Friday, February 13
Shadow

Author: Bashir Ahmed

An damƙa wa kowane gwamna tallafin shinkafa ban da na Kano – Kwankwaso

An damƙa wa kowane gwamna tallafin shinkafa ban da na Kano – Kwankwaso

Duk Labarai
Jagoran jam'iyyar NNPP, mai mulkin jihar kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana takaicinsa kan yadda ya ce gwamnatin tarayya ta raba kayan tallafin shinkafa ga Jihohi 35 duk ta hannun Gwamnonin su, amma ban da Jihar Kano. Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Jagoran Kwankwasiyyar ya yi zargin cewa gwamnatin tarayyar ta miƙa kason jihar Kano hannun jiga-jigan jam'iyyar APC, wanda a cewarsa hakan ya saɓa wa dimikraɗiyya. ''Wannan babban cin fuska ne ga dimokradiyya da kuma tsarin mulkin ƙasar mu. Wannan mataki dai nuna ɓangaranci ne da ya wuce gona da iri,'' in ji jagoran jam'iyyar NNPP. Ya kuma yi kira ga shugaban ƙasar ya gagguata dakatar da abin da ya kira karan-tsaye wa tsarin dimikraɗiyyar ƙasar. Tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar na jam'iyyar NNPP ya kuma nun...

Gyaran nono lokacin yaye

Nono
A yayin da jaririnki ya daina shan nono kika yayeshi. Nononki zai iya daukar kusan kwanaki 5 zuwa 10 yana dan kumburi nan da can, hakan ba matsala bane,duk da ba kowace mace ce ke fuskantar wannan matsala ba. Idan hakan ya faru dake, zaki iya rika yiwa nonon naki tausa sannan zaki iya rika matso ruwan nonon kadan-kadan. Hakanan ga wanda nonuwan ke zafi bayan kammala shayarwa, ana iya rika dira ruwan sanyi ko a nade kankara a tsumma me kyau a rika dorawa akan nonon. Yana da kyau kuma a rika shan ruwa ko abinda ya danganci riwa. Ana iya shan magungunan rage radadin ciwo irin su Ibuprofen. Sannan maganar gyaran nono ya koma kamar yanda yake kamin ki dauki ciki kuwa, daya daga cikin hanyoyin da ake samun nasarar hakan shine ta hanyar motsa jiki. An fi son motsa jikin da zai ...

Maganin mura mai toshe hanci

Maganin Mura
Akwai magungunan mura na gargajiya dana bature da suke aiki sosai ga masu fana da mura. A wannan bayani zamu fadi magungunan da ake amfani dasu suka inganta daga wajan masana kiwon lafiya. Idan ana fama da mura, musamman wadda ta toshe hanci, ana son mutum ya yawaita shan abu me ruwa-ruwa. Ana kuma son mutum idan da hali ya sha farfesun kaza wanda ke da dan yaji, hakan na taimakawa sosai. Idan kuma makogoro na kaikai, a dumama ruwa da gishiri a barshi ya huce amma da dan dumi a rika wasa sashi a makogoron. Hakanan likitoci sun tabbatar da cewa tsotsar kankara ta ruwan sanyi, musamman wadda babu sugar/sikari a ciki tana maganin kaikayin makogoro sosai, ko da kuwa kaikayin makogoron ya kai matakin da da kyar ake shan ruwa. Hakanan Lemon Grass wadda tana fitowa a wasu gurare...
Ji abinda Bello Turji yawa mutanen Moriki a jihar Zamfara da ya tayar da hankula

Ji abinda Bello Turji yawa mutanen Moriki a jihar Zamfara da ya tayar da hankula

Duk Labarai
Shugaban 'yan ta'adda masu garkuwa da mutane, Bello Turji ya nemi mutanen garin Moriki dake jihar Zamfara su biyashi Naira Miliyan 50 a matsayin diyya. Saidai an yi tattaunawa mutanen sun yadda zasu biyashi Naira Miliyan 30. Wadannan kudade suna a matsayin diyyar shanun Bello Turji ne da sabon shugaban sojoji na harin Morikin yayi inda Bellon yace idan ba'a biyashi ba zai kai hari garin. Shahararren dan jarida, Bulama Bukarti ne ya bayyana hakan inda yace shugaban sojojin ya nemi mutane kada su biya kudin amma basu saurareshi ba dan sun san Bello Turji zai iya kai musu hari. Kowane gida suna biyan Naira 10,000 sai kuma wanda bashi da aure yana biyan Naira dubu 2.
Ana rade-radin akwai yiyuwar wasu manyan jami’an gwamnatin Tinubu su yi Murabus

