyar masu dillancin man fetur a karkashin PETROAN ta bayyana cewa, tana nan kan bakanta na man fetur din da zata shigo dashi daga kasar waje ya fi na matatar Dangote sauki.
Me magana da yawun kungiyar, Dr. Joseph Obele ya bayyana cewa dolene a bar kowa yayi kasuwancinsa ba tare da katsalandan ba tunda dai gwamnati tace ta cire hannunta daga harkar.
Kungiyar tace ta kammala shirin ta tsaf dan shigo da man fetur cikin kasarnan kamin watan Disamba.
Kungiyar ta kuma musanta ikirarin da Dangote yayi cewa, suna shirin shigo da man fetur gurbataccene tace wana kawai soki burutsu ne irin na Dangote wanda ya saba yi dan kawai a barshi shi kadai ya rika siyar da man fetur din.
Rahotanni daga jihar Sokoto na cewa wata sabuwar kungiyar 'yan ta'adda ta bulla a jihar.
Mataimakin gwamnan jihar, Idris Gobir ne ya bayyana haka a yayin ziyarar da wata tawagar rundunar tsaro ta kasa ta kai masa ziyara.
Yace sunan wannan sabuwar kungiyar 'yan ta'adda, LAKURAWAS kuma kungiyace dake danganta kanta da addini.
Sannan ya kara da cewa sun fara gudanar da ayyukan ta'addanci a wasu garuruwan na jihar Sokoto.
Sannan kuma yace kungiyar ta mallaki muggan makamai.
Hakan na zuwane yayin da jihar ta Sokoto ke fama da matsalar hare-haren 'yan Bindiga wanda mataimakin gwamnan yace jami'an tsaro na aiki tukuru dan magancewa.
Shugaban 'yansandan Najeriya, IGP Kayode Egbetokun ya bayar da umarnin fara bincike kan yanda aka tsare kananan yara masu zanga-zanga wanda aka gurfanar a kotu.
A baya dai, an gurfanar da kananan yaran a kotu su 32 inda suka rika faduwa saboda tsananin yunwa, saidai shugaban 'yansandan ya bayyana cewa faduwar karyace kawai dan neman magane.
Amma a sabuwar sanarwar da kakakin 'yansandan, Muyiwa Adejobi ya fitar yace shugaban 'yansandan yace a yi bincike dan gano ko an aikata ba daidai ba yayin tsaron yaran.
Sannan ya sha Alwashin daukar mataki da kuma hukunta duk wanda aka samu da laifi yayin kamawa ko kula da yaran.
Hotunan Aurena Dake Ta Yawo A Kafafun Sadarwa An Yi Su Ne Bayan Daurin Aure, Kuma Bada Yawuna Aka Fitar Da Su Ba, Kuma Don Alah Ina Rokon Wadanda Suka Dora Da Su Goge, Cewar Abdulrahim Mansur Yelwa.
https://twitter.com/el_uthmaan/status/1853386068621512806?s=19
Abdulrahim Mansur Isa Yelwa ya magantu akan Hoton sa da Amaryasa dake yawo a Social Media tare da rokon duk wanda yayi posting ya goge.
A ranar Litinin an samu masu zanga-zanga da yaqa sun je Hedikwatar kamfanin mai na kasa,NNPCL inda suke nema shugaban kamfanin yayi murabus.
Masu zanga-zangar wanda wasu kungiyoyin dake ikirarin kare hakkokin al'umma suka jagoranta sun zargi Shugaban na NNPCL, Abba kyari da rashin iya aiki saboda yanda man fetur ke ta kara tsada.
Daya daga cikin shuwagabannin kungiyar, Abdullahi Bilal ya bayyana cewa shugabancin kamfanin na NNPCL ya gaza.
Masu zanga-zangar sun kuma nemi a dakatar da shigo da man fetur daga kasar waje inda suka ce yana lalatawa mutane motoci a Najeriya.
Kungiyar Likitocin Najeriya, NMA ta dakatar da aiki a Asibitin Murtala Muhammad dake Kano inda tace likitocin ta su daina aiki a asibitin.
Kungiyar Likitocin ta dauki wannan mataki ne bayan cin zarafin da ta zargi kwamishiniyar jin kai ta jihar, Amina Abdullahi Ganduje da yiwa wata likita.
Kungiyar tace tana neman gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf ya kori kwamishiniyar daga aiki kamin su koma bakin aiki.
A sanarwar da ta fitar ta bakin shugabanta, Abdurrahman Ali kungiyar tace abin takaici ne lamarin da ya faru ranar 1 ga watan Nuwamba.
Likitar na bakin aiki a bangaren kula da yara inda take kula da yara kusan 100 ita kadai, sai ga kwamishiyar ta shiga wajan inda ta rika cin zarafin likitar akan rashin wani magani da aka rubuta.
Sanarwar kungiyar likitocin tace wannan kuma ba ...
Tsohon me magana da yawun shugaban kasa, Doyin Okupe ya bayyana cewa su yarbawa ba zasu kara yadda a rika zagin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ba.
Yace Tinubu dan lelene a wajansu.
Ya bayyana hakane a hirar da gidan talabijin na Channels TV suka yi dashi.
Saidai yace idan abubuwa a yanzu basa tafiya yanda ya kamata a yi hakuri nan gaba komai zai daidaita.
Labarin Shugaban hukumar binciken kudi ta kasar Equatorial Guinea Baltasar Engonga da ya rika lalata da matan manyan mutane kuma yana daukar Bidiyon lalatar ya dauki sabon salo.
A jiya ne dai hutudole ya kawo muku labarin mutumin inda aka ruwaito cewa ya dauki bidiyo kusan 400 yana lalata da mata daban-daban.
https://twitter.com/GucciStarboi/status/1853527395669606450?t=FX-xtQ8W58w1wTxj4KY06A&s=19
Tuni dai Bidiyon suka watsu sosai a kafafen sada zumunta.
Daya daga cikin matan da yayi lalatar dasu da ta ga Bidiyon kuma surutu yayi yawa akan lamarin, ta kasa jurewa inda ta kashe kanta.
Har yanzu da hukumomi na ci gaba da bincike akan lamarin.