Ana rade-radin akwai yiyuwar wasu manyan jami’an gwamnatin Tinubu su yi Murabus

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa,akwai rade-radin wasu manyan jami'n gwamnatin Shugaban kasa,Bola Ahmad Tinubu zasu yi murabua. Daga cikin wadanda ake rade-radin akansu akwai shugaban ma'aikatan fadar shugaban kasar, Femi Gbajabiamila. A jiya ne dai kakakin shugaban kasar, Ajuri Ngelale yayi murabus wanda hakan ya jawo cece-kuce sosai akan siyasar fadar shugaban kasar.
Ashe Shugaba Tinubu korar me magana da yawunsa Ajuri Ngelale yayi, ji bayani dalla-dalla

Ashe Shugaba Tinubu korar me magana da yawunsa Ajuri Ngelale yayi, ji bayani dalla-dalla

labaran tinubu ayau
Rahotanni na ta kara fitowa kan dalilin ajiye aikin me magana da yawun shugaban kasa,Ajuri Ngelale. A ranar Asabar ne dai Ajuri ya ajiye aikin nasa inda ya bayyana dalilan rashin lafiyar danginsa a matsayin abinda yasa ya ajiye aikin. Jaridar Daily Nigerian ta ruwaito cewa fada ne ko rashin jituwa tsakanin Ajuri da wasu na kusa da shugaban kasar yasa ya ajiye aikin. Hakanan a wani sabon Rahoto na kafar FIJ, suma sun bayyana cewa, rashin jituwa ne tsakanin Ajuri da dayan kakakin shugaban Bayo Onanuga inda kowa kw ganin shine babba a tsakanin su. Majiyar tace an yi yunkurij sasantasu amma Ajuri yaki yadda a yi musu sulhu wanda haka tasa daga baya aka koreshi daga aiki. Saidai bayan da aka koreshi daga aikin,ya yi rokon a taimaka masa yayi ritaya da kansa dan idan akace an kore...
Nine zan lashe zaben shugaban kasa na 2027 saboda PDP ta mutu murus>>Kwankwaso

Nine zan lashe zaben shugaban kasa na 2027 saboda PDP ta mutu murus>>Kwankwaso

Duk Labarai
Tsohon gwamnan Kano kuma dan takarar shugaban kasa a jami'iyyar NNPP, Dr. Rabiu Musa Kwankwaso ya bayyana cewa,shine zai lashe zaben shekarar 2027 saboda PDP ta mutu. Ya bayyana hakane a Katsina bayan kaddamar da ofishin jam'iyyar a kan hanyar IBB Way. Kwankwaso yayi kira ga mutanen jam'iyyarsa da kada su yadda a yaudaresu da Taliya da kudi yayin zabe inda ya jawo hankalinsu kan su ci gaba da aiki tukuru dan ci gaban jam'iyyar.
Ji Ainahin dalilin da yasa me magana da yawun shugaban kasa, Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa

Ji Ainahin dalilin da yasa me magana da yawun shugaban kasa, Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa

Duk Labarai
Rahotanni sun bayyana cewa me magana da yawun shugaban kasa, Ajuri Ngelale ya ajiye aikinsa na wucin gadi inda yace zai taci hutun sai abinda hali yayi. Ya bayyana dalilin cewa, wani daga cikin iyalansa ne ba lafiya shiyasa ya dauki wannan mataki duk da yake bai masa dadi ba. Saidai a binciken da jaridar Daily Nigerian ta gudanar, ta gano cewa ba haka abin yake ba. Jaridar tace wasu na kusa da shugaban kasa ne suka fara sakawa Ajuri ido kan cewa mukaman da yake rike dasu sun masa yawa kuma sun ci karo da aikinsa na matsayin me magana da yawun shugaban kasa. Dan hakane suka bukaci ya zabi daya daga cikin mukaman da yake rike dasu ya ajiye sauran, jaridar tace na hannun damar shugaban kasar, sun dauka cewa zai ajiye aikin magana da yawun shugaban kasa ne amma sai ya zabi ya ci ga